Iran ta zargi Amurka da karya yarjejeniyar tsagaita wutar da ke tsakaninsu, bayan da mahukuntan birnin Washington suka bayar da umarnin kai farmakin kan cibiyar harba makamai masu linzami da kuma jiragen ruwan yaƙin Iran a cikin daren da ya gabata.
Mai magana da yawun rundunar sojin Amurka Tim Hawkins, ya ce sun kai farmakin ne domin kare kai daga duk wata barzana da za ta iya fitowa daga dakarun Iran musamman ma a ɓangaren kudancin ƙasar.
Sanarwar ta ƙara da cewa an kai hare-haren ne kan cibiyoyin da Iran ke amfani da su domin harba makamai masu linzami, da kuma jiragen sojin ruwan ƙasar da ke ƙoƙarin dasa nakiyoyi a teku. Kuma wannan shi ne karon farko bayan share makonnin 7 babu tsokana a tsakaninsu.
Makomar yarjejeniyar tsagaita wuta da ke tsakanin amurka da iran?
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio da ke ziyara a ƙasar Indiya, ya ce duk da farmakin da dakarunsu suka kai, yarjejeniyar tsagaita wutar na nan daram, kazalika tataunawar da ɓangarorin biyu ke yi a Ƙatar za ta ci gaba, yana mai cewa ga alama ana ma dab da cimma yarjejeniya.
Sai dai ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bayyana harin da Amurka ta kai a yankin Bandar Abas mai tsahar jiragen ruwa a matsayin karya yarjejeniyar tsagaita wuta da ke tsakaninsu, yayin da Rundunar Sojin Iran ɗin ke cewa ta harbo wani jirgi maras matuƙi mallakin Amurka lokacin da ya shiga sararin samaniyar ƙasar.
Inda tattaunawar Amurka da Iran ta fi karkata
Bayanai na nuni da cewa, Amurka da Iran na tattaunawa ne wannan karo kan abubuwa 14 a maimakon 20, amma batun sako wa Iran bilyoyin kuɗaɗe da Amurka ta riƙe a sassan duniya, da janyewar dakarun Amurka daga Gabas ta Tsakiya, da tabbatar da cewa ba wani jami’in sojin Amurka a Hormuz, da kawo ƙarshen duk wasu hare-hare da Isra’ila ke kai wa ƙasar Lebanon da dai sauransu, su ne suka fi ɗaukar hankula a zaman da ake yi a birnin Doha ƙasar Ƙatar.
Tasirin harin Amurka kan Iran a kasuwannin Duniya
Tasirin da wannan mataki ya yi shi ne, haifar da fargaba a tsakanin al’ummomin ƙasashen Yankin Gulf da kuma su kansu al’ummar ƙasar Iran, bayan share makwanni na tsagaita wuta, daga nan kuma an ɗan samu hauhawar farashin man fetur a kasuwannin duniya saboda fargaba.















Discussion about this post