ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Abba K. Yusuf Ya Naɗa Mukaddashin Darakta Janar Na Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Kano

by Muhammad Bashir
5 months ago
Gwamna

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle a matsayin Mukaddashin Darakta Janar na Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano, biyo bayan murabus ɗin Darakta Janar na hukumar, Alhaji Laminu Rabiu, wanda ya ajiye muƙaminsa a kwanaki.

Wannan naɗi na daga cikin sabbin naɗe-naɗe da ƙarin mukamai da gwamnan ya amince da su, a shirinsa na ƙarfafa manyan hukumomin gwamnati da tabbatar da ingantaccen tsarin gudanar da ayyuka a jihar.

  • NAHCON Ta Jaddada Ƙudirinta Na Kammala Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2026 A Kan Lokaci
  • Alhazan Nijeriya Bana Ba Za A Ba Su Guzuri A Hannu Ba, Sai Dai Su Cira Ta Katin ATM – CBN

Sanarwar hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mai magana da yawun gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu a ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar naɗe-naɗen sun hada da:

1. Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle – Mukaddashin Darakta Janar, Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

2. Yusuf Mukhtar – An ɗaga shi zuwa mukamin Babban Sakataren Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano.

3. Barrista Rahama Malam Alhaji – Shugabar, Cibiyar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano.

4. Aina’u Ade – An ɗaga darajarta zuwa Mai taimakawa Gwamna kan Harkokin Kannywood.

Sanarwar ta bayyana cewa Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle ya taɓa riƙe muƙamin Sakataren Zartarwa na Hukumar Alhazai da kuma Babban Sakatare a Ma’aikatar kafin ritayarsa daga aikin gwamnati. An bayyana shi a matsayin gogaggen ma’aikaci da ya shafe shekaru yana kula da harkokin aikin Hajji cikin nasara.

Game da Barrista Rahama Malam Alhaji, sanarwar ta ce ƙwararriyar lauya ce da ta shafe sama da shekaru bakwai tana aiki a fannoni daban-daban na shari’a, ciki har da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) da kuma zama shugabar Tsangayar Ilimin Shari’a a Jami’ar Maryam Abacha (MAAUN).

Haka kuma, ɗaga Aina’u Ade biyo bayan irin bajintar da ta nuna a tsohon muƙaminta.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya buƙaci sabbin waɗanda aka naɗa da su tabbatar da amincewar da aka yi musu ta hanyar aiki tukuru, gaskiya, da biyayya ga manufar “Kano Farko”. Dukkan naɗe-naɗen sun fara aiki nan take.

Gwamna
Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Sojoji Sun Hallaka Babban Kwamandan Boko Haram, Abu Khalid, Da Wasu 10 A Borno

Sojoji Sun Hallaka Babban Kwamandan Boko Haram, Abu Khalid, Da Wasu 10 A Borno

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.