Jam’iyyar ADC ta nuna damuwarta game da abin da ta kira yunƙurin hana ta fitar da ƴan takara a zaɓe 2027 daga ɓangaren hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC).
Wannan na zuwa ne yayin da INEC, a ranar Laraba da ta gabata, ta shaida wa ADC cewa ba za ta sa ido kan babban taronta na ƙasa ba, wanda ya fara tun daga ranar 7 ga Afrilu 2026, tare da tantance masu neman muƙamai, har zuwa lokacin yanke hukunci kan ƙarar da ke gaban babban kotun tarayya.
- INEC Ta Gargaɗi Jam’iyyu Kan Gudanar Da Babban Taro Ba Tare Da Sanin Ta Ba
- Rikicin PDP: Kotun Koli Ce Kadai Za Ta Warware Lamarin Ba INEC Ba –Bangaren Turaki
Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, ya kuma kare shawarar hukumar zaɓe na rashin sa ido kan gudanar babban taron jam’iyyar a ranar Jumma’a, inda ya yi gargaɗin cewa yin watsi da bin shari’a na iya haifar da mummunan sakamako, wanda jam’iyyun siyasa na iya rasa nasarorin zaɓe saboda rashin bin doka.
Duk da haka, jam’iyyar a ranar Juma’a ta ce aikin zai ci gaba duk da abin da ta kira haramtacciyar ayyukan INEC, tana bayyana matsayar hukumar zaɓe a matsayin wasa da umarnin kotun ɗaukaka ƙara na kiyaye matsayin da ake ciki, wanda ke nufin rashin mutunta kotu da ƙoƙarin bin hanyoyin da suka saɓa wa doka da kuma wace gona da iri wajen gudanar da aikinta.
Sai dai kuma a ranar Alhamis, shugaban jam’iyyar ADC na ƙasa, Sanata Daɓid Mark, yayin da yake jawabi a taron manema labarai a cibiyar Yar’Adua da ke Abuja, wanda tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso da Rotimi Amaechi suka halarta, ya buƙaci shugaban hukumar zaɓe ya yi murabus nan take ko a kori shi da kuma dukka kwamishinonin zaɓe.
Jawabinsa ya biyo bayan matakin da INEC ta ɗauka na cire sunayen kwamitin gudanarwa na jam’iyya ADC da Sanata Daɓid Mark ke jagoranta daga shafinta na intanet da dakatar da amincewa da dukkanin ɓangarorin masu hamayya a jam’iyyar, har sai an kammala shari’ar shugabanci da ke gudana a gaban babban kotun tarayya da ke Abuja.
A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar, Malam Bolaji Abdullahi, ya sa mata hannu, ta bayyana cewa a tsakiyar wannan rikici da ke tasowa shi ne matsayin INEC na cewa ba zai sake karɓar kowanne wasiƙa daga ADC ba har sai an yanke hukunci kan shari’ar da ke gaban babban kotun tarayya.
Abdullahi ya ce, a bayyane lamarin na iya bayyana kamar na tsarin aiki ne, amma a zahiri, yana haifar da rikici kai tsaye kuma mai haɗari ga jaddawalin dokar zaɓe ta shekara ta 2026, wadda ta shimfiɗa ƙa’idoji ciki har da wajabcin sanarwa na kwanaki 21 ga jam’iyyun siyasa na cewa dole ne su kammala muhimman ayyuka na zaɓe.
ADC ta ce ta hanyar shigar da lamarin da ke gaban kotu da kuma yi wa doka karan tsaye, hukumar zaɓe ta raunana kanta kan aikin da take iƙirarin karewa.
Mai magana da yawun jam’iyya ya ce abin da ya fi damunsu shi ne, cewa wannan matsayin ya saba wa yadda INEC ta gudanar da ayyukanta a baya da kuma yadda doka ta tanada.
Ya ce wannan hukuma da ke sa ido, ta tabbatar da shugabancin ADC tun da farko, amma yanzu tana aiki a wata hanya da ta saɓa wa matsayinta na farko.
Saboda haka, jam’iyyar tana kira ga hukumar zaɓe da ta dakatar da wannan matsayi nan take, ta ci gaba da karɓar duk wata wasiƙa ta doka daga ADC kuma ta kiyaye nauyin da tsarin mulki ya tabbatar mata wajen daidaita dukkan jam’iyyun siyasa.
Haka nan kuma ta yi kira ga ƴan Nijeriya da su yi hattara su kasance masu sa ido game da waɗannan mummun mataki na karkatar da dimokuraɗiyyar Nijeriya da tilasta yin mulkin kama-karya a ƙasar nan.
ADC ta tsara gudanar da tantance masu neman muƙami a ranar 7 ga Afrilu 2026 da ɗaukaka ƙara kan aikin tantancewa a 8 ga Afrilu 2026 da gudanar da babban taronta na mazaɓu da na ƙananan hukumomi a 9 ga Afrilu 2026 da ɗaukaka ƙara kan babban taron a ranar 10 ga Afrilu 2026 da babban taronta na jihohi a ranar 11 ga Afrilu 2026 da ɗaukaka ƙara kan babban taronta na jihohi a ranar 12 ga Afrilu 2026 da babban taronta na ƙasa a ranar 14 ga Afrilu 2026.















Discussion about this post