Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya shigar da ƙarar neman diyya ta Naira biliyan 10 a kan Hukumar ICPC, bisa zargin hana shi ganin matarsa, Aichatou Asabe, da ɗansa, Abba El-Rufai, yayin da yake tsare a hannun hukumar. Lauyansa, Ubong Akpan, ne ya shigar da ƙarar, inda aka kuma haɗa Shugaban ICPC da Babban Lauyan Tarayya (AGF) a matsayin waɗanda ake ƙara.
A ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/1852/2026, wadda aka shigar a ranar 13 ga Agusta, El-Rufai ya roƙi Babbar Kotun Tarayya ta Abuja da ta tabbatar da cewa haƙƙoƙinsa na asali da kundin tsarin mulkin Nijeriya ya tanada ba su tafi a banza ba saboda tsare shi. Ya kuma ce hana shi damar ganin iyalansa, musamman domin su kai masa abinci, da magunguna da sauran buƙatu, ba tare da sahalewar doka ko umarnin kotu ba, ya saɓa wa haƙƙinsa.
Tsohon gwamnan ya kuma zargi jami’an ICPC da amfani da ƙarfi, da tsoratarwa da kuma tsoma baki cikin dangantakarsa da iyalansa yayin da matarsa da ɗansa suka yi ƙoƙarin ganinsa a ranar 7 ga Yuli. Ya ce hakan ya haifar masa da wulakanci, da damuwa da matsananciyar matsalar tunani, tare da neman kotu ta umurci ICPC da ta ba shi damar ganin iyalansa da lauyoyinsa cikin sauƙi a duk lokacin da yake tsare.
A cikin rantsuwar da aka gabatar wa kotu, Babban Sakataren El-Rufai, Mohammed Shaba, ya ce matarsa ta kasance tana kai masa abinci, da tufafi, da magunguna da sauran abubuwan da yake buƙata tun bayan tsare shi. Ya kuma bayyana cewa a ranar 1 ga Afrilu, Babbar Kotun Tarayya da ke Kaduna ta bayar da umarnin bai wa waɗanda ake tsare damar ganin lauyoyinsu da likitocinsu. A cewarsa, wannan umarni ya nuna cewa bai kamata a tsare mutum ba tare da ya samu damar sadarwa da mutanensa ba.
Shaba ya ƙara da cewa kafin ranar 7 ga Yuli, Asabe tana ziyartar mijinta akai-akai tare da kai masa abinci da sauran abubuwa ba tare da cikas ba. Sai dai daga baya aka hana ta yin hakan, lamarin da ya sa El-Rufai ya garzaya kotu domin neman a tabbatar da haƙƙinsa na ganin iyalansa da samun kulawar da yake buƙata yayin da yake tsare.














