ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Wadata ‘Yan Nijeriya Da Wutar Lantarki A Ramadan

by Ibrahim Bala
5 months ago
Nijeriya

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanmu da shigowa wata mai girma, mai alfarma, watan Ramadana, barkanmu da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, filin da ke zaƙulo muku batutuwan da suke ci wa al’umma tuwo a ƙwarya.

A wannan mako zan yi magana ne a kan shugabanninmu, wakilanmu, masu mulkinmu, masu sarauta, masu kuɗinmu. Idan muka yi duba a cikin shekara muna da kwana 360, a wannan kwana ɗari uku da sittin ɗin wata ɗaya ne ko na ce kwana 29 ne na watan Ramadana da musulmai suke gabatar da ibada.

ADVERTISEMENT
  • KEDCO Ta Nuna Damuwa Kan Katsewar Wutar Lantarki A Arewa Maso Yamma
  • Samar Da Wutar Lantarki A Kaduna Wajibi Ne Ba Alfarma Ba – Gwamna

Wata ne da yake da falala da girma a wajen ubangiji, sai dai babban abin baƙin ciki da takaici, duk waɗannan mutanen da muke da su; masu mulki, masu sarauta, masu kuɗi, masu faɗa a ji a Arewacin Nijeriya, a wata ɗaya ba ma iya samu a gabatar da ibadar ubangiji. Ko da haɗuwa za su yi Arewacin Nijeriya musulmai su yi ƙoƙarin yadda za a yi a samar da wuta a watan azumin Ramadana, domin al’ummar musulmi talakawa su ji daɗin ibada, su ma su samu lada, amma ba a iya yi, wannan abun takaici ne.

Ina mai bayar da shawara waɗannan mutane shuwagabannin namu su riƙa haɗa kai, idan watan azumi ya kama za su sami lada, su ma suna so su sami rahamar ubangiji. Ita kuma wutar Nefa kamar wata rahama ce a duniya da talaka yake iya mora. Saboda sana’o’insa da komai nasa zai haɓaka a wannan wata na Ramadana, wannan ba abun lura bane ba?

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ku lura fa duk lokacin da za ku ga ana samun wuta sosai akai-akai to, Kirsimeti ce ta zo watan Disamba. To, me ya sa mu ma ba za mu yi haka ba, ku fa wakilanmu ne wakilan ƙasar mu ne. Saboda haka, wannan abun takaici ne. Kuma ina kira ga malamai su yi kira da masu hannu da shuni, shugabanni lallai su riƙa yin ƙoƙari wata na Ramadan, watan azumi ana iya samun wutar da talaka zai amfana ko da ta wata ɗaya ce.

Allah (SWT) zai yi farin ciki da wannan, amma an kau da kai, bai kamata ba a ce ana da shugabanni wakilai a Arewacin Nijeriya kuma musulmai amma ba za su iya yi wa musulunci hidimar wata ɗaya ba. Ko haɗuwa suka yi suka ce sun samar da wuta dan kawai watan azumin Ramadana, ai sun yi wa musulunci hidima za kuma su sami lada.

Muna fatan za su yi amfani da wannan dama, wannan wata da muka shiga na Ramadana su samar da wuta ga talaka da al’ummar musulmi ta Najeriya baki ɗaya su amfana.

Nijeriya
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

MASU ALAKA

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027
Labarai

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi

Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.