ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuncin Kotun Ƙoli Ya Kawo Ƙarshen Rarrabuwar PDP — Wike

by Abubakar Sulaiman
2 months ago

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana cewa jam’iyyar PDP ta zama dunƙulalliya kuma babu sauran ɓangarori a cikinta, bayan wani muhimmin hukunci da Kotun ƙoli ta ƙasa ta yanke.

Da yake jawabi a wani taron manema labarai a gidansa da ke Abuja ranar Alhamis, Wike ya ce hukuncin kotun ƙoli ya kawo ƙarshen duk wata taƙaddama kan shugabanci ɓangare biyu da ake yi a cikin jam’iyyar. Ya kuma ƙaryata raɗe-raɗin cewa kotun ta tabbatar da dakatar da Sakataren PDP na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, yana mai cewa babu irin wannan batu da kotun ta yanke hukunci a kai.

Wike ya bayyana cewa kotun ta yi watsi da ɗaukaka ƙarar da aka shigar domin ƙalubalantar hukuncin kotunan baya, lamarin da ya tabbatar da sahihancin babban taron jam’iyyar da kuma shugabancinta na yanzu. Ya ƙara da cewa duk kokarin wasu bangarori na rushe sakamakon taron bai yi nasara ba a kowanne mataki na shari’a.

ADVERTISEMENT

Ya buƙaci ‘yan siyasa da su riƙa aiki bisa tsarin doka, yana gargaɗin cewa duk wani mataki da zai karya kundin tsarin jam’iyya ko dokokin zaɓe zai haifar da matsala. Haka kuma ya yi watsi da muhimmancin wasu da suka fice daga jam’iyyar a lokacin rikicin, yana mai cewa ba su da tasiri a siyasa, amma ya buɗe ƙofar dawowa ga waɗanda suka fita saboda rashin tabbas.

A ƙarshe, Wike ya jaddada cewa PDP na nan daram a matsayin babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya, yana mai cewa hukuncin kotun nasara ce ga bin doka da kuma dimokuraɗiyya, tare da nuna cewa jam’iyyar a shirye take domin taka rawarta yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed
  • Abubakar Sulaiman
    Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa
  • Abubakar Sulaiman
    Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

MASU ALAKA

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed
Siyasa

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

June 27, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Siyasa

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Next Post
Shugaban Saliyo: Sin Na Neman Samun Ci Gaba Tare Da Afirka A Bisa Matakinta Na Soke Harajin Kwastam

Shugaban Saliyo: Sin Na Neman Samun Ci Gaba Tare Da Afirka A Bisa Matakinta Na Soke Harajin Kwastam

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

June 27, 2026

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

June 27, 2026
Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.