Haɗakar jami’an tsaron soji na ruwa da ke aiki, a kudu maso kudu wato OPDS, sun ƙwace Jiragen Ruwa uku, da aka shaƙe da Ɗanyen Mai, da aka sato. Jiregen Man uku da jami’an suka kama tare da kuma waɗanda ake zargi, a garin Kalaba na jihar, an ƙiyasta, ya kai na sama da Naira biliyan 4.2.
Kwamandan jami’an tsaron na haɗaka, Olugbenga Oladipo ne, ya shedawa manema labarai wannan nasarar a garin Kalaba. A cewarsa, jami’an, sun gudanar da aikin ne, a ranar 8, na watan Afirlun 2026, bayan da jami’an suka samu bayanana siirii, inda suka kama Jirge biyu, a MT Mkpodu da kuma a MT Westaf, Kalaba.
- Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
- Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
- Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
- ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP
- An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
A cewarsa, ana zargin an yo dakon Ɗanyen Man da aka sato ne, inda kuma Jirgin, ke ɗauke da ma’aikata 26 waɗanda, duk an kama su. “An kama wata motar Tanka da ake ƙoƙarin zuba Ɗanyen Man a cikinta a Mkpodu wacce kuma ke ɗauke da aƙalla metric tan 480, na Ɗanyen Man da ake zargin, an sato, Inji shi. “An kuma kama wata motar Tankar Mai a Westaf, da ke ɗauke da kimanin metric tan 459, na Ɗanyen Man da ake zargin an sato, “ A cewarsa.
Ya ƙara da cewa, bayan da jami’an suka kama Jiragen, sun buƙaci ɗaukin jami’an soji na sama, inda suka turo Jirgin sama mai saukar Ungulu, domin taiamaka wa, a gudanar da aikin, a cikin nasara.
Ya ƙara da cewa, biyo bayan ci gaba da sintirin da jami’an suka gudanar, sun kuma gano Jigin Ruwa na uku, a MT Stellos a ranar 10 na watan Afirilun 2026, da shima yake shaƙe da Ɗanyen Man da ake zargi, na sata ne.
Ya kuma sanar da ƙoƙarin da ake ci gaba da yi, na daƙile satar Ɗanyen Mai, a yankin, bisa haɗka da sauran hukumomin tsaro, musamman ta hanyar ƙara ƙarfafa, ayyukan sanya ido.
Ya ce, an kuma yi bajin kolin waɗanda aka ake zargin a rundunar jami’an tsaron na ruwa da ke a garin na Kalaba.
Oladipo ya ƙara jaddada ƙudurin jami’an na daƙile duk wasu ayyuka, na satar ɗanyen Mai da kuma duk wani yunƙurin zagon ƙasa, ga tattalin arzikin ƙasar nan, a yankin
Shi kuwa a na sa jawabin Kwamanda rundunar Ruwa na yankin Gabas Chidozie Okehie ya bayyana cewa, a yanzu haka, rundunar na kan bibiyar ƙarin wasu da ake zargi, ɓarayin ɗanyen Mai ne, a yankin.















Discussion about this post