ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Wadata ‘Yan Nijeriya Da Wutar Lantarki A Ramadan

by Ibrahim Bala
6 months ago
Nijeriya

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanmu da shigowa wata mai girma, mai alfarma, watan Ramadana, barkanmu da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, filin da ke zaƙulo muku batutuwan da suke ci wa al’umma tuwo a ƙwarya.

A wannan mako zan yi magana ne a kan shugabanninmu, wakilanmu, masu mulkinmu, masu sarauta, masu kuɗinmu. Idan muka yi duba a cikin shekara muna da kwana 360, a wannan kwana ɗari uku da sittin ɗin wata ɗaya ne ko na ce kwana 29 ne na watan Ramadana da musulmai suke gabatar da ibada.

ADVERTISEMENT
  • KEDCO Ta Nuna Damuwa Kan Katsewar Wutar Lantarki A Arewa Maso Yamma
  • Samar Da Wutar Lantarki A Kaduna Wajibi Ne Ba Alfarma Ba – Gwamna

Wata ne da yake da falala da girma a wajen ubangiji, sai dai babban abin baƙin ciki da takaici, duk waɗannan mutanen da muke da su; masu mulki, masu sarauta, masu kuɗi, masu faɗa a ji a Arewacin Nijeriya, a wata ɗaya ba ma iya samu a gabatar da ibadar ubangiji. Ko da haɗuwa za su yi Arewacin Nijeriya musulmai su yi ƙoƙarin yadda za a yi a samar da wuta a watan azumin Ramadana, domin al’ummar musulmi talakawa su ji daɗin ibada, su ma su samu lada, amma ba a iya yi, wannan abun takaici ne.

Ina mai bayar da shawara waɗannan mutane shuwagabannin namu su riƙa haɗa kai, idan watan azumi ya kama za su sami lada, su ma suna so su sami rahamar ubangiji. Ita kuma wutar Nefa kamar wata rahama ce a duniya da talaka yake iya mora. Saboda sana’o’insa da komai nasa zai haɓaka a wannan wata na Ramadana, wannan ba abun lura bane ba?

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku lura fa duk lokacin da za ku ga ana samun wuta sosai akai-akai to, Kirsimeti ce ta zo watan Disamba. To, me ya sa mu ma ba za mu yi haka ba, ku fa wakilanmu ne wakilan ƙasar mu ne. Saboda haka, wannan abun takaici ne. Kuma ina kira ga malamai su yi kira da masu hannu da shuni, shugabanni lallai su riƙa yin ƙoƙari wata na Ramadan, watan azumi ana iya samun wutar da talaka zai amfana ko da ta wata ɗaya ce.

Allah (SWT) zai yi farin ciki da wannan, amma an kau da kai, bai kamata ba a ce ana da shugabanni wakilai a Arewacin Nijeriya kuma musulmai amma ba za su iya yi wa musulunci hidimar wata ɗaya ba. Ko haɗuwa suka yi suka ce sun samar da wuta dan kawai watan azumin Ramadana, ai sun yi wa musulunci hidima za kuma su sami lada.

Muna fatan za su yi amfani da wannan dama, wannan wata da muka shiga na Ramadana su samar da wuta ga talaka da al’ummar musulmi ta Najeriya baki ɗaya su amfana.

Nijeriya
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    A Duba Halin Da Masu Buƙata Ta Musamman Ke Ciki
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi

Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.