KEDCO ta bayyana fargaba kan matsalolin samar da wutar lantarki daga kamfanin samar da wutar lantarki na ƙasa da kuma turken samar da wutar, inda ta ce yankin Kano na dogaro ne da hanyoyin wutar lantarki guda biyu kacal ta Kaduna da Jos. A cewarta, ƙarancin hanyoyin kai wutar zuwa Kano, Katsina da Jigawa yasa ake fuskantar matsalar rashin kwanciyar hankali a wutar lantarki, musamman idan aka samu tangarda a ɗaya daga cikin layukan.
Kamfanin ya jaddada buƙatar ƙara tsaro, da gyara wa gami da faɗaɗa ƙarfin layin Shiroro–Mando–Kano domin rage yawaitar katsewa. Ya kuma ce ana buƙatar ƙarin jari wajen inganta manyan kayan aiki da ƙara hanyoyin madadin aikewa wa domin tabbatar da daidaiton samar da wuta.
- Ma’aikatan KEDCO Sun Dakatar Da Yajin Aiki
- Gwamnatin Kano Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Hana Kwankwaso Shigowa Kano — Buba Galadima
KEDCO ta ƙara da cewa ayyukan gyare-gyare da shigar da sabuwar na’urar Optical Ground Wire (OPGW) a kan layukan watsawa sun haddasa yawan katsewar wuta a ƙarshen mako, lamarin da ya shafi masana’antu da walwalar al’umma a yankin.
Kamfanin ya roƙi Gwamnatin Tarayya ta hannun Ma’aikatar Wutar Lantarki da ta umurci TCN da ta gaggauta inganta ayyukan aikewa wa da kammala gyare-gyare. Haka kuma, ya ce yana tattaunawa da hukumar kula da masana’antar samar da wutar lantarki ta ƙasa (Nigerian Electricity Regulatory Commission) da masu zaman kansu (Nigerian Independent System Operator), tare da hanzarta shirye-shiryen faɗaɗa samar da wutar cikin gida, yayin da ya yaba da zuba jari da gwamnatocin Kano, Katsina da Jigawa ke yi a fannin samar da wuta.















Discussion about this post