ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Da ASUU Za Su Sanya Hannu Kan Sabuwar Yarjejeniya Ranar 14 Ga Janairu

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Asuu

Gwamnatin Tarayya da Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU) na shirin sanya hannu kan sabuwar yarjejeniya a ranar Laraba, 14 ga Janairu, domin ƙarfafa zaman lafiyar aiki da inganta yanayin koyo da karatu a jami’o’in Nijeriya. Wannan na ƙunshe ne cikin wata gayyata a hukumance da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta fitar, inda ta gayyaci shugabannin jami’o’in tarayya domin halartar bikin sanya hannu kan yarjejeniyar a Abuja.

Bikin, wanda aka shirya gudanarwa da ƙarfe 11:00 na safe, zai ƙunshi muhimman tanade-tanade da suka haɗa da ƙarin albashi kashi 40 cikin 100 ga malaman jami’a, da kuma inganta tsarin fansho. Daga cikin sabbin sharuɗɗan, farfesoshi za su yi ritaya ne suna da shekaru 70, tare da karɓar fansho da ya kai daidai albashinsu na shekara gaba ɗaya, wata muhimmiyar buƙata da ASUU ta daɗe tana nema.

  • AFCON 2025: Hukumar CAF Ta Sauya Alƙalin Da Zai Jagoranci Wasan Nijeriya Da Algeria
  • ASUU Ta Yi Watsi Da Ƙarin Albashin Kashi 35, Ta Buƙaci A Bai Wa Jami’o’i Isassun Kuɗi

Sabuwar yarjejeniyar ta kuma tanadi sabon tsarin tallafin kuɗaɗe ga jami’o’i, inda za a ware kuɗi na musamman domin bincike, da ɗakunan karatu, da ɗakunan gwaje-gwaje, da kayan aiki da bunƙasa ƙwarewar ma’aikata.

ADVERTISEMENT

Ma’aikatar Ilimin ta bayyana yarjejeniyar a matsayin wani babban ci gaba a tattaunawar da aka daɗe ana yi tsakanin gwamnati da ASUU, tare da nuni da cewa hakan na nuna ƙudirin gwamnati na tabbatar da zaman lafiya a fannin ilimi.

An cimma matsayar yarjejeniyar ne a ranar 23 ga Disamba, 2025, bayan kammala sake tattauna yarjejeniyar 2009 tsakanin Gwamnatin Tarayya da ASUU, lamarin da ya kawo ƙarshen rikicin aiki da ya shafe sama da shekaru 16.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Yarjejeniyar za ta fara aiki daga 1 ga Janairu, 2026, tare da duba ta bayan shekaru uku, kuma ta haɗa da shirin kafa Hukumar Bincike ta Ƙasa wadda za ta tallafa wa bincike da aƙalla kashi ɗaya cikin ɗari na GDP na Nijeriya, daidai da Manufar “Renewed Hope” ta Shugaban Ƙasa.

Asuu
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Wani Mai Taɓin Ƙwaƙwalwa Ya Kashe Soja A Legas

Abubuwan Da Suka Fi Daukar Hankali A Bangaren Tsaron Nijeriya A 2025

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.