ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

by Rabi'u Ali Indabawa
5 days ago

Iran ta zargi Amurka da karya yarjejeniyar tsagaita wutar da ke tsakaninsu, bayan da mahukuntan birnin Washington suka bayar da umarnin kai farmakin kan cibiyar harba makamai masu linzami da kuma jiragen ruwan yaƙin Iran a cikin daren da ya gabata.

Mai magana da yawun rundunar sojin Amurka Tim Hawkins, ya ce sun kai farmakin ne domin kare kai daga duk wata barzana da za ta iya fitowa daga dakarun Iran musamman ma a ɓangaren kudancin ƙasar.

Sanarwar ta ƙara da cewa an kai hare-haren ne kan cibiyoyin da Iran ke amfani da su domin harba makamai masu linzami, da kuma jiragen sojin ruwan ƙasar da ke ƙoƙarin dasa nakiyoyi a teku. Kuma wannan shi ne karon farko bayan share makonnin 7 babu tsokana a tsakaninsu.

ADVERTISEMENT

Makomar yarjejeniyar tsagaita wuta da ke tsakanin amurka da iran?

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio da ke ziyara a ƙasar Indiya, ya ce duk da farmakin da dakarunsu suka kai, yarjejeniyar tsagaita wutar na nan daram, kazalika tataunawar da ɓangarorin biyu ke yi a Ƙatar za  ta ci gaba, yana mai cewa ga alama ana ma dab da cimma yarjejeniya.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

Sai dai ma’aikatar harkokin wajen Iran ta bayyana harin da Amurka ta kai a yankin Bandar Abas mai tsahar jiragen ruwa a matsayin karya yarjejeniyar tsagaita wuta da ke tsakaninsu, yayin da Rundunar Sojin Iran ɗin ke cewa ta harbo wani jirgi maras matuƙi mallakin Amurka lokacin da ya shiga sararin samaniyar ƙasar.

Inda tattaunawar Amurka da Iran ta fi karkata

Bayanai na nuni da cewa, Amurka da Iran na tattaunawa ne wannan karo kan abubuwa 14 a maimakon 20, amma batun sako wa Iran bilyoyin kuɗaɗe da Amurka ta riƙe a sassan duniya, da janyewar dakarun Amurka daga Gabas ta Tsakiya, da tabbatar da cewa ba wani jami’in sojin Amurka a Hormuz, da kawo ƙarshen duk wasu hare-hare da Isra’ila ke kai wa ƙasar Lebanon da dai sauransu, su ne suka fi ɗaukar hankula a zaman da ake yi a birnin Doha ƙasar Ƙatar.

Tasirin harin Amurka kan Iran a kasuwannin Duniya

Tasirin da wannan mataki ya yi shi ne, haifar da fargaba a tsakanin al’ummomin ƙasashen Yankin Gulf da kuma su kansu al’ummar ƙasar Iran, bayan share makwanni na tsagaita wuta, daga nan kuma an ɗan samu hauhawar farashin man fetur a kasuwannin duniya saboda fargaba.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kasashen Ketare

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

May 30, 2026
Trump Ya Ce Har Yanzu Bai Gamsu Da Tattaunawar Yarjejeniyar Da Ake Yi Da Iran Ba
Kasashen Ketare

Trump Ya Ce Har Yanzu Bai Gamsu Da Tattaunawar Yarjejeniyar Da Ake Yi Da Iran Ba

May 28, 2026
Next Post
Dambazau Ya Karɓi Aiki A Matsayin Jakadan Nijeriya A China

Dambazau Ya Karɓi Aiki A Matsayin Jakadan Nijeriya A China

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.