Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Murtala Sule Garo murna bayan rantsar da shi a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan Jihar Kano.
Tinubu ya bayyana jin daɗinsa, ya kuma yaba da yadda aka gudanar da nadin cikin tsari da bin doka.
Rantsar da Garo ya biyo bayan amincewar Majalisar Dokokin Jihar Kano da kuma kammala dukkan matakan da doka ta tanada kafin a naɗa shi a matsayin mataimakin gwamna.
An gudanar da bikin rantsuwar a Fadar Gwamnatin Kano, inda manyan jami’an gwamnati, ‘yan siyasa da masu ruwa da tsaki suka halarta, ciki har da tsoffin gwamnoni da wasu manyan jiga-jigan ƙasa.
Garo ya karɓi mukamin ne bayan murabus ɗin tsohon mataimakin gwamna, abin da ya haifar da sabon sauyi a tsarin shugabancin jihar.
Wannan lamari na daga cikin manyan sauye-sauyen siyasa a Kano, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen tunkarar zaɓen 2027.















Discussion about this post