ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Masu Ruwa Da Tsaki Sun Gudanar Da Taro Kan Yadda Za A Tunkari Kakar Noman Bana

by Abubakar Abba
7 months ago
Noma

Hukumar Bunkasa Aikin Noma ta Kasa (NADF), ta fara gudanar da nazari a kan kashi na farko, na yadda shirinta zai kasance kan samar da kayan aikin noma na bana.

Ta kuma yi alkawarin magance gibin da ake samu na samar da kayan aikin noma a kasar da kuma kara karfafa fannin aikin noman kasar a kakar noma ta bana da muke tunkara.

  • Yadda Jihohi Bakwai Da Murtala Ya Kirkiro Suka Kasance Bayan Shekara 50
  • Arewa Maso Gabashin Jigawa: Abokan Babandede Sun Dauki Harama

An gudanar da wannan nazari ne, a taron masu ruwa da tsaki a fannin na aikin noma, wanda kuma ya samu halartar wasu manoma da masu sarrafa amfanin gona da kuma kwararru.

ADVERTISEMENT

Taron ya mayar da hankali ne, kan duba kan sakamakon da aka samu tun bayan kaddamar aikin na zango na daya.

Kazalika, an gudanar da shi ne, bisa nufin lalubo da mafita kan kalubalen da shirin ya fusknata a baya, musamman na sauyin yanayi, domin fara shirin tunkarar shirin zagaye na biyu.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

An dai kaddamar da shirin ne, da nufin samar wa manoma ingantattun kayan aikin noma, domin su kara bunkasa aikin nomansu, musaman kananan manoman da ke cikin fadin kasar nan.

A jawabinsa a  Abuja, a madadin hukumar ta NADF, Babban Sakare a hukumar,  Mohammed Ibrahim Nasir Ingawa, ya bayyana cewa; an samar da shirin ne, domin dakile kalubalen da fannin aikin na kasar ke ci gaba da fuskanta da kuma samar da ingantattun kayan aikin noma ga manoman kasar, musamman a kan lokaci.

“Muna sane da wannan shirin da aka kaddamar tare da sanin kalubalen da ake fuskta, domin wadannan kalubale a zahirance suke, musmman a bangaren wanzar da duk wani abu da ya shafi samar da daukin ga fannin aikin noma,“ in ji Ibrahim.

“Kayan aikin noma da hukumar ta NADF ke samarwa a karkashin wannan shiri, wanda kuma ya kasance wata dabara ce da nufin kara samar da kayan aikin, musamman domin a kara habaka samar da amfanin gona mai tarin yawa ga kananan manoman da ke zaune a karkara,” a cewar Ingawa.

A cewar tasa, manyan nasarorin da aka samu a lokacin da aka kaddamar da shirin, sun hada da samar manyan aikin noma da rage kalubalen sauyin yanayi da ke zama babbar illa ga fannin na aikin noma a fadin kasar.

Ya ci gaba da cewa, aikin da za a gudanar a nan gaba, za a mayar da hankali ne wajen tabbatar da samar da ingantattun kayan aikin noma ga matasa da samar da kayan aikin noman rani, musamman domin a rage asarar da manoman kasar ke tafkawa, musamman bayan sun yi shuka.

Shi ma a nasa jawabin, wani mai sarrafa amfanin gona, Farfesa

Mukhtar Yusuf Abdullahi, ya sanar da cewa; wannan shirin, zai taimaka matuka, wajen rage kalubalen da manoman kasar ke fuskanta a fannin.

Sai dai, ya yi gargadin cewa; ana fuskantar matsaloli kan yadda ake shigo da kayan abinci cikin kasar nan daga kasashen ketare, wanda hakan ke haifar da tarnaki ga fannin aikin noman kasar.

Shi kuwa, wani wanda ya halarci taron Abubakar Said Dansadau ya sanar da cewa; tattaunawar na da matukar muhimmanci, sannan kuma ya kamata a ci gaba da gudanar da irinta a-kai-a-kai, musamman domin cimma burin da aka sanya a gaba.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

NDLEA Ta Yi Alkawarin Kwace Kadarorin Da Ke Ba Da Mafaka Ga Dillalan Kayoyi

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.