Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya buƙaci matasan Nijeriya da su taka muhimmiyar rawa a gaba wajen kare wa da kuma ƙarfafa dimokuraɗiyyar ƙasar, yana mai bayyana su a matsayin ginshiƙi da tasiri ga zaman lafiya da makomar ƙasa.
Da yake jawabi a kan sauye-sauyen da ake yi a ƙasa a halin yanzu, Yilwatda ya ƙarfafa matasa musamman masu shekaru tsakanin 25 zuwa 55 da su ɗauki alhakin kare tsarin dimokuraɗiyya, tare da ƙin amincewa da yunƙurin wasu ’yan siyasa masu son zuciya da ke ƙoƙarin kawo cikas ga ci gaban ƙasa.
Ya ce wannan kira ya zama dole duba da yadda wasu ɓangarorin siyasa ke yunƙurin yaɗa manufofi na son rai, tare da ruɗar da jama’a game da manufar da sakamakon sauye-sauyen da gwamnatin yanzu ke aiwatarwa.
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan yaɗa labarai, Abimbola Tooki, ya rattaba wa hannu, ya ce: “Dimokuraɗiyyar Nijeriya na cikin wani muhimmin mataki. Nauyin kare ta da kuma tabbatar da dorewarta yana kan matasa, waɗanda ke da ƙarfi, ƙirƙira da kishin ƙasa da ake buƙata domin ciyar da ƙasa gaba. Bai kamata mu bari waɗanda ba su da sahihan mafita su ruɗi jama’a ko su dakile nasarorin da aka samu ba.”
Yilwatda ya bayyana cewa APC ta zama jam’iyya mai dogaro da matasa, inda fiye da rabin mambobinta matasa ne, abin da ya ce ya nuna tsari na musamman na haɗa kowa da kowa, sabunta shugabanci da kuma bunƙasa matasa.
Ya ƙara da cewa fitowar matashi a matsayin shugaban jam’iyyar na ƙasa a karon farko tun bayan kafuwarta alama ce ta ƙudirin bai wa matasa dama da kuma daidaita tsarin jam’iyyar da yanayin yawan al’ummar Nijeriya.
A cewarsa, bai wa matashi wannan matsayi na nuna amincewa da ƙwarewa da hangen nesa na matasa, tare da ƙarfafa ra’ayin cewa dorewar dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa na rataye ne a kan shigar su a harkokin mulki da sauye-sauye.
Shugaban APC ya kuma yi gargaɗi game da bai wa mutanen da ke bin son rai makomar ƙasa, musamman waɗanda ya zarga da neman shugabanci “ko ta halin kaka,” yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasa cikin rashin tabbas.
Ya amince cewa sauye-sauyen da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na tattare da ƙalubale, amma ya jaddada cewa suna da muhimmanci domin samar da daidaiton tattalin arziki da ci gaba mai ɗorewa.
Yilwatda ya ce alamun farko sun nuna cewa sauye-sauyen na taimakawa wajen sake fasalin Nijeriya zuwa tafarkin ci gaba mai ɗorewa, ladabtar da harkokin kuɗi da kuma ƙara ƙwarewa a kasuwannin duniya.















Discussion about this post