Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya bayyana mamakinsa kan wani ƙuduri a Majalisar Dokokin Amurka da ke neman ƙaƙaba takunkumi ga tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, yana mai cewa lamarin na da alamar tambaya.
Ndume ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi a tashar Channels Television, inda ya ce ya yi mamakin yadda aka ambaci sunan Kwankwaso shi kaɗai cikin ƙudirin, yana mai cewa watakila akwai wasu bayanan sirri da wasu suka sani amma ba kowa ba.
- Gwamnatin Kano Ta Nemi Gwamnatin Tarayya Ta Hana Kwankwaso Shigowa Kano — Buba Galadima
- NNPP Ta Yi Watsi DA Rahoton Hukuncin Amurka Kan Kwankwaso
Ƙudirin mai taken “Nigeria Religious Freedom and Accountability Act of 2026” ya nemi a ƙaƙaba takunkumi, ciki har da hana biza da daskarar da kadarori, kan wasu mutane da ƙungiyoyi, ciki har da Kwankwaso da Miyetti Allah, bisa zargin take ’yancin addini. Matakin na zuwa ne bayan Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake sanya Nijeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargin tauye ’yancin addini.
Sai dai Ndume ya ce idan har Amurka na son taimakawa, ya kamata ta maida hankali kan “mutane na musamman” maimakon lakaba wa ƙasa baki ɗaya suna. A gefe guda, tafiyar Kwankwasiyya ta yi watsi da ƙudirin, tana mai cewa zargin ba shi da tushe kuma na siyasa ne, yayin da har yanzu Kwankwaso bai fitar da wata sanarwa kai tsaye ba kan batun.















Discussion about this post