ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Wadata ‘Yan Nijeriya Da Wutar Lantarki A Ramadan

by Ibrahim Bala
3 months ago
Nijeriya

Assalamu Alaikum Wa Rahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Jama’a barkanmu da shigowa wata mai girma, mai alfarma, watan Ramadana, barkanmu da kasancewa tare da wannan fili mai albarka, filin da ke zaƙulo muku batutuwan da suke ci wa al’umma tuwo a ƙwarya.

A wannan mako zan yi magana ne a kan shugabanninmu, wakilanmu, masu mulkinmu, masu sarauta, masu kuɗinmu. Idan muka yi duba a cikin shekara muna da kwana 360, a wannan kwana ɗari uku da sittin ɗin wata ɗaya ne ko na ce kwana 29 ne na watan Ramadana da musulmai suke gabatar da ibada.

ADVERTISEMENT
  • KEDCO Ta Nuna Damuwa Kan Katsewar Wutar Lantarki A Arewa Maso Yamma
  • Samar Da Wutar Lantarki A Kaduna Wajibi Ne Ba Alfarma Ba – Gwamna

Wata ne da yake da falala da girma a wajen ubangiji, sai dai babban abin baƙin ciki da takaici, duk waɗannan mutanen da muke da su; masu mulki, masu sarauta, masu kuɗi, masu faɗa a ji a Arewacin Nijeriya, a wata ɗaya ba ma iya samu a gabatar da ibadar ubangiji. Ko da haɗuwa za su yi Arewacin Nijeriya musulmai su yi ƙoƙarin yadda za a yi a samar da wuta a watan azumin Ramadana, domin al’ummar musulmi talakawa su ji daɗin ibada, su ma su samu lada, amma ba a iya yi, wannan abun takaici ne.

Ina mai bayar da shawara waɗannan mutane shuwagabannin namu su riƙa haɗa kai, idan watan azumi ya kama za su sami lada, su ma suna so su sami rahamar ubangiji. Ita kuma wutar Nefa kamar wata rahama ce a duniya da talaka yake iya mora. Saboda sana’o’insa da komai nasa zai haɓaka a wannan wata na Ramadana, wannan ba abun lura bane ba?

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Ku lura fa duk lokacin da za ku ga ana samun wuta sosai akai-akai to, Kirsimeti ce ta zo watan Disamba. To, me ya sa mu ma ba za mu yi haka ba, ku fa wakilanmu ne wakilan ƙasar mu ne. Saboda haka, wannan abun takaici ne. Kuma ina kira ga malamai su yi kira da masu hannu da shuni, shugabanni lallai su riƙa yin ƙoƙari wata na Ramadan, watan azumi ana iya samun wutar da talaka zai amfana ko da ta wata ɗaya ce.

Allah (SWT) zai yi farin ciki da wannan, amma an kau da kai, bai kamata ba a ce ana da shugabanni wakilai a Arewacin Nijeriya kuma musulmai amma ba za su iya yi wa musulunci hidimar wata ɗaya ba. Ko haɗuwa suka yi suka ce sun samar da wuta dan kawai watan azumin Ramadana, ai sun yi wa musulunci hidima za kuma su sami lada.

Muna fatan za su yi amfani da wannan dama, wannan wata da muka shiga na Ramadana su samar da wuta ga talaka da al’ummar musulmi ta Najeriya baki ɗaya su amfana.

Nijeriya
Ibrahim Bala
+ postsBio
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Matsalar Ƙwacen Waya: Ina Mafita?
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Falalar Goman Farko Na Zul-hajji 
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Bukatar Kulawa Da Marayu Da Masu Karamin Karfi
  • Ibrahim Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/ibrahim-bala/
    Talauci Ba Hujjar Aikata Muggan Laifukka Ba Ne 

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi

Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.