ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Kamfanonin Mai Na Kasashen Waje Na Mana Kafar Ungulu Wajen Samun Danyen Man Nijeriya – Dangote

Ya Yaba Wa NUPRC Bisa Wallafa Ka’idodjin Samar Da Danyen Mai A Gida

by Sani Anwar
2 years ago
dangote

Hukumar Gudanarwar Kamfanonin Ɗangote, ta yaba wa Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriya (NUPRC), bisa yadda take gudanar da ayyuka daban-daban; a kan buƙatun da kamfanin mai yake da shi na samar da ɗanyen mai daga Kamfanonin Mai na Duniya (IOCs), tare kuma da samar da dokoki da tsare-tsaren hada-hadar ɗanyen mai na cikin gida, wanda zai bad a damar aiwatar da gaskiya a kamfanonin mai.

Mataimakin Shugaban Kamfanin Man Fetur da Gas na Kamfanin Ɗangote, Mista Edwin ya bayyana cewa; “Idan aka gabatar da sharuɗɗa tare da ƙa’idojin sayar da ɗanyan man fetir a cikin gida yadda ya kamata, hakan na tabbatar da cewa; za mu yi hulɗa kai tsaye tare da kamfanonin da ke haƙo ɗanyen mai a Nijeriya kamar yadda dokar kamfanoni man fetur (PIA) ta gindaya.”

Edwin ya ƙara da cewa, Kamfanonin Mai na Duniya (IOCs), da ke aiki a Nijeriya; sun ta faman yi wa buƙatun wannan kamfani zagon ƙasa, kan buƙatar samar da ɗanyen mai tare da tace shi a cikin gida.

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da bayyana cewa, idan aka bai wa kamfanin man dakon kaya ta hannun ‘yan kasuwa, wani lokacin farashin ya kan kai dala biyu zuwa dala huɗu (kowace ganga), sama da farashin da Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriya (NUPRC) ta ƙayyade.

“Misali, mun biya dala 96.23 kan kowace ganga ta kayan ɗanyen man Bonga a watan Afrilu (ban da kuɗin sufuri). Farashin ya haɗa da dala 90.15 da kuma dala 5.08 na Kamfanin Albartun Mai na Nijeriya NNPC da kuma dala ɗaya na ‘yankasuwa. Saboda haka, a cikin wannan watan; mun samu damar sayen WTI a kan farashin dala 90.15 da kuma dala 0.93 ciki har da kuɗin sufuri. A lokacin da Kamfanin NNPC ya rage farashinsa, sakamakon yadda kasuwa ta tabbatar da cewa farashin ya yi yawa, sai wasu daga cikin ‘yan kasuwa suka fara neman kimanin dala miliyan huɗu a hannunmu, sama da na kamfanin ɗaukar kaya na ‘Bonny Light’.”

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

Har ila yau, bayanan kafafen sadarwa sun nuna cewa; farashin da ake ba mu, ya fi farashin kasuwa kamar yadda muke ji ko bibiyar waɗannan kafafen sadarwa ko dandamali. Kwanan, dole ta sa muka sanar da Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriya (NUPRC)”,

 

Edwin ya ce, ya kuma buƙaci hukumar da ta sake duba batun farashin.

Martanin na Edwin, ya zo ne daidai lokacin da wata sanarwa; wadda Babban Jami’in Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriyan (NUPRC), Injiniya Gbenga Komolafe; a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin ARISE, inda yake cewa; “kuskure ne mutum kamfanonin mai na ƙasashen waje sun ƙi samar da ɗanyen mai ga masu tacewa na cikin gida, kamar yadda dokar masana’antar mai ta tanadar, akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin mai saya da mai sayarwa.”

Edwin ya bayyana cewa, “Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriyan (NUPRC), ta taimaka wa matatar mai ta Ɗangote ƙwarai da gaske, domin kuwa sun taka muhimiyar rawa don taimaka man wajen samun ɗanyan mai. Duk da haka, akwai yiwuwar wasu ne suka yi wa Shugaban Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriyan (NUPRC) kuskure, shi ya say a yi wannan furuci na cewa, an ƙi sayar mana. Don saita bayanan daidai, muna so mu sake fito da bayanan dalla-dalla a ƙasa.

“Baya ga Kamfanin Kula da Albakatun Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), har zuwa yau ɗin nan; daga hannun wani mai samar da mai a ƙasar nan shi kaɗai muka sayi ɗanyan man fetur (Sapetro). Duk sauran masu hada-hadar man, na tura mu ne ga abokanan kasuwancinsu na waje.

“Waɗannan masu gudanar da kasuwanci a waje, babu wani abin da suke tsinanawa a matsayinsu na waɗanda ke zaune a ƙasashen waje, illa samun rarar man fetur ɗin da ake samarwa da kuma wanda ake amfani das hi a Nijeriya. Ba a yi musu hukunci da dokokin Nijeriya, sannan ba sa biyan haraji a Nijeriyan a kan wannan rara da ba ta dace ba; suke kuma samu.

