Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana cewa jam’iyyar PDP ta zama dunƙulalliya kuma babu sauran ɓangarori a cikinta, bayan wani muhimmin hukunci da Kotun ƙoli ta ƙasa ta yanke.
Da yake jawabi a wani taron manema labarai a gidansa da ke Abuja ranar Alhamis, Wike ya ce hukuncin kotun ƙoli ya kawo ƙarshen duk wata taƙaddama kan shugabanci ɓangare biyu da ake yi a cikin jam’iyyar. Ya kuma ƙaryata raɗe-raɗin cewa kotun ta tabbatar da dakatar da Sakataren PDP na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, yana mai cewa babu irin wannan batu da kotun ta yanke hukunci a kai.
Wike ya bayyana cewa kotun ta yi watsi da ɗaukaka ƙarar da aka shigar domin ƙalubalantar hukuncin kotunan baya, lamarin da ya tabbatar da sahihancin babban taron jam’iyyar da kuma shugabancinta na yanzu. Ya ƙara da cewa duk kokarin wasu bangarori na rushe sakamakon taron bai yi nasara ba a kowanne mataki na shari’a.
Ya buƙaci ‘yan siyasa da su riƙa aiki bisa tsarin doka, yana gargaɗin cewa duk wani mataki da zai karya kundin tsarin jam’iyya ko dokokin zaɓe zai haifar da matsala. Haka kuma ya yi watsi da muhimmancin wasu da suka fice daga jam’iyyar a lokacin rikicin, yana mai cewa ba su da tasiri a siyasa, amma ya buɗe ƙofar dawowa ga waɗanda suka fita saboda rashin tabbas.
A ƙarshe, Wike ya jaddada cewa PDP na nan daram a matsayin babbar jam’iyyar adawa a Nijeriya, yana mai cewa hukuncin kotun nasara ce ga bin doka da kuma dimokuraɗiyya, tare da nuna cewa jam’iyyar a shirye take domin taka rawarta yadda ya kamata.















Discussion about this post