ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Tabbacin Za Mu Iya Gudanar Da Sahihin Zaɓe A 2027 —Shugaban INEC

by Leadership Hausa
4 months ago
INEC

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), Farfesa Joash Ojo Amupitan, ya ce babu tabbacin ko hukumar zaɓe za ta iya gudanar da sahihin zaɓe mai cike da nasara 100 bisa 100 a 2027 ko da ta saka sakamakon zaɓen a na’ura.

Amupitan ya bayyana hakan ne a yayin wani taro da ƙungiyar farar hula ta mai neman a inganta harkokin zaɓe ta shirya, wanda aka gudanar a Otel ɗin Abuja Continental, a ranar Lahadi da ta gabata.

A cewarsa, zaɓen shugaban ƙasa na 2027 zai kasance mafi kyau a tarihin Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ƙungiyoyin farar hula da masana harkokin zaɓe da masu sa ido a cikin harkokin zaɓe da kuma wakilan al’umma na daga cikin waɗanda suka halarci a taron don tattauna al’amuran da suka shafi zaɓe.

  • Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe
  • Majalisar Ƙoli Kan Shari’ar Musulunci Ta Sake Neman A Cire Shugaban INEC

Sai dai kuma Amupitan ya ce Nijeriya na buƙatar yin amfani da sauƙaƙan dokar harshe, inda zai yi saukin fahimta ga kowane ɗan Nijeriya tare da yaba wa kowane sashe na dokar zaɓe ta 2026.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

Ya ce a yayin zaɓen shugabannin ƙananan hukumomin Abuja, sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi biyar an bayyanasu a kan lokaci, amma sakamakon zaɓe ƙaramar hukumar Kuje bai bayyana kan lokaci ba har sai da ya kai rana ta gaba.

Amupitan ya ƙara da cewa ya kamata a tabbatar da cewa zaɓe mai nasara ya dogara ne kan kammala tsarin kayan aiki.

Amupitan ya ce, “Na farko, idan kana son auna ko zaɓen ya yi nasara, dole ne ka tantance ko an fara zaɓen kamar yadda aka sanar. Kuma mun sanar da zaɓen da ƙarfe 8.30. Don haka idan mun iya fara zaɓen da ƙarfe 8.30 shi ne za mu iya samun nasara.

“Na biyu, idan zaɓen ya kasance cikin lumana. Na uku, idan muka iya sarrafa sakamakon zaɓen yadda ya kamata, sannan a bayyanar da sakamakon, to za ka iya cewa ka yi zaɓe mai nasara.

“A matsayinmu na hukumar da ke sa ido, mun ƙudiri aniyar cimma duk wannan nasarar.

“Amma duk da haka, dole mu yarda cewa akwai wasu matsalolin kayan aiki, wasu kuwa na Ɗan’adam ne, kuma muna ƙoƙarin magancesu. Bari in roƙi ‘yan Nijeriya, saboda na lura yanzu cewa abin da ‘yan Nijeriya suke so shi ne, sahihin zaɓe. Zan yi ƙoƙarina daidai gwargwadon ikona don ba wannan ƙasa zaɓe mafi kyau.

“Watakila ba za mu iya samun zaɓen kashi 100 cikakke a yanzu ba. Amma dangane da isar da sakamakon ta hanyar na’ura, na riga na faɗa a gabanin zaɓen shugabannin ƙananan hukumomin Abuja cewa muna da ikon isar da sakamakon ta na’ura, kuma za mu sanar da sakamakon ta na’ura.

“Abin da kawai ke damunmu shi ne, lokaci na haƙiƙa. Mene ne lokaci na haƙiƙa? Misali, idan ka tafi, ka yi amfani da manhajarka don tura kuɗi daga asusunka. Ko a cikin birnin Abuja, ka tura naira 50,000 zuwa ga Mista B, kuma daga manhajarka, kuɗin ya tafi.

“Amma mutumin bai ga kuɗin ba har sai bayan wasu mintuna 30, wani sa’a, ko ma da yamma. Don haka waɗannan wasu ne daga cikin abubuwan. Kuma lokacin da ka ce lokaci ne na haƙiƙa, da zarar an gama, dole ne a karɓa.

“Saboda haka, gudanar da sakamakon zaɓe da kayan aiki su ne manyan batutuwa guda biyu da, daga ɓangarenmu, muna ƙoƙarin ganin yadda za mu iya gudanar da su sosai, domin inganta gaskiya da amincin tsarin.

“An kawar da matsalar na’ura. Na’ura ba zai sake kawo matsala ba a zaɓen Nijeriya, kuma duk lokacin da na kalli sashe na 63 na dokar zaɓe, ko a zaɓen ƙananan hukumomin abuja, ban da wannan jinkiri, ba mu samu wata matsala ta na’ura ba, ma’ana cewa kwai an samar da ita ne don kariya. Kuma a lokacin mulkina, ba za ta gaza ba.

“Ko da ta gaza, dole ne a sanar da sakamakon zaɓe. Amma matsalar kaɗai ita ce, idan ta gaza sanar da sakamakon zaɓe a kan lokaci, kamar yadda muka samu a wancan ƙaramar hukuma.

“Wannan shi ne babban matsala. Yanzu da haka da nake yin magana game da magance matsalar, zaɓe yanzu, ko da yaushe, yana da nasaba da fasaha. Amma kafin ka yi amfani da kowace fasaha, yana da muhimmanci ka gwada wannan fasaha sosai.

“Don haka bincikena na zaɓen 2023 shi ne yayin da aka gwada na’urar a cikin jihohi, alal misali zaɓɓen Osun, zaɓen Ekiti, duk da haka, lokacin da ya zo ga zaɓen tarayya, musamman zaɓen shugaban ƙasa wanda yanzu ya zama na tsakanin jihohi, ba a gwada shi yadda ya kamata ba.

“Don haka, ɗaya daga cikin abubuwan da muke ƙoƙarin yi kafin zaɓen shi ne, tabbatar da cewa an sanar da sakamakon zaɓen ta na’ura a dukkan faɗin jihohin ƙasar nan.

“Da yardar Allah, zaɓen shekarar 2027 zai kasance mafi kyawun zaɓen da ‘yan Nijeriya za su yi. Domin ‘yan Nijeriya a 2023 sun sha bamban da abin da za ku samu a 2027. Mutane sun ƙara samun wayewa sosai.”

INEC
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗege Shari’ar Ganduje Da Wasu Mutum 7 Zuwa 14 Ga Oktoba 2026

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
Next Post
Rashin Tsaro Yayi Sauƙi A Mulkin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu – Daniel Bwala

Rashin Tsaro Yayi Sauƙi A Mulkin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu - Daniel Bwala

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.