ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Irin Makaman Da Iran Ta Kai Hari Da Su A Isra’ila

by Rabi'u Ali Indabawa and Abubakar Sulaiman
2 years ago
Iran

Matakin da Iran ta dauka na harba makamai masu linzami masu hanzarin da ya kai 180 a Isra’ila na nuni da cewa Tehran ya yi mummunar barna a harin da aka kai a daren ranar Talata, sabanin harin da aka kai da makami mai linzami a watan Afrilu.

 

Gudun da makaman suke ya sa makaman ballistic suka yi kakkabo su, amma dai rahotannin farko na nuni da cewa ba a samu asarar rai ba cikin Isra’ila da gabar yammacin kogin Jordan, duk da yawan makaman da aka harba.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ga ‘Yan Kasa: Ina Sane Da Tsadar Rayuwar Da Kuke Ciki 
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Rage Kudin Sufuri Da Kashi 40 Ta Hanyar Amfani Da Motoci Masu Iskar Gas

Makamai masu linzami samfurin Tehran Emad da Ghadr, da aka yi amfani da su a farkon wannan shekara, an kiyasta gaggawar tafiyarsu ya ninka sau shida ko fiye da haka, sannann minti 12 kacal suka dauka daga Iran zuwa Isra’ila. Wannan haura fiye da makamain 4,600mph. Amma Iran ta ce ta aika da makami mafi gaggawa Fatteh-2, tare da 10,000mph mai matsakaicin sauri kamar yadda aka kiyasta.

 

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

An yi kiyasin cewa Iran tana da makaman roka kusan 3,000 samfurin ballistic, ko da yake Amurka ta yi lissafin haka ne shekaru biyu da rabi da suka gabata, don haka adadin zai iya karuwa. Tehran za ta so ta ci gaba da rike mafi yawan hannun jarin ta idan har rikici da Isra’ila ya kara ruruwa zuwa babban yaki.

 

An harba makamai masu linzami da yawa a cikin ‘yan mintuna da za su yi wahala su riski inda ake bukata a Isra’la, Saboda suna da kwarewa wajen harbo makami mai linzami.

 

Dakatar da makamin ballistic a cikin jirgin babban aiki ne na da Arrow 3 na Amurka-Isra’ila ke da alhakin dauka tare da mai nisa Arrow 2, wanda aka fara amfani da shi a lokacin yakin Isra’ila da Hamas, na Dabid’s Sling matsakaicin zango ke tallafawa.

 

A watan Afrilu, wani tsohon mai ba da shawara kan harkokin kudi ga shugaban ma’aikatan IDF ya ce makami mai linzami na Arrow yawanci kudinsa ya kai Dala miliyan 3.5 daidai da Fam miliyan (£2.8m), a lokaci guda, kuma Dabid’s Sling mai kakkabo makami kuma kudinsa ya kai Dala miliyan $1m daidai da Fam (£ 800,000).

 

Harbo makamai masu linzami 100 ko fiye zai iya shiga cikin sauƙi zuwa daruruwan miliyoyin daloli – ko da yake makamai masu linzami da kansu za su ci Iran fam 80,000 kowanne ko fiye da haka.

 

A wancan lokacin, Ministan Harkokin Wajen Tehran, Hossein Amir-Abdollahian, ya ce ta bai wa kasashen da ke makotaka da kasar sa’o’i 72 na sanar da kai harin da aka shirya – wanda ya faru makonni biyu bayan da Isra’ila ta kai harin bam a ofishin jakadancin Iran da ke Damascus. A wannan karon, Iran ta dauki matakin ne a cikin kwanaki da Isra’ila ta kashe shugaban Hezbollah, Hassan Nasrallah a ranar Juma’a.

 

…Ana Ci Gaba Da Gwabzawa A Kudancin Lebanon

Rahotanni sun bayyana yadda ake ci gaba da gwaba yaki a tsakanin Israíla da dakarun kungiyar Hezbullah a Kudancin Lebanon inda Isra’ila ta ce an kashe mata sojoji guda takwas a ranar Talata.

