ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gudanar Da Taro Kan Yadda Za A Tunkari Kakar Noman Bana

by Abubakar Abba
5 months ago
Noma

Hukumar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa (NADF), ta fara gudanar da nazari a kan kashi na farko, na yadda shirinta zai kasance kan samar da kayan aikin noma na bana.

Ta kuma yi alkawarin magance gibin da ake samu na samar da kayan aikin noma a kasar da kuma kara karfafa fannin aikin noman kasar a kakar noma ta bana da muke tunkara.

  • Yadda Jihohi Bakwai Da Murtala Ya Kirkiro Suka Kasance Bayan Shekara 50
  • Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

An gudanar da wannan nazari ne, a taron masu ruwa da tsaki a fannin na aikin noma, wanda kuma ya samu halartar wasu manoma da masu sarrafa amfanin gona da kuma kwararru.

ADVERTISEMENT

Taron ya mayar da hankali ne, kan duba kan sakamakon da aka samu tun bayan kaddamar aikin na zango na daya.

Kazalika, an gudanar da shi ne, bisa nufin lalubo da mafita kan kalubalen da shirin ya fusknata a baya, musamman na sauyin yanayi, domin fara shirin tunkarar shirin zagaye na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

An dai kaddamar da shirin ne, da nufin samar wa manoma ingantattun kayan aikin noma, domin su kara bunkasa aikin nomansu, musaman kananan manoman da ke cikin fadin kasar nan.

A jawabinsa a  Abuja, a madadin hukumar ta NADF, Babban Sakare a hukumar,  Mohammed Ibrahim Nasir Ingawa, ya bayyana cewa; an samar da shirin ne, domin dakile kalubalen da fannin aikin na kasar ke ci gaba da fuskanta da kuma samar da ingantattun kayan aikin noma ga manoman kasar, musamman a kan lokaci.

“Muna sane da wannan shirin da aka kaddamar tare da sanin kalubalen da ake fuskta, domin wadannan kalubale a zahirance suke, musmman a bangaren wanzar da duk wani abu da ya shafi samar da daukin ga fannin aikin noma,“ in ji Ibrahim.

“Kayan aikin noma da hukumar ta NADF ke samarwa a karkashin wannan shiri, wanda kuma ya kasance wata dabara ce da nufin kara samar da kayan aikin, musamman domin a kara habaka samar da amfanin gona mai tarin yawa ga kananan manoman da ke zaune a karkara,” a cewar Ingawa.

A cewar tasa, manyan nasarorin da aka samu a lokacin da aka kaddamar da shirin, sun hada da samar manyan aikin noma da rage kalubalen sauyin yanayi da ke zama babbar illa ga fannin na aikin noma a fadin kasar.

Ya ci gaba da cewa, aikin da za a gudanar a nan gaba, za a mayar da hankali ne wajen tabbatar da samar da ingantattun kayan aikin noma ga matasa da samar da kayan aikin noman rani, musamman domin a rage asarar da manoman kasar ke tafkawa, musamman bayan sun yi shuka.

Shi ma a nasa jawabin, wani mai sarrafa amfanin gona, Farfesa

Mukhtar Yusuf Abdullahi, ya sanar da cewa; wannan shirin, zai taimaka matuka, wajen rage kalubalen da manoman kasar ke fuskanta a fannin.

Sai dai, ya yi gargadin cewa; ana fuskantar matsaloli kan yadda ake shigo da kayan abinci cikin kasar nan daga kasashen ketare, wanda hakan ke haifar da tarnaki ga fannin aikin noman kasar.

Shi kuwa, wani wanda ya halarci taron Abubakar Said Dansadau ya sanar da cewa; tattaunawar na da matukar muhimmanci, sannan kuma ya kamata a ci gaba da gudanar da irinta a-kai-a-kai, musamman domin cimma burin da aka sanya a gaba.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.