ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Na Yunƙurin Hana Mu Fitar Da Ƴan Takara – ADC

by Abubakar Sulaiman
3 months ago
INEC

Jam’iyyar ADC ta nuna damuwarta game da abin da ta kira yunƙurin hana ta fitar da ƴan takara a zaɓe 2027 daga ɓangaren hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC).

Wannan na zuwa ne yayin da INEC, a ranar Laraba da ta gabata, ta shaida wa ADC cewa ba za ta sa ido kan babban taronta na ƙasa ba, wanda ya fara tun daga ranar 7 ga Afrilu 2026, tare da tantance masu neman muƙamai, har zuwa lokacin yanke hukunci kan ƙarar da ke gaban babban kotun tarayya.

  • INEC Ta Gargaɗi Jam’iyyu Kan Gudanar Da Babban Taro Ba Tare Da Sanin Ta Ba
  • Rikicin PDP: Kotun Koli Ce Kadai Za Ta Warware Lamarin Ba INEC Ba –Bangaren Turaki

Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, ya kuma kare shawarar hukumar zaɓe na rashin sa ido kan gudanar babban taron jam’iyyar a ranar Jumma’a, inda ya yi gargaɗin cewa yin watsi da bin shari’a na iya haifar da mummunan sakamako, wanda jam’iyyun siyasa na iya rasa nasarorin zaɓe saboda rashin bin doka.

ADVERTISEMENT

Duk da haka, jam’iyyar a ranar Juma’a ta ce aikin zai ci gaba duk da abin da ta kira haramtacciyar ayyukan INEC, tana bayyana matsayar hukumar zaɓe a matsayin wasa da umarnin kotun ɗaukaka ƙara na kiyaye matsayin da ake ciki, wanda ke nufin rashin mutunta kotu da ƙoƙarin bin hanyoyin da suka saɓa wa doka da kuma wace gona da iri wajen gudanar da aikinta.

Sai dai kuma a ranar Alhamis, shugaban jam’iyyar ADC na ƙasa, Sanata Daɓid Mark, yayin da yake jawabi a taron manema labarai a cibiyar Yar’Adua da ke Abuja, wanda tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da Peter Obi da Rabiu Musa Kwankwaso da Rotimi Amaechi suka halarta, ya buƙaci shugaban hukumar zaɓe ya yi murabus nan take ko a kori shi da kuma dukka kwamishinonin zaɓe.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Jawabinsa ya biyo bayan matakin da INEC ta ɗauka na cire sunayen kwamitin gudanarwa na jam’iyya ADC da Sanata Daɓid Mark ke jagoranta daga shafinta na intanet da dakatar da amincewa da dukkanin ɓangarorin masu hamayya a jam’iyyar, har sai an kammala shari’ar shugabanci da ke gudana a gaban babban kotun tarayya da ke Abuja.

A cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar, Malam Bolaji Abdullahi, ya sa mata hannu, ta bayyana cewa a tsakiyar wannan rikici da ke tasowa shi ne matsayin INEC na cewa ba zai sake karɓar kowanne wasiƙa daga ADC ba har sai an yanke hukunci kan shari’ar da ke gaban babban kotun tarayya.

Abdullahi ya ce, a bayyane lamarin na iya bayyana kamar na tsarin aiki ne, amma a zahiri, yana haifar da rikici kai tsaye kuma mai haɗari ga jaddawalin dokar zaɓe ta shekara ta 2026, wadda ta shimfiɗa ƙa’idoji ciki har da wajabcin sanarwa na kwanaki 21 ga jam’iyyun siyasa na cewa dole ne su kammala muhimman ayyuka na zaɓe.

ADC ta ce ta hanyar shigar da lamarin da ke gaban kotu da kuma yi wa doka karan tsaye, hukumar zaɓe ta raunana kanta kan aikin da take iƙirarin karewa.

Mai magana da yawun jam’iyya ya ce abin da ya fi damunsu shi ne, cewa wannan matsayin ya saba wa yadda INEC ta gudanar da ayyukanta a baya da kuma yadda doka ta tanada.

Ya ce wannan hukuma da ke sa ido, ta tabbatar da shugabancin ADC tun da farko, amma yanzu tana aiki a wata hanya da ta saɓa wa matsayinta na farko.

Saboda haka, jam’iyyar tana kira ga hukumar zaɓe da ta dakatar da wannan matsayi nan take, ta ci gaba da karɓar duk wata wasiƙa ta doka daga ADC kuma ta kiyaye nauyin da tsarin mulki ya tabbatar mata wajen daidaita dukkan jam’iyyun siyasa.

Haka nan kuma ta yi kira ga ƴan Nijeriya da su yi hattara su kasance masu sa ido game da waɗannan mummun mataki na karkatar da dimokuraɗiyyar Nijeriya da tilasta yin mulkin kama-karya a ƙasar nan.

ADC ta tsara gudanar da tantance masu neman muƙami a ranar 7 ga Afrilu 2026 da ɗaukaka ƙara kan aikin tantancewa a 8 ga Afrilu 2026 da gudanar da babban taronta na mazaɓu da na ƙananan hukumomi a 9 ga Afrilu 2026 da ɗaukaka ƙara kan babban taron a ranar 10 ga Afrilu 2026 da babban taronta na jihohi a ranar 11 ga Afrilu 2026 da ɗaukaka ƙara kan babban taronta na jihohi a ranar 12 ga Afrilu 2026 da babban taronta na ƙasa a ranar 14 ga Afrilu 2026.

 

INEC
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine
  • Abubakar Sulaiman
    Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
  • Abubakar Sulaiman
    Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
  • Abubakar Sulaiman
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Ƙarin Farashin Man Fetur: TUC Ta Shawarci Gwamnati Ta Tallafawa Matatun Mai Na Cikin Gida

Ƙarin Farashin Man Fetur: TUC Ta Shawarci Gwamnati Ta Tallafawa Matatun Mai Na Cikin Gida

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.