 

Israíla ta kaddamar da farmaki ta kasa a kudancin Lebanon kan kungiyar Hezbollah, lamarin da ke kara rura rikicin da ke barazanar barkewar yaki a yankin.

 

Rundunar sojin Isra’ila ta ce dakarunta sun kai farmaki a kauyuka kusa da kan iyaka, yayin da jiragen yaki ke ci gaba da luguden wuta a Lebanon.

 

Wannan ya biyo bayan illar da Isra’ila ta yi wa Hezbollah, ciki har da kisan shugabanta Hassan Nasrallah.

 

Duk da cewa an yi wa Hezbollah illa, amma ta jajirce. Kungiyar ta ci gaba da harba rokoki zuwa arewacin Isra’ila kuma ta ce a shirye take ta abka yaki.

 

Wakilin BBC a Gabas ta Tsakiya Hugo Bachega Beirut ya ce Lebanon ta tashi ne da sabon labarin cewa Isra’ila ta kaddamar da farmaki ta kasa a kudanci.

 

Fargabar ita ce wannan zai iya zama babbar manufa ta yakar Hezbollah, da ta shafe wata tana yaki da Isra’ila a shekarar 2006.

 

A wata sanarwa, rundunar sojin Isra’ila ta ce dakarunta tare da taimakon jiragen yaki da makaman atilare sun fara kai farmaki kan Hezbollah a kauyukan da ke kan iyaka, tana mai cewa sun kasance barazana ga al’ummar Isra’ila da ke arewaci.

 

Ba a dai san yadda yakin zai kaya ba domin fargabar da ake ta nunawa na ruruwan wutar yakin a yankin gabas ta tsakiya tun daga lokacin da Isra’ila ta kaddamar da munanan hare-hare a Gaza.

 

Kaddamar Da Hari Kan Isr’ila

Rundunar sojin Isra’ila ta ce Iran ta kaddamar mata da hare-hare na makamai masu masu linzami.

 

Sanarwar da rundunar sojin Isra’ila ta fitar ta ce hare-haren sun fito ne daga Iran.

 

Iran ta tabbatar da kaddamar da hare-haren kan Isra’ila, kamar yadda Kamfanin Dillacin Labaran kasar IRNA ya tabbatar.

 

Isra’ila ta bukaci ‘yan kasarta su kasance cikin shiri tare da neman wurin fakewa idan har sun ji kara ta gargadi.

 

Masu aiko da rahotanni sun ce an kakkabo wasu makaman a sararin samaniyar Jordan.

 

Kafofin yada labaran Isra’ila sun ce harin makamai masu linzami kusan 100 Iran ta harbo.

 

Sai dai rahotanni sun ce Amurka ta taimaka wa Isra’ila wajen kakkabo makaman kafin isa Tel Abib.

 

Bayanai sun ce wasu makaman da Iran ta harbo sun fada yankunan Falasdinawa

 

A wani labarin kuma, an harbe mutum shida a wani hari da aka kai a Tel Abib, inda akalla wasu mutum bakwai kuma sun jikkata, da dama daga cikinsu sun samu munanan raunuka.

 

‘Yan sanda sun ce harin ya auku ne a kusa da tashar jirgin kasa da ke yankin Jaffa na birnin.

 

Kafofin yada labaran Isra’ila sun ce maharan biyu da aka gani suna sauka daga jirgin kasa, wani mai wucewa ne da kuma wani mai gadi ne suka harbe su.

 

Hotunan sun nuna daya daga cikin maharan dauke da bindiga.

 

Zuwa yanzu ba a san dalilin kai harin ba.

Iran
Rabi'u Ali Indabawa
+ posts Bio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
Iran
Abubakar Sulaiman
Website |  + posts Bio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Kokarin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba A Duniya

Kasar Sin Na Kokarin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.