ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Duƙufa Wajen Gina Ingantattun Rundunonin Tsaro

by Sani Anwar
5 months ago
Tarayya

Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa, ya jaddada aniyar gwamnatin tarayya na gina
ingantattun rundunonin soji, cike da ƙwararru da kuma juriya, domin kare martabar Nijeriya da kuma tallafa wa ci gaban ƙasa.
Musa ya bayyana haka ne a ranar Litinin, a wajen buɗe taron ƙarawa juna sani na ƙasa, wanda aka shirya; domin tunawa da ranar sojojin ƙasar na shekarar 2026 a Abuja.

Ya ce, ma’aikatar tsaro a ƙarƙashin gwamnatin mai ci, tana ba da fifiko kan jin daɗin sojoji da inganta horar da su da inganta koyarwa da kuma faɗaɗa samar da tsaro na cikin gida, domin tabbatar da ɗorewar tsaro na tsawon lokaci.
A cewar tasa, ci gaba da tsare-tsare na dokoki suna farfaɗo da masana’antun tsaro na cikin gida, da ƙarfafa gwiwar kamfanoni masu zaman kansu, samar da ayyukan yi da zurfafa abubuwan cikin gida tare da rage dogaro ga masu samar da kayayyaki na ƙasashen waje.

  • Matakin Kaddamar Da Shekarar Musayar Al’umma Tsakanin Sin Da Afirka Ya Dace Da Ajandar Nahiyar Ta Nan Zuwa 2063
  • An Yi Bikin Murnar Kaddamar Da Shekarar Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Ta Sin Da Afirka A Afirka Ta Kudu

Musa ya bayyana cewa, Nijeriya na amfani da waɗanda suka samu ƙwarewa a cikin gida tare kuma ƙarfafa ƙirƙire-ƙirƙire ta fuskar tsaro da kuma samar da ƙwarewa.
Ya ƙara da cewa, dandali na tsaro da aka samar a cikin gida a yanzu, ya nuna yadda cibiyar masana’antun tsaron Nijeriya ke daɗa ƙarfi da kuma irin gudunmawar da take bayarwa, wajen samar da tsaro da bunƙasar tattalin arziƙin yankin.

ADVERTISEMENT

Game da ayyukan, ministan ya bayyana cewa; ingantacciyar hanyar horar da sojoji ta
musamman da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa tare da abokan hulɗar yanki da na ƙasa da ƙasa, sun inganta musayar bayanan sirri da tasirin aiki, kan barazanar da ke tsakanin ƙasashen duniya.

Ya ƙara da cewa, ci gaba da kai hare-hare da sojoji suka yi a yankunan ƴan ta’adda
daban-daban, sun samu gagarumar nasara, yayin da ingantattun ayyukan sojan ruwa da wayar da kai kan harkokin teku ya daƙile ayyukan miyagun laifuka da kuma kare muhimman kadarorin
ƙasa.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Har ila yau, Musa ya jaddada cewa; tsaro wani nauyi ne da ya rataya a wuyansa, inda ya yi kira
ga al’umma, sarakunan gargajiya, malaman addini da na ƙananan hukumomi, da su ba da
goyon baya ga ƙoƙarin da ake yi na daƙile ayyukan ta’addanci.

Haka zalika, ya buƙaci mahalarta taron da su samar da shawarwari masu amfani, domin ƙara ƙarfafa gine-ginen tsaron Nijeriya da kuma haɗin kan ƙasa.
Ministan, ya yaba wa shugabannin tsaron soji, bisa jajircewarsu, inda ya tabbatar wa ƴan Nijeriya cewa; sojoji suna da azama da kuma ƙarfin da za su iya karya lagon makiya Nijeriya.
“Nijeriya babbar ƙasa ce, sannan da haɗin kai da juriya, za mu iya shawo kan ƙalubalen da
muke fuskanta da kuma samar da makoma mai inganci,” in ji shi.

Ministan, ya kuma jinjina wa jaruman da suka mutu, suka sadaukar da rayuwarsu wajen kare ƙasa tare da yaba wa ma’aikatan da suka yi aiki bisa jajircewa da kuma ƙwarewa.

Tarayya
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Matawalle Na Amafani Da Jami’an Tsaro Don Tsorata ‘Yan Adawa – Kakakin Gwamnan Zamfara 

Matawalle Na Amafani Da Jami'an Tsaro Don Tsorata 'Yan Adawa - Kakakin Gwamnan Zamfara 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.