ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da ASUU Za Su Sanya Hannu Kan Sabuwar Yarjejeniya Ranar 14 Ga Janairu

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Asuu

Gwamnatin Tarayya da Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) na shirin sanya hannu kan sabuwar yarjejeniya a ranar Laraba, 14 ga Janairu, domin ƙarfafa zaman lafiyar aiki da inganta yanayin koyo da karatu a jami’o’in Nijeriya. Wannan na ƙunshe ne cikin wata gayyata a hukumance da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta fitar, inda ta gayyaci shugabannin jami’o’in tarayya domin halartar bikin sanya hannu kan yarjejeniyar a Abuja.

Bikin, wanda aka shirya gudanarwa da ƙarfe 11:00 na safe, zai ƙunshi muhimman tanade-tanade da suka haɗa da ƙarin albashi kashi 40 cikin 100 ga malaman jami’a, da kuma inganta tsarin fansho. Daga cikin sabbin sharuɗɗan, farfesoshi za su yi ritaya ne suna da shekaru 70, tare da karɓar fansho da ya kai daidai albashinsu na shekara gaba ɗaya, wata muhimmiyar buƙata da ASUU ta daɗe tana nema.

  • AFCON 2025: Hukumar CAF Ta Sauya Alƙalin Da Zai Jagoranci Wasan Nijeriya Da Algeria
  • ASUU Ta Yi Watsi Da Ƙarin Albashin Kashi 35, Ta Buƙaci A Bai Wa Jami’o’i Isassun Kuɗi

Sabuwar yarjejeniyar ta kuma tanadi sabon tsarin tallafin kuɗaɗe ga jami’o’i, inda za a ware kuɗi na musamman domin bincike, da ɗakunan karatu, da ɗakunan gwaje-gwaje, da kayan aiki da bunƙasa ƙwarewar ma’aikata.

ADVERTISEMENT

Ma’aikatar Ilimin ta bayyana yarjejeniyar a matsayin wani babban ci gaba a tattaunawar da aka daɗe ana yi tsakanin gwamnati da ASUU, tare da nuni da cewa hakan na nuna ƙudirin gwamnati na tabbatar da zaman lafiya a fannin ilimi.

An cimma matsayar yarjejeniyar ne a ranar 23 ga Disamba, 2025, bayan kammala sake tattauna yarjejeniyar 2009 tsakanin Gwamnatin Tarayya da ASUU, lamarin da ya kawo ƙarshen rikicin aiki da ya shafe sama da shekaru 16.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Yarjejeniyar za ta fara aiki daga 1 ga Janairu, 2026, tare da duba ta bayan shekaru uku, kuma ta haɗa da shirin kafa Hukumar Bincike ta Ƙasa wadda za ta tallafa wa bincike da aƙalla kashi ɗaya cikin ɗari na GDP na Nijeriya, daidai da Manufar “Renewed Hope” ta Shugaban Ƙasa.

Asuu
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Wani Mai Taɓin Ƙwaƙwalwa Ya Kashe Soja A Legas

Abubuwan Da Suka Fi Daukar Hankali A Bangaren Tsaron Nijeriya A 2025

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.