Gwamna Uba Sani ya ce, babban abin da ya fi mayar da hankali a kai a kokarinsa na samar da wutar lantarki shi ne, bunkasa ayyukan tattalin arziki da kuma karfafa kanana da matsakaitan kamfanoni.
Ya bayyana hakan ne, a lokacin kaddamar da mataki na daya na rarraba na’urori masu canza wutar lantarki guda 600 da kayan hadi a fadin kananan hukumomi 23, da kuma tura sanya fitilun titi guda 10,000 masu amfani da hasken rana.
- Hukumar RUWASSA Ta Kudiri Aniyar Samar Da Ruwa A Fadin Jihar Katsina
- Neymar Na Duba Yiwuwar Ritaya Daga Ƙwallon Ƙafa A Ƙarshen Shekara
Da yake jawabi a wurin bikin, Gwamnan ya ce; ”muna bai wa masu walda da masu dinki da masu sana’ar kayan sanyi da cibiyoyin sadarwa na zamani da sauran masana’antu damar yin aiki cikin mutunci da annashawa.
“Muna aika sako bayyananne cewa, samun water lantarki ba gata ba ne ga wasu cibiyoyi na birane, illa abu ne da ya zama hakkin kowace al’umma,” in ji shi, ya kara da cewa; wutar lantarki ba abin jin dadi ba ne, illa kusan a ce jinin al’ummar wannan zamani.”
Gwamnan ya nuna cewa, wutar lantarki tana taimaka wa asibitoci da kuma kiyaye alluran rigakafi, tana kuma haskaka azuzuwa da kuma fadada yanayin walwalar yara, haka kuma tana “jagorantar masana’antunmu, tana taimakawa wajen ban ruwa ga gonakinmu, sannan kuma tana tallafa wa kananan kasuwanci, wadanda suka zama ginshikin tattalin arzikinmu.”
A cewar Gwamnan, idan ba samu ingantacciyar wutar lantarki ba, ci gaba yana matukar raguwa, haka nan tsaro da sauran makamantantansu.
Gwamna Uba Sani ya bayyana cewa, gwamnatinsa ta kammala wasu ayyukan wutar lantarki da aka yi watsi da su, sannan kuma ta fara sabbin ayyuka, tun lokacin da ya hau mulki kusan shekara uku da suka gabata.















Discussion about this post