ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Buƙatun Kwankwaso Suka Tarwatsa Yiwuwar Haɗin Gwuiwa Da APC

by Abubakar Sulaiman
4 months ago
Kwankwaso

Majiyoyi a jam’iyyar APC sun bayyana cewa tattaunawar da aka yi da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ta rushe ne bayan ya gabatar da buƙatu masu yawa da suka haɗa da neman iko a manyan tsare-tsaren jam’iyyar da kuma neman kujerar mataimakin shugaban ƙasa.

Sabbin bayanai sun bayyana a ranar Alhamis cewa ƙoƙarin fadar shugaban ƙasa da APC na ƙulla yarjejeniya da tsohon gwamnan Kano wanda a baya ake kallonsa a matsayin “amaryar siyasa” mai tasiri ya ƙare ba tare da cimma matsaya ba.

  • Gwamna Yusuf Zai Yi Nadamar Barinmu – Kwankwaso
  • Tinubu Da Kwankwaso Za Su Gana Yayin Da Siyasar Kano Ta Ɗauki Sabon Salo

An ce Kwankwaso, jagoran Kwankwasiyya da NNPP, an nemi haɗin gwiwarsa ne saboda tasirin siyasar jar hularsa da rawar da jam’iyyarsa ta taka a zaɓen 2023. Majiyoyi da ke da masaniya kan tattaunawar sun shaida wa jaridar THISDAY cewa ganawar tsakanin Kwankwaso da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta gudana na tsawon awanni, musamman a Abuja, domin samar da tsani zuwa Kano da sassan Arewa maso Yamma.

ADVERTISEMENT

Sai dai manyan majiyoyi a APC sun ce tattaunawar ta samu tsaiko ne kan abin da suka kira buƙatun da suka wuce gona da iri. A cewarsu, Kwankwaso ya nemi a ba shi ikon kusan kashi 20 cikin 100 na tsare-tsaren jam’iyyar a matakin ƙasa, tare da neman kujerar mataimakin shugaban ƙasa da kuma tabbaci har zuwa zagayen siyasar 2031—abin da ya tayar da ƙararrawa yayin da shirye-shiryen zaɓen 2027 ke ɗaukar zafi.

“Ko Shugaba Tinubu bai taɓa neman wani kaso na tsarin APC ba. Buƙatar kashi 20 cikin 100 ta kasance abin da ya karya yarjejeniyar. Haka kuma, kujerar mataimakin shugaban ƙasa dama ba ta kan tebur ba, kuma ba a da hujjar tattauna batun 2031 a wannan lokaci,” in ji wata majiya mai ƙarfi da ta halarci tattaunawar.

LABARAI MASU NASABA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

A gefe guda, ɓangaren Dr. Boniface Aniebonam a NNPP ya ce ficewar Gwamna Abba Kabir Yusuf daga jam’iyyar ya samo asali ne daga halin danniya da yunƙurin Kwankwaso na iko da komai.

Har ila yau, mai ba Gwamna Yusuf shawara kan siyasa, Alhaji Mustapha Bakwana, ya ce a wani shirin rediyo na cikin gida cewa warware rikicin masarautar Kano muhimmin ginshiƙi ne ga ci gaban siyasar jihar. Ya ƙara da cewa gwamnati na shirin haɗa Masarautar Kano ƙarƙashin shugaba guda domin kawo ƙarshen ta ƙaddamar da ke ci gaba.

Kwankwaso
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Waɗanda Suka Kai Hari Cocin Owo Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya

June 3, 2026
Next Post
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Babu Wata Tanka Da Ta Sauka A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas A Ranar Juma’a —NPA

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.