ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Duƙufa Wajen Gina Ingantattun Rundunonin Tsaro

by Sani Anwar
8 months ago
Tarayya

Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa, ya jaddada aniyar gwamnatin tarayya na gina
ingantattun rundunonin soji, cike da ƙwararru da kuma juriya, domin kare martabar Nijeriya da kuma tallafa wa ci gaban ƙasa.
Musa ya bayyana haka ne a ranar Litinin, a wajen buɗe taron ƙarawa juna sani na ƙasa, wanda aka shirya; domin tunawa da ranar sojojin ƙasar na shekarar 2026 a Abuja.

Ya ce, ma’aikatar tsaro a ƙarƙashin gwamnatin mai ci, tana ba da fifiko kan jin daɗin sojoji da inganta horar da su da inganta koyarwa da kuma faɗaɗa samar da tsaro na cikin gida, domin tabbatar da ɗorewar tsaro na tsawon lokaci.
A cewar tasa, ci gaba da tsare-tsare na dokoki suna farfaɗo da masana’antun tsaro na cikin gida, da ƙarfafa gwiwar kamfanoni masu zaman kansu, samar da ayyukan yi da zurfafa abubuwan cikin gida tare da rage dogaro ga masu samar da kayayyaki na ƙasashen waje.

  • Matakin Kaddamar Da Shekarar Musayar Al’umma Tsakanin Sin Da Afirka Ya Dace Da Ajandar Nahiyar Ta Nan Zuwa 2063
  • An Yi Bikin Murnar Kaddamar Da Shekarar Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Ta Sin Da Afirka A Afirka Ta Kudu

Musa ya bayyana cewa, Nijeriya na amfani da waɗanda suka samu ƙwarewa a cikin gida tare kuma ƙarfafa ƙirƙire-ƙirƙire ta fuskar tsaro da kuma samar da ƙwarewa.
Ya ƙara da cewa, dandali na tsaro da aka samar a cikin gida a yanzu, ya nuna yadda cibiyar masana’antun tsaron Nijeriya ke daɗa ƙarfi da kuma irin gudunmawar da take bayarwa, wajen samar da tsaro da bunƙasar tattalin arziƙin yankin.

ADVERTISEMENT

Game da ayyukan, ministan ya bayyana cewa; ingantacciyar hanyar horar da sojoji ta
musamman da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa tare da abokan hulɗar yanki da na ƙasa da ƙasa, sun inganta musayar bayanan sirri da tasirin aiki, kan barazanar da ke tsakanin ƙasashen duniya.

Ya ƙara da cewa, ci gaba da kai hare-hare da sojoji suka yi a yankunan ƴan ta’adda
daban-daban, sun samu gagarumar nasara, yayin da ingantattun ayyukan sojan ruwa da wayar da kai kan harkokin teku ya daƙile ayyukan miyagun laifuka da kuma kare muhimman kadarorin
ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Har ila yau, Musa ya jaddada cewa; tsaro wani nauyi ne da ya rataya a wuyansa, inda ya yi kira
ga al’umma, sarakunan gargajiya, malaman addini da na ƙananan hukumomi, da su ba da
goyon baya ga ƙoƙarin da ake yi na daƙile ayyukan ta’addanci.

Haka zalika, ya buƙaci mahalarta taron da su samar da shawarwari masu amfani, domin ƙara ƙarfafa gine-ginen tsaron Nijeriya da kuma haɗin kan ƙasa.
Ministan, ya yaba wa shugabannin tsaron soji, bisa jajircewarsu, inda ya tabbatar wa ƴan Nijeriya cewa; sojoji suna da azama da kuma ƙarfin da za su iya karya lagon makiya Nijeriya.
“Nijeriya babbar ƙasa ce, sannan da haɗin kai da juriya, za mu iya shawo kan ƙalubalen da
muke fuskanta da kuma samar da makoma mai inganci,” in ji shi.

Ministan, ya kuma jinjina wa jaruman da suka mutu, suka sadaukar da rayuwarsu wajen kare ƙasa tare da yaba wa ma’aikatan da suka yi aiki bisa jajircewa da kuma ƙwarewa.

Tarayya
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ko Kun San Amfanin Kwanciya Da Bangaren Hagu?
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027:Mata Shida Da Ke Takarar Neman Shugabancin Nijeriya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Dambarwa A Kasuwancin Iyalan Indimi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Illar Shan Taba Sigari Da Dangoginta

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Matawalle Na Amafani Da Jami’an Tsaro Don Tsorata ‘Yan Adawa – Kakakin Gwamnan Zamfara 

Matawalle Na Amafani Da Jami'an Tsaro Don Tsorata 'Yan Adawa - Kakakin Gwamnan Zamfara 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.