“Sashen ciniki na ɗaya daga cikin abubuwan da Kamfanonin Mai na Duniyar (IOCs), suka ƙi yarda a sayar mana kai tsaye, inda aka nemi mu nemo waɗanda za su a tsakiya, a sayar musu sai su kuma su sayar mana. Don haka, mun yi tattaunawa da su ta kusan wata tara, amma a ƙarshe said a muka dangana zuwa Kamfanin Kula da Albakatun Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), wanda ya taimaka wajen warware matsalar,” in ji Edwin.

A cewarsa, “Lokacin da muka dangana zuwa kasuwa don sayen ɗanyen man da muke buƙata a watan Agusta, waɗannan masu harkokin kasuwanci a waje cewa suka yi da mu, sun shigo da kayansu Nijeriya a jirgin ɗaukar kaya na Pertamina (mallakin kamfani mai na ƙasar Indunisiya), amma mu ɗan jira mu ga abin da zai faru.

“Wannan ba shi ne karo na farko ba, ya sha faruwa musamman a kan ɗanyen man da muke so saya, amma sai a sayar wa da matatar mai ta Indiya ko wasu daga cikin ƙasashen Asiya tun kafin ma a raba kayan a hukumance a taron rage farashin da Kamfanin Kula da Albakatun Man Fetur na Nijeriya (NNPCL) ke jagoranta.

“Duk da haka, muna buƙatar Hukumar Kula da Man Fetur ta Nijeriyan (NUPRC), ta sake duba batun farashin. Domin kuwa, hukumar ta yi iƙrari da dama na cewa; ya kamata ciniki ya kasance a kan tsarin mai saye da mai sayarwa. Duk da haka, ƙalubalen shi ne; taɓarɓarewar kasuwanci, ta hanyar samun masu saye da dama da kuma masu sayarwa su ma da yawa duk a lokaci guda. Inda kuma a gefe guda matatar man fetur ke buƙatar yin lodi na ɗanyan man fetir a daidai wannan lokaci, sai ga shi kuma an bai wa mutum shi kaɗai a gefe.

“Don kaucewa hauhawar farashin kayayyaki a kasuwa, wajibi ne a samar da iskar gas a cikin gida tare da ƙayyade adadin yadda masu samar da shi za su samar, wanda hakan zai taimaka wajen ƙayyade farashinsa”, in ji Edwin.

dangote
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta
Labaran Kasuwanci

Nijeriya Ta Yi Asarar Biliyoyin Naira Saboda Dakatar Da Shigo Da Motoci Ta Iyakokinta

May 29, 2026
Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA
Labaran Kasuwanci

Farashin Siminti Zai Ragu Idan Farashin Kayan Aiki Ya Sauka – BUA

May 21, 2026
Next Post
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Bunkasa Daga Dukkanin Fannoni Duk Da Sauye-sauye Da Ake Fuskanta

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Bunkasa Daga Dukkanin Fannoni Duk Da Sauye-sauye Da Ake Fuskanta

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

Binciken CGTN Ya Nuna Yadda Cimma Yarjejeniya Tsakanin Amurka Da Iran Ta Fallasa Koma Bayan Tasirin Amurka A Harkokin Duniya

June 18, 2026
Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

June 18, 2026
Kasar Sin: Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Tsakanin Amurka Da Iran A Matakin Farko Na Da Matukar Muhimmanci

Kasar Sin: Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Fahimtar Juna Tsakanin Amurka Da Iran A Matakin Farko Na Da Matukar Muhimmanci

June 18, 2026
Tinubu

Rashin Tsaro: CUPP Ta Goyi Bayan Kiran Da Aka Yi Wa Tinubu Na Jagoranci Ko Murabus

June 18, 2026
Sakon Kasar Sin Game Da Ingiza Tsarin Jagorancin Kare Hakkin Bil’adama 

Sakon Kasar Sin Game Da Ingiza Tsarin Jagorancin Kare Hakkin Bil’adama 

June 18, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Wakiliyar Kasar Sin Ta Bayyana Matsayin Kasar A Gun Taron Majalisar Hakkin Dan Adam Ta MDD

Wakiliyar Kasar Sin Ta Bayyana Matsayin Kasar A Gun Taron Majalisar Hakkin Dan Adam Ta MDD

June 18, 2026
Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano

Hisbah Ta Kama Maza Da Mata 16 A Samamen Dare Kan Zargin Ayyukan Lalata A Kano

June 18, 2026
Wakilin Sin Ya Fayyace Matsayin Kasar Game Da Yadda Wasu Kasashe Ke Tada Hankali Kan “Hukuncin Shari’ar Tekun Kudancin Sin”

Wakilin Sin Ya Fayyace Matsayin Kasar Game Da Yadda Wasu Kasashe Ke Tada Hankali Kan “Hukuncin Shari’ar Tekun Kudancin Sin”

June 18, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.