Gwamnan jihar Kano, Abba Yusuf, ya yaba da dawowar tsohon gwamna kuma sanata, Ibrahim Shekarau, zuwa jam’iyyar APC, yana mai bayyana hakan a matsayin babban ci gaba ga ƙarfin jam’iyyar a jihar. A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaransa, Mustapha Muhammad, ya fitar a ranar Lahadi, Gwamna Yusuf ya ce dawowar Shekarau za ta ƙara ƙarfafa tubalin siyasar APC da kuma shirin ta na tunkarar zaɓuka masu zuwa.
Ya bayyana cewa ana shirye-shiryen gudanar da liyafar karɓar tsohon gwamnan a hukumance, inda za a sanar da ranar bayan tuntuɓa da shugabannin jam’iyyar na ƙasa. Gwamna Yusuf ya ƙara da cewa APC na ci gaba da samun ƙarin goyon baya a faɗin Kano, tare da jaddada cewa jam’iyyar na da ƙarfin da za ta iya yin tasiri a zaɓuka masu zuwa.
- Na Tsaya Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
- Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
- “Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
- Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka
- Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu
Gwamnan ya nuna ƙwarin gwuiwa kan nasarar APC a zaɓukan gaba, yana danganta hakan da ƙarin haɗin kai da kyakkyawar fahimta tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar. Ya kuma tabbatar da cewa ana ci gaba da ƙoƙarin ƙarfafa haɗin kai a cikin jam’iyyar tare da faɗaɗa tasirinta a matakin ƙasa.
A ɗaya ɓangaren kuma, Shekarau ya riga ya tabbatar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP a wata wasiƙa da ya rubuta a ranar 19 ga Afrilu, 2026, zuwa ga shugaban PDP na mazaɓar Giginyu a ƙaramar hukumar Nassarawa ta jihar Kano, inda ya ce ficewar ta fara aiki nan take.
Ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bayan tuntuɓa mai zurfi da abokan siyasarsa, yana mai gode wa shugabannin jam’iyyar bisa goyon bayan da suka ba shi a lokacin da yake cikinta.














