ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Duƙufa Wajen Gina Ingantattun Rundunonin Tsaro

by Sani Anwar
5 months ago
Tarayya

Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa, ya jaddada aniyar gwamnatin tarayya na gina
ingantattun rundunonin soji, cike da ƙwararru da kuma juriya, domin kare martabar Nijeriya da kuma tallafa wa ci gaban ƙasa.
Musa ya bayyana haka ne a ranar Litinin, a wajen buɗe taron ƙarawa juna sani na ƙasa, wanda aka shirya; domin tunawa da ranar sojojin ƙasar na shekarar 2026 a Abuja.

Ya ce, ma’aikatar tsaro a ƙarƙashin gwamnatin mai ci, tana ba da fifiko kan jin daɗin sojoji da inganta horar da su da inganta koyarwa da kuma faɗaɗa samar da tsaro na cikin gida, domin tabbatar da ɗorewar tsaro na tsawon lokaci.
A cewar tasa, ci gaba da tsare-tsare na dokoki suna farfaɗo da masana’antun tsaro na cikin gida, da ƙarfafa gwiwar kamfanoni masu zaman kansu, samar da ayyukan yi da zurfafa abubuwan cikin gida tare da rage dogaro ga masu samar da kayayyaki na ƙasashen waje.

  • Matakin Kaddamar Da Shekarar Musayar Al’umma Tsakanin Sin Da Afirka Ya Dace Da Ajandar Nahiyar Ta Nan Zuwa 2063
  • An Yi Bikin Murnar Kaddamar Da Shekarar Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Ta Sin Da Afirka A Afirka Ta Kudu

Musa ya bayyana cewa, Nijeriya na amfani da waɗanda suka samu ƙwarewa a cikin gida tare kuma ƙarfafa ƙirƙire-ƙirƙire ta fuskar tsaro da kuma samar da ƙwarewa.
Ya ƙara da cewa, dandali na tsaro da aka samar a cikin gida a yanzu, ya nuna yadda cibiyar masana’antun tsaron Nijeriya ke daɗa ƙarfi da kuma irin gudunmawar da take bayarwa, wajen samar da tsaro da bunƙasar tattalin arziƙin yankin.

ADVERTISEMENT

Game da ayyukan, ministan ya bayyana cewa; ingantacciyar hanyar horar da sojoji ta
musamman da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa tare da abokan hulɗar yanki da na ƙasa da ƙasa, sun inganta musayar bayanan sirri da tasirin aiki, kan barazanar da ke tsakanin ƙasashen duniya.

Ya ƙara da cewa, ci gaba da kai hare-hare da sojoji suka yi a yankunan ƴan ta’adda
daban-daban, sun samu gagarumar nasara, yayin da ingantattun ayyukan sojan ruwa da wayar da kai kan harkokin teku ya daƙile ayyukan miyagun laifuka da kuma kare muhimman kadarorin
ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Har ila yau, Musa ya jaddada cewa; tsaro wani nauyi ne da ya rataya a wuyansa, inda ya yi kira
ga al’umma, sarakunan gargajiya, malaman addini da na ƙananan hukumomi, da su ba da
goyon baya ga ƙoƙarin da ake yi na daƙile ayyukan ta’addanci.

Haka zalika, ya buƙaci mahalarta taron da su samar da shawarwari masu amfani, domin ƙara ƙarfafa gine-ginen tsaron Nijeriya da kuma haɗin kan ƙasa.
Ministan, ya yaba wa shugabannin tsaron soji, bisa jajircewarsu, inda ya tabbatar wa ƴan Nijeriya cewa; sojoji suna da azama da kuma ƙarfin da za su iya karya lagon makiya Nijeriya.
“Nijeriya babbar ƙasa ce, sannan da haɗin kai da juriya, za mu iya shawo kan ƙalubalen da
muke fuskanta da kuma samar da makoma mai inganci,” in ji shi.

Ministan, ya kuma jinjina wa jaruman da suka mutu, suka sadaukar da rayuwarsu wajen kare ƙasa tare da yaba wa ma’aikatan da suka yi aiki bisa jajircewa da kuma ƙwarewa.

Tarayya
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Matawalle Na Amafani Da Jami’an Tsaro Don Tsorata ‘Yan Adawa – Kakakin Gwamnan Zamfara 

Matawalle Na Amafani Da Jami'an Tsaro Don Tsorata 'Yan Adawa - Kakakin Gwamnan Zamfara 

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.