Hukumar da ke shirya Jarabawar Shiga Jami’a (JAMB) ta gargaɗi ɗalibai masu zana Jarabawar (UTME) ta 2026 game da bayar da bayanan ƙarya ko taka dokokin hukumar yayin zana jarrabawar.
Shugaban Hukumar JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, ne ya yi wannan gargaɗin, yayin da ake kan rajistar zana jarrabawar UTME ta 2026, wacce aka fara a ranar 26 ga Janairu.
- Ra’ayin Raya Makoma Ta Bai-daya Ga Daukacin Bil’adama Hanya Ce Mafi Dacewa Wajen Neman Samun Ci Gaban Duniya Mai Jituwa Da Dorewa
- Ɗan Ganduje Ya Gwangwaje Manoma, Da ‘Yan Kasuwa Da Manyan Kyautata A Kano
Farfesa Oloyede ya bayyana haka ne a ranar Litinin a yayin tattaunawa da manema labarai, inda ya jaddada muhimmancin kiyaye ƙa’idojin hukumar ga ɗalibai yayin rajistar jarrabawar.
A cewarsa, taka ƙa’idojin hukumar na iya jawo hukunci mai tsauri, gami da dakatar da wanda aka kama ya taka ƙa’idojin hana zana jarrabawar UTME har tsawon shekara uku.
“Za a iya buga sunayen waɗanda suka taka ƙa’idojin jarrabawar a jaridu kuma a miƙa sunayen ga sauran hukumomin jarrabawa,” in ji Farfesa Oloyede















Discussion about this post