ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

by Rabi'u Ali Indabawa
4 weeks ago

Iran ta zargi Amurka da karya yarjejeniyar tsagaita wutar da ke tsakaninsu, bayan da mahukuntan birnin Washington suka bayar da umarnin kai farmakin kan cibiyar harba makamai masu linzami da kuma jiragen ruwan yaƙin Iran a cikin daren da ya gabata.

Mai magana da yawun rundunar sojin Amurka Tim Hawkins, ya ce sun kai farmakin ne domin kare kai daga duk wata barzana da za ta iya fitowa daga dakarun Iran musamman ma a ɓangaren kudancin ƙasar.

Sanarwar ta ƙara da cewa an kai hare-haren ne kan cibiyoyin da Iran ke amfani da su domin harba makamai masu linzami, da kuma jiragen sojin ruwan ƙasar da ke ƙoƙarin dasa nakiyoyi a teku. Kuma wannan shi ne karon farko bayan share makonnin 7 babu tsokana a tsakaninsu.

ADVERTISEMENT

Makomar yarjejeniyar tsagaita wuta da ke tsakanin amurka da iran?

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio da ke ziyara a ƙasar Indiya, ya ce duk da farmakin da dakarunsu suka kai, yarjejeniyar tsagaita wutar na nan daram, kazalika tataunawar da ɓangarorin biyu ke yi a Ƙatar za  ta ci gaba, yana mai cewa ga alama ana ma dab da cimma yarjejeniya.

LABARAI MASU NASABA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

Sai dai ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bayyana harin da Amurka ta kai a yankin Bandar Abas mai tsahar jiragen ruwa a matsayin karya yarjejeniyar tsagaita wuta da ke tsakaninsu, yayin da Rundunar Sojin Iran ɗin ke cewa ta harbo wani jirgi maras matuƙi mallakin Amurka lokacin da ya shiga sararin samaniyar ƙasar.

Inda tattaunawar Amurka da Iran ta fi karkata

Bayanai na nuni da cewa, Amurka da Iran na tattaunawa ne wannan karo kan abubuwa 14 a maimakon 20, amma batun sako wa Iran bilyoyin kuɗaɗe da Amurka ta riƙe a sassan duniya, da janyewar dakarun Amurka daga Gabas ta Tsakiya, da tabbatar da cewa ba wani jami’in sojin Amurka a Hormuz, da kawo ƙarshen duk wasu hare-hare da Isra’ila ke kai wa ƙasar Lebanon da dai sauransu, su ne suka fi ɗaukar hankula a zaman da ake yi a birnin Doha ƙasar Ƙatar.

Tasirin harin Amurka kan Iran a kasuwannin Duniya

Tasirin da wannan mataki ya yi shi ne, haifar da fargaba a tsakanin al’ummomin ƙasashen Yankin Gulf da kuma su kansu al’ummar ƙasar Iran, bayan share makwanni na tsagaita wuta, daga nan kuma an ɗan samu hauhawar farashin man fetur a kasuwannin duniya saboda fargaba.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya
Kasashen Ketare

Yara 14 Sun Rasu Sakamakon Gobara A Kudancin Indiya

June 23, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Kasashen Ketare

Amurka Ta Dakatar Da Takunkumin Man Fetur Kan Iran

June 22, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran
Kasashen Ketare

Iran Ta Ce Shirinta Na Makamai Masu Linzami Ba Ya Cikin Tattaunawa Da Amurka

June 18, 2026
Next Post
Dambazau Ya Karɓi Aiki A Matsayin Jakadan Nijeriya A China

Dambazau Ya Karɓi Aiki A Matsayin Jakadan Nijeriya A China

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.