ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Wadata ‘Yan Nijeriya Da Wutar Lantarki A Ramadan

by Ibrahim Bala
4 months ago
Nijeriya

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanmu da shigowa wata mai girma, mai alfarma, watan Ramadana, barkanmu da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, filin da ke zaƙulo muku batutuwan da suke ci wa al’umma tuwo a ƙwarya.

A wannan mako zan yi magana ne a kan shugabanninmu, wakilanmu, masu mulkinmu, masu sarauta, masu kuɗinmu. Idan muka yi duba a cikin shekara muna da kwana 360, a wannan kwana ɗari uku da sittin ɗin wata ɗaya ne ko na ce kwana 29 ne na watan Ramadana da musulmai suke gabatar da ibada.

ADVERTISEMENT
  • KEDCO Ta Nuna Damuwa Kan Katsewar Wutar Lantarki A Arewa Maso Yamma
  • Samar Da Wutar Lantarki A Kaduna Wajibi Ne Ba Alfarma Ba – Gwamna

Wata ne da yake da falala da girma a wajen ubangiji, sai dai babban abin baƙin ciki da takaici, duk waɗannan mutanen da muke da su; masu mulki, masu sarauta, masu kuɗi, masu faɗa a ji a Arewacin Nijeriya, a wata ɗaya ba ma iya samu a gabatar da ibadar ubangiji. Ko da haɗuwa za su yi Arewacin Nijeriya musulmai su yi ƙoƙarin yadda za a yi a samar da wuta a watan azumin Ramadana, domin al’ummar musulmi talakawa su ji daɗin ibada, su ma su samu lada, amma ba a iya yi, wannan abun takaici ne.

Ina mai bayar da shawara waɗannan mutane shuwagabannin namu su riƙa haɗa kai, idan watan azumi ya kama za su sami lada, su ma suna so su sami rahamar ubangiji. Ita kuma wutar Nefa kamar wata rahama ce a duniya da talaka yake iya mora. Saboda sana’o’insa da komai nasa zai haɓaka a wannan wata na Ramadana, wannan ba abun lura bane ba?

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ku lura fa duk lokacin da za ku ga ana samun wuta sosai akai-akai to, Kirsimeti ce ta zo watan Disamba. To, me ya sa mu ma ba za mu yi haka ba, ku fa wakilanmu ne wakilan ƙasar mu ne. Saboda haka, wannan abun takaici ne. Kuma ina kira ga malamai su yi kira da masu hannu da shuni, shugabanni lallai su riƙa yin ƙoƙari wata na Ramadan, watan azumi ana iya samun wutar da talaka zai amfana ko da ta wata ɗaya ce.

Allah (SWT) zai yi farin ciki da wannan, amma an kau da kai, bai kamata ba a ce ana da shugabanni wakilai a Arewacin Nijeriya kuma musulmai amma ba za su iya yi wa musulunci hidimar wata ɗaya ba. Ko haɗuwa suka yi suka ce sun samar da wuta dan kawai watan azumin Ramadana, ai sun yi wa musulunci hidima za kuma su sami lada.

Muna fatan za su yi amfani da wannan dama, wannan wata da muka shiga na Ramadana su samar da wuta ga talaka da al’ummar musulmi ta Najeriya baki ɗaya su amfana.

Nijeriya
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi

Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.