ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar APC Ta Bukaci Matasa Su Jagoranci Kare Dimokuraɗiyyar Nijeriya

by Muhammad
1 month ago

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya buƙaci matasan Nijeriya da su taka muhimmiyar rawa a gaba wajen kare wa da kuma ƙarfafa dimokuraɗiyyar ƙasar, yana mai bayyana su a matsayin ginshiƙi da tasiri ga zaman lafiya da makomar ƙasa.

Da yake jawabi a kan sauye-sauyen da ake yi a ƙasa a halin yanzu, Yilwatda ya ƙarfafa matasa musamman masu shekaru tsakanin 25 zuwa 55 da su ɗauki alhakin kare tsarin dimokuraɗiyya, tare da ƙin amincewa da yunƙurin wasu ’yan siyasa masu son zuciya da ke ƙoƙarin kawo cikas ga ci gaban ƙasa.

Ya ce wannan kira ya zama dole duba da yadda wasu ɓangarorin siyasa ke yunƙurin yaɗa manufofi na son rai, tare da ruɗar da jama’a game da manufar da sakamakon sauye-sauyen da gwamnatin yanzu ke aiwatarwa.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan yaɗa labarai, Abimbola Tooki, ya rattaba wa hannu, ya ce: “Dimokuraɗiyyar Nijeriya na cikin wani muhimmin mataki. Nauyin kare ta da kuma tabbatar da dorewarta yana kan matasa, waɗanda ke da ƙarfi, ƙirƙira da kishin ƙasa da ake buƙata domin ciyar da ƙasa gaba. Bai kamata mu bari waɗanda ba su da sahihan mafita su ruɗi jama’a ko su dakile nasarorin da aka samu ba.”

Yilwatda ya bayyana cewa APC ta zama jam’iyya mai dogaro da matasa, inda fiye da rabin mambobinta matasa ne, abin da ya ce ya nuna tsari na musamman na haɗa kowa da kowa, sabunta shugabanci da kuma bunƙasa matasa.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Ya ƙara da cewa fitowar matashi a matsayin shugaban jam’iyyar na ƙasa a karon farko tun bayan kafuwarta alama ce ta ƙudirin bai wa matasa dama da kuma daidaita tsarin jam’iyyar da yanayin yawan al’ummar Nijeriya.

A cewarsa, bai wa matashi wannan matsayi na nuna amincewa da ƙwarewa da hangen nesa na matasa, tare da ƙarfafa ra’ayin cewa dorewar dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa na rataye ne a kan shigar su a harkokin mulki da sauye-sauye.

Shugaban APC ya kuma yi gargaɗi game da bai wa mutanen da ke bin son rai makomar ƙasa, musamman waɗanda ya zarga da neman shugabanci “ko ta halin kaka,” yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasa cikin rashin tabbas.

Ya amince cewa sauye-sauyen da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na tattare da ƙalubale, amma ya jaddada cewa suna da muhimmanci domin samar da daidaiton tattalin arziki da ci gaba mai ɗorewa.

Yilwatda ya ce alamun farko sun nuna cewa sauye-sauyen na taimakawa wajen sake fasalin Nijeriya zuwa tafarkin ci gaba mai ɗorewa, ladabtar da harkokin kuɗi da kuma ƙara ƙwarewa a kasuwannin duniya.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
An Nuna Al’Adun Gargajiyar Kasar Sin A Karon Farko Yayin Bikin Murnar Samun ’Yancin Kan Kasar Togo

An Nuna Al’Adun Gargajiyar Kasar Sin A Karon Farko Yayin Bikin Murnar Samun ’Yancin Kan Kasar Togo

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.