ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gudanar Da Taro Kan Yadda Za A Tunkari Kakar Noman Bana

by Abubakar Abba
4 months ago
Noma

Hukumar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa (NADF), ta fara gudanar da nazari a kan kashi na farko, na yadda shirinta zai kasance kan samar da kayan aikin noma na bana.

Ta kuma yi alkawarin magance gibin da ake samu na samar da kayan aikin noma a kasar da kuma kara karfafa fannin aikin noman kasar a kakar noma ta bana da muke tunkara.

  • Yadda Jihohi Bakwai Da Murtala Ya Kirkiro Suka Kasance Bayan Shekara 50
  • Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

An gudanar da wannan nazari ne, a taron masu ruwa da tsaki a fannin na aikin noma, wanda kuma ya samu halartar wasu manoma da masu sarrafa amfanin gona da kuma kwararru.

ADVERTISEMENT

Taron ya mayar da hankali ne, kan duba kan sakamakon da aka samu tun bayan kaddamar aikin na zango na daya.

Kazalika, an gudanar da shi ne, bisa nufin lalubo da mafita kan kalubalen da shirin ya fusknata a baya, musamman na sauyin yanayi, domin fara shirin tunkarar shirin zagaye na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

An dai kaddamar da shirin ne, da nufin samar wa manoma ingantattun kayan aikin noma, domin su kara bunkasa aikin nomansu, musaman kananan manoman da ke cikin fadin kasar nan.

A jawabinsa a  Abuja, a madadin hukumar ta NADF, Babban Sakare a hukumar,  Mohammed Ibrahim Nasir Ingawa, ya bayyana cewa; an samar da shirin ne, domin dakile kalubalen da fannin aikin na kasar ke ci gaba da fuskanta da kuma samar da ingantattun kayan aikin noma ga manoman kasar, musamman a kan lokaci.

“Muna sane da wannan shirin da aka kaddamar tare da sanin kalubalen da ake fuskta, domin wadannan kalubale a zahirance suke, musmman a bangaren wanzar da duk wani abu da ya shafi samar da daukin ga fannin aikin noma,“ in ji Ibrahim.

“Kayan aikin noma da hukumar ta NADF ke samarwa a karkashin wannan shiri, wanda kuma ya kasance wata dabara ce da nufin kara samar da kayan aikin, musamman domin a kara habaka samar da amfanin gona mai tarin yawa ga kananan manoman da ke zaune a karkara,” a cewar Ingawa.

A cewar tasa, manyan nasarorin da aka samu a lokacin da aka kaddamar da shirin, sun hada da samar manyan aikin noma da rage kalubalen sauyin yanayi da ke zama babbar illa ga fannin na aikin noma a fadin kasar.

Ya ci gaba da cewa, aikin da za a gudanar a nan gaba, za a mayar da hankali ne wajen tabbatar da samar da ingantattun kayan aikin noma ga matasa da samar da kayan aikin noman rani, musamman domin a rage asarar da manoman kasar ke tafkawa, musamman bayan sun yi shuka.

Shi ma a nasa jawabin, wani mai sarrafa amfanin gona, Farfesa

Mukhtar Yusuf Abdullahi, ya sanar da cewa; wannan shirin, zai taimaka matuka, wajen rage kalubalen da manoman kasar ke fuskanta a fannin.

Sai dai, ya yi gargadin cewa; ana fuskantar matsaloli kan yadda ake shigo da kayan abinci cikin kasar nan daga kasashen ketare, wanda hakan ke haifar da tarnaki ga fannin aikin noman kasar.

Shi kuwa, wani wanda ya halarci taron Abubakar Said Dansadau ya sanar da cewa; tattaunawar na da matukar muhimmanci, sannan kuma ya kamata a ci gaba da gudanar da irinta a-kai-a-kai, musamman domin cimma burin da aka sanya a gaba.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.