ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Abba K. Yusuf Ya Naɗa Mukaddashin Darakta Janar Na Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Kano

by Muhammad Bashir
4 months ago
Gwamna

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle a matsayin Mukaddashin Darakta Janar na Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano, biyo bayan murabus ɗin Darakta Janar na hukumar, Alhaji Laminu Rabiu, wanda ya ajiye muƙaminsa a kwanaki.

Wannan naɗi na daga cikin sabbin naɗe-naɗe da ƙarin mukamai da gwamnan ya amince da su, a shirinsa na ƙarfafa manyan hukumomin gwamnati da tabbatar da ingantaccen tsarin gudanar da ayyuka a jihar.

  • NAHCON Ta Jaddada Ƙudirinta Na Kammala Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 A Kan Lokaci
  • Alhazan Nijeriya Bana Ba Za A Ba Su Guzuri A Hannu Ba, Sai Dai Su Cira Ta Katin ATM – CBN

Sanarwar hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mai magana da yawun gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu a ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar naɗe-naɗen sun hada da:

1. Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle – Mukaddashin Darakta Janar, Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

2. Yusuf Mukhtar – An ɗaga shi zuwa mukamin Babban Sakataren Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano.

3. Barrista Rahama Malam Alhaji – Shugabar, Cibiyar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano.

4. Aina’u Ade – An ɗaga darajarta zuwa Mai taimakawa Gwamna kan Harkokin Kannywood.

Sanarwar ta bayyana cewa Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle ya taɓa riƙe muƙamin Sakataren Zartarwa na Hukumar Alhazai da kuma Babban Sakatare a Ma’aikatar kafin ritayarsa daga aikin gwamnati. An bayyana shi a matsayin gogaggen ma’aikaci da ya shafe shekaru yana kula da harkokin aikin Hajji cikin nasara.

Game da Barrista Rahama Malam Alhaji, sanarwar ta ce ƙwararriyar lauya ce da ta shafe sama da shekaru bakwai tana aiki a fannoni daban-daban na shari’a, ciki har da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) da kuma zama shugabar Tsangayar Ilimin Shari’a a Jami’ar Maryam Abacha (MAAUN).

Haka kuma, ɗaga Aina’u Ade biyo bayan irin bajintar da ta nuna a tsohon muƙaminta.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya buƙaci sabbin waɗanda aka naɗa da su tabbatar da amincewar da aka yi musu ta hanyar aiki tukuru, gaskiya, da biyayya ga manufar “Kano Farko”. Dukkan naɗe-naɗen sun fara aiki nan take.

Gwamna
Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Sojoji Sun Hallaka Babban Kwamandan Boko Haram, Abu Khalid, Da Wasu 10 A Borno

Sojoji Sun Hallaka Babban Kwamandan Boko Haram, Abu Khalid, Da Wasu 10 A Borno

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.