ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukuncin Kotun Ƙoli Ya Kawo Ƙarshen Rarrabuwar PDP — Wike

by Abubakar Sulaiman
4 months ago

Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana cewa jam’iyyar PDP ta zama dunƙulalliya kuma babu sauran ɓangarori a cikinta, bayan wani muhimmin hukunci da Kotun ƙoli ta ƙasa ta yanke.

Da yake jawabi a wani taron manema labarai a gidansa da ke Abuja ranar Alhamis, Wike ya ce hukuncin kotun ƙoli ya kawo ƙarshen duk wata taƙaddama kan shugabanci ɓangare biyu da ake yi a cikin jam’iyyar. Ya kuma ƙaryata raɗe-raɗin cewa kotun ta tabbatar da dakatar da Sakataren PDP na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, yana mai cewa babu irin wannan batu da kotun ta yanke hukunci a kai.

Wike ya bayyana cewa kotun ta yi watsi da ɗaukaka ƙarar da aka shigar domin ƙalubalantar hukuncin kotunan baya, lamarin da ya tabbatar da sahihancin babban taron jam’iyyar da kuma shugabancinta na yanzu. Ya ƙara da cewa duk kokarin wasu bangarori na rushe sakamakon taron bai yi nasara ba a kowanne mataki na shari’a.

ADVERTISEMENT

Ya buƙaci ‘yan siyasa da su riƙa aiki bisa tsarin doka, yana gargaɗin cewa duk wani mataki da zai karya kundin tsarin jam’iyya ko dokokin zaɓe zai haifar da matsala. Haka kuma ya yi watsi da muhimmancin wasu da suka fice daga jam’iyyar a lokacin rikicin, yana mai cewa ba su da tasiri a siyasa, amma ya buɗe ƙofar dawowa ga waɗanda suka fita saboda rashin tabbas.

A ƙarshe, Wike ya jaddada cewa PDP na nan daram a matsayin babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya, yana mai cewa hukuncin kotun nasara ce ga bin doka da kuma dimokuraɗiyya, tare da nuna cewa jam’iyyar a shirye take domin taka rawarta yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku
  • Abubakar Sulaiman
    An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro
  • Abubakar Sulaiman
    Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18
  • Abubakar Sulaiman
    Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

MASU ALAKA

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna
Siyasa

Rashin Mulki Ke Firgita Atiku – Kakakin APC Na Kaduna

September 9, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Next Post
Shugaban Saliyo: Sin Na Neman Samun Ci Gaba Tare Da Afirka A Bisa Matakinta Na Soke Harajin Kwastam

Shugaban Saliyo: Sin Na Neman Samun Ci Gaba Tare Da Afirka A Bisa Matakinta Na Soke Harajin Kwastam

LABARAI MASU NASABA

Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

September 12, 2026
An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

September 12, 2026
Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

September 12, 2026
Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Sanata Yari Ya Gudanar Da Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

September 12, 2026
Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

September 12, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Jam’iyyar APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Da Gwamnoni A Nijeriya -Dikko Raɗɗa

September 12, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.