ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Buƙatun Kwankwaso Suka Tarwatsa Yiwuwar Haɗin Gwuiwa Da APC

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
Kwankwaso

Majiyoyi a jam’iyyar APC sun bayyana cewa tattaunawar da aka yi da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ta rushe ne bayan ya gabatar da buƙatu masu yawa da suka haɗa da neman iko a manyan tsare-tsaren jam’iyyar da kuma neman kujerar mataimakin shugaban ƙasa.

Sabbin bayanai sun bayyana a ranar Alhamis cewa ƙoƙarin fadar shugaban ƙasa da APC na ƙulla yarjejeniya da tsohon gwamnan Kano wanda a baya ake kallonsa a matsayin “amaryar siyasa” mai tasiri ya ƙare ba tare da cimma matsaya ba.

  • Gwamna Yusuf Zai Yi Nadamar Barinmu – Kwankwaso
  • Tinubu Da Kwankwaso Za Su Gana Yayin Da Siyasar Kano Ta Ɗauki Sabon Salo

An ce Kwankwaso, jagoran Kwankwasiyya da NNPP, an nemi haɗin gwiwarsa ne saboda tasirin siyasar jar hularsa da rawar da jam’iyyarsa ta taka a zaɓen 2023. Majiyoyi da ke da masaniya kan tattaunawar sun shaida wa jaridar THISDAY cewa ganawar tsakanin Kwankwaso da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta gudana na tsawon awanni, musamman a Abuja, domin samar da tsani zuwa Kano da sassan Arewa maso Yamma.

ADVERTISEMENT

Sai dai manyan majiyoyi a APC sun ce tattaunawar ta samu tsaiko ne kan abin da suka kira buƙatun da suka wuce gona da iri. A cewarsu, Kwankwaso ya nemi a ba shi ikon kusan kashi 20 cikin 100 na tsare-tsaren jam’iyyar a matakin ƙasa, tare da neman kujerar mataimakin shugaban ƙasa da kuma tabbaci har zuwa zagayen siyasar 2031—abin da ya tayar da ƙararrawa yayin da shirye-shiryen zaɓen 2027 ke ɗaukar zafi.

“Ko Shugaba Tinubu bai taɓa neman wani kaso na tsarin APC ba. Buƙatar kashi 20 cikin 100 ta kasance abin da ya karya yarjejeniyar. Haka kuma, kujerar mataimakin shugaban ƙasa dama ba ta kan tebur ba, kuma ba a da hujjar tattauna batun 2031 a wannan lokaci,” in ji wata majiya mai ƙarfi da ta halarci tattaunawar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

A gefe guda, ɓangaren Dr. Boniface Aniebonam a NNPP ya ce ficewar Gwamna Abba Kabir Yusuf daga jam’iyyar ya samo asali ne daga halin danniya da yunƙurin Kwankwaso na iko da komai.

Har ila yau, mai ba Gwamna Yusuf shawara kan siyasa, Alhaji Mustapha Bakwana, ya ce a wani shirin rediyo na cikin gida cewa warware rikicin masarautar Kano muhimmin ginshiƙi ne ga ci gaban siyasar jihar. Ya ƙara da cewa gwamnati na shirin haɗa Masarautar Kano ƙarƙashin shugaba guda domin kawo ƙarshen ta ƙaddamar da ke ci gaba.

Kwankwaso
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Babu Wata Tanka Da Ta Sauka A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas A Ranar Juma’a —NPA

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.