Wani hadimin tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya zargi ICPC da hana tsohon gwamnan samun kulawar likitansa duk da umarnin kotu da ya ba shi damar ganin likitocinsa ba tare da wata takura ba.
A cewar hadimin Muyiwa Adekeye, likitan El-Rufai ya kai ziyara ofishin ICPC domin tattauna sakamakon wasu gwaje-gwajen lafiya da aka yi masa, amma jami’an hukumar suka hana shi ganawa da tsohon gwamnan, suna mai cewa sai an samu amincewar shugaban hukumar kafin hakan ya yiwu.
Ya kuma yi zargin cewa matar El-Rufai, Hajiya Aishatou, ta fuskanci irin wannan matsala bayan an hana ta kai masa abincin dare a wurin da ake tsare da shi. Ya bayyana matakan a matsayin take haƙƙin da kundin tsarin mulki ya tanada ga wanda ake tsare da shi.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ICPC ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan zarge-zargen ba. El-Rufai na fuskantar shari’a kan wasu zarge-zargen almundahanar kuɗaɗe, zargin da ya sha musantawa.














Discussion about this post