ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar APC Ta Bukaci Matasa Su Jagoranci Kare Dimokuraɗiyyar Nijeriya

by Muhammad
2 months ago

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya buƙaci matasan Nijeriya da su taka muhimmiyar rawa a gaba wajen kare wa da kuma ƙarfafa dimokuraɗiyyar ƙasar, yana mai bayyana su a matsayin ginshiƙi da tasiri ga zaman lafiya da makomar ƙasa.

Da yake jawabi a kan sauye-sauyen da ake yi a ƙasa a halin yanzu, Yilwatda ya ƙarfafa matasa musamman masu shekaru tsakanin 25 zuwa 55 da su ɗauki alhakin kare tsarin dimokuraɗiyya, tare da ƙin amincewa da yunƙurin wasu ’yan siyasa masu son zuciya da ke ƙoƙarin kawo cikas ga ci gaban ƙasa.

Ya ce wannan kira ya zama dole duba da yadda wasu ɓangarorin siyasa ke yunƙurin yaɗa manufofi na son rai, tare da ruɗar da jama’a game da manufar da sakamakon sauye-sauyen da gwamnatin yanzu ke aiwatarwa.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan yaɗa labarai, Abimbola Tooki, ya rattaba wa hannu, ya ce: “Dimokuraɗiyyar Nijeriya na cikin wani muhimmin mataki. Nauyin kare ta da kuma tabbatar da dorewarta yana kan matasa, waɗanda ke da ƙarfi, ƙirƙira da kishin ƙasa da ake buƙata domin ciyar da ƙasa gaba. Bai kamata mu bari waɗanda ba su da sahihan mafita su ruɗi jama’a ko su dakile nasarