Gwamnatin mulkin soja ta jamhuriyar Nijar ta dakatar da kusan kafafen yaɗa labarai na Faransa guda 10, tana mai zarginsu da haddasa barazana ga zaman lafiyar jama’a yayin da rikici ke ƙara tsananta tsakanin Nijar da tsohuwar mai mulkin mallakarta, Faransa.
Sanarwar dakatarwar ta fito ne a ranar Juma’a ta gidan talabijin na ƙasar, inda gwamnatin sojan ta ƙara matsa lamba kan tasirin ƙasashen waje da ayyukan kafafen yaɗa labarai na ƙasa da ƙasa a Nijar.
Daga cikin kafafen da aka dakatar akwai France 24, da Radio France Internationale (RFI), da Agence France-Presse (AFP), da TV5Monde, da TF1 Info, da Jeune Afrique da Mediapart. Haka kuma an sanya France Afrique Media da LSI Africa cikin jerin waɗanda aka dakatar.
Mahukuntan Nijar sun ce an ɗauki matakin ne saboda kafafen suna yin abin da zai iya tayar da hargitsi da barazana ga tsaron jama’a, duk da cewa ba su gabatar da cikakkun hujjoji ba kan zargin.
Matakin na zuwa ne yayin da ƙasashen Sahel kamar Mali, da Burkina Faso da Nijar ke ci gaba da nesanta kansu daga Faransa bayan juyin mulkin da ya faru a yankin, tare da ƙarfafa alaƙa da ƙasashen Rasha da China a ɓangaren siyasa da tsaro.















Discussion about this post