ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gudanar Da Taro Kan Yadda Za A Tunkari Kakar Noman Bana

by Abubakar Abba
5 months ago
Noma

Hukumar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa (NADF), ta fara gudanar da nazari a kan kashi na farko, na yadda shirinta zai kasance kan samar da kayan aikin noma na bana.

Ta kuma yi alkawarin magance gibin da ake samu na samar da kayan aikin noma a kasar da kuma kara karfafa fannin aikin noman kasar a kakar noma ta bana da muke tunkara.

  • Yadda Jihohi Bakwai Da Murtala Ya Kirkiro Suka Kasance Bayan Shekara 50
  • Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

An gudanar da wannan nazari ne, a taron masu ruwa da tsaki a fannin na aikin noma, wanda kuma ya samu halartar wasu manoma da masu sarrafa amfanin gona da kuma kwararru.

ADVERTISEMENT

Taron ya mayar da hankali ne, kan duba kan sakamakon da aka samu tun bayan kaddamar aikin na zango na daya.

Kazalika, an gudanar da shi ne, bisa nufin lalubo da mafita kan kalubalen da shirin ya fusknata a baya, musamman na sauyin yanayi, domin fara shirin tunkarar shirin zagaye na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

An dai kaddamar da shirin ne, da nufin samar wa manoma ingantattun kayan aikin noma, domin su kara bunkasa aikin nomansu, musaman kananan manoman da ke cikin fadin kasar nan.

A jawabinsa a  Abuja, a madadin hukumar ta NADF, Babban Sakare a hukumar,  Mohammed Ibrahim Nasir Ingawa, ya bayyana cewa; an samar da shirin ne, domin dakile kalubalen da fannin aikin na kasar ke ci gaba da fuskanta da kuma samar da ingantattun kayan aikin noma ga manoman kasar, musamman a kan lokaci.

“Muna sane da wannan shirin da aka kaddamar tare da sanin kalubalen da ake fuskta, domin wadannan kalubale a zahirance suke, musmman a bangaren wanzar da duk wani abu da ya shafi samar da daukin ga fannin aikin noma,“ in ji Ibrahim.

“Kayan aikin noma da hukumar ta NADF ke samarwa a karkashin wannan shiri, wanda kuma ya kasance wata dabara ce da nufin kara samar da kayan aikin, musamman domin a kara habaka samar da amfanin gona mai tarin yawa ga kananan manoman da ke zaune a karkara,” a cewar Ingawa.

A cewar tasa, manyan nasarorin da aka samu a lokacin da aka kaddamar da shirin, sun hada da samar manyan aikin noma da rage kalubalen sauyin yanayi da ke zama babbar illa ga fannin na aikin noma a fadin kasar.

Ya ci gaba da cewa, aikin da za a gudanar a nan gaba, za a mayar da hankali ne wajen tabbatar da samar da ingantattun kayan aikin noma ga matasa da samar da kayan aikin noman rani, musamman domin a rage asarar da manoman kasar ke tafkawa, musamman bayan sun yi shuka.

Shi ma a nasa jawabin, wani mai sarrafa amfanin gona, Farfesa

Mukhtar Yusuf Abdullahi, ya sanar da cewa; wannan shirin, zai taimaka matuka, wajen rage kalubalen da manoman kasar ke fuskanta a fannin.

Sai dai, ya yi gargadin cewa; ana fuskantar matsaloli kan yadda ake shigo da kayan abinci cikin kasar nan daga kasashen ketare, wanda hakan ke haifar da tarnaki ga fannin aikin noman kasar.

Shi kuwa, wani wanda ya halarci taron Abubakar Said Dansadau ya sanar da cewa; tattaunawar na da matukar muhimmanci, sannan kuma ya kamata a ci gaba da gudanar da irinta a-kai-a-kai, musamman domin cimma burin da aka sanya a gaba.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.