ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Buƙatun Kwankwaso Suka Tarwatsa Yiwuwar Haɗin Gwuiwa Da APC

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Kwankwaso

Majiyoyi a jam’iyyar APC sun bayyana cewa tattaunawar da aka yi da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ta rushe ne bayan ya gabatar da buƙatu masu yawa da suka haɗa da neman iko a manyan tsare-tsaren jam’iyyar da kuma neman kujerar mataimakin shugaban ƙasa.

Sabbin bayanai sun bayyana a ranar Alhamis cewa ƙoƙarin fadar shugaban ƙasa da APC na ƙulla yarjejeniya da tsohon gwamnan Kano wanda a baya ake kallonsa a matsayin “amaryar siyasa” mai tasiri ya ƙare ba tare da cimma matsaya ba.

  • Gwamna Yusuf Zai Yi Nadamar Barinmu – Kwankwaso
  • Tinubu Da Kwankwaso Za Su Gana Yayin Da Siyasar Kano Ta Ɗauki Sabon Salo

An ce Kwankwaso, jagoran Kwankwasiyya da NNPP, an nemi haɗin gwiwarsa ne saboda tasirin siyasar jar hularsa da rawar da jam’iyyarsa ta taka a zaɓen 2023. Majiyoyi da ke da masaniya kan tattaunawar sun shaida wa jaridar THISDAY cewa ganawar tsakanin Kwankwaso da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta gudana na tsawon awanni, musamman a Abuja, domin samar da tsani zuwa Kano da sassan Arewa maso Yamma.

ADVERTISEMENT

Sai dai manyan majiyoyi a APC sun ce tattaunawar ta samu tsaiko ne kan abin da suka kira buƙatun da suka wuce gona da iri. A cewarsu, Kwankwaso ya nemi a ba shi ikon kusan kashi 20 cikin 100 na tsare-tsaren jam’iyyar a matakin ƙasa, tare da neman kujerar mataimakin shugaban ƙasa da kuma tabbaci har zuwa zagayen siyasar 2031—abin da ya tayar da ƙararrawa yayin da shirye-shiryen zaɓen 2027 ke ɗaukar zafi.

“Ko Shugaba Tinubu bai taɓa neman wani kaso na tsarin APC ba. Buƙatar kashi 20 cikin 100 ta kasance abin da ya karya yarjejeniyar. Haka kuma, kujerar mataimakin shugaban ƙasa dama ba ta kan tebur ba, kuma ba a da hujjar tattauna batun 2031 a wannan lokaci,” in ji wata majiya mai ƙarfi da ta halarci tattaunawar.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A gefe guda, ɓangaren Dr. Boniface Aniebonam a NNPP ya ce ficewar Gwamna Abba Kabir Yusuf daga jam’iyyar ya samo asali ne daga halin danniya da yunƙurin Kwankwaso na iko da komai.

Har ila yau, mai ba Gwamna Yusuf shawara kan siyasa, Alhaji Mustapha Bakwana, ya ce a wani shirin rediyo na cikin gida cewa warware rikicin masarautar Kano muhimmin ginshiƙi ne ga ci gaban siyasar jihar. Ya ƙara da cewa gwamnati na shirin haɗa Masarautar Kano ƙarƙashin shugaba guda domin kawo ƙarshen ta ƙaddamar da ke ci gaba.

Kwankwaso
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Babu Wata Tanka Da Ta Sauka A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas A Ranar Juma’a —NPA

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.