ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kano Zata Kashe Biliyan ₦8.53bn Wajen Aiwatar Da Wasu Aiyuka

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Kano

Majalisar Zartarwa ta Jihar Kano ta amince da kashe kimanin naira biliyan 8.53 domin aiwatar da manyan ayyukan gine-gine, lafiya, ilimi, samar da ruwan sha da jin dadin jama’a a sassa daban-daban na jihar. An yanke shawarar ne a taron Majalisar na 37 da aka gudanar a ranar Alhamis, 16 ga Janairu, 2026, a gidan gwamnatin Malam Aminu Kano House da ke Asokoro, Abuja.

Da yake yi wa manema labarai bayani bayan taron, Kwamishinan yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya ce kuɗaɗen sun shafi ma’aikatun gwamnati, hukumomi da sassa daban-daban, tare da nufin magance manyan ƙalubale a fannonin ruwan sha, da kiwon lafiya, da hanyoyi da ayyukan jin daɗin jama’a a faɗin jihar.

  • Asiri Ya Tonu: Yadda Aka Kashe Uwa da Ƴaƴanta Shida A Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wata Mata Da ‘Ya’yanta 6 A Kano

A cewarsa, Majalisar ta amince da kashe Naira biliyan 3.1 domin sayen sinadarin tsaftace ruwa (alum) na tsawon watanni shida a shekarar 2026 ƙarƙashin Ma’aikatar Albarkatun Ruwa.

ADVERTISEMENT

Haka kuma, an amince da Naira biliyan 1.7 domin gina hanyar mota daga Chiromawa zuwa Garun Babba a ƙaramar hukumar Garun Malam, tare da Naira miliyan 677.5 domin gyara da sake farfaɗowa da Asibitin Rogo bayan gobarar da ta afka masa.

Sauran kuɗaɗen da aka amince da su sun haɗa da Naira miliyan 520 domin sayen na’urar CT Scan a Asibitin Koyarwa na Muhammad Abdullahi Wase, da Naira miliyan 660.3 domin aikin magudanan ruwa da shimfida tayal a unguwar Ayagi-Aisami da ke ƙaramar hukumar Dala.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Majalisar ta kuma amince da gina masaukin marayu a Gidan Yara na Nassarawa, da gyaran makarantar GJSS Tatsawarki a Kumbotso, da biyan diyya ga manoma da kadarorin da ayyukan hanyoyi da dam-dam suka shafa, tare da yin Allah-wadai da mutuwar wata mara lafiya a Cibiyar Urology ta Abubakar Imam, tana mai jaddada cewa za a ci gaba da bincike har sai an kai ga ƙarshe.

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje
  • Abubakar Sulaiman
    Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Next Post
Ƴan Nijeriya Sun Cire Tiriliyan ₦36.3 Ta ATM Cikin Watanni 6 Duk Da Ƙarin Kuɗin Caji — CBN

Ƴan Nijeriya Sun Cire Tiriliyan ₦36.3 Ta ATM Cikin Watanni 6 Duk Da Ƙarin Kuɗin Caji — CBN

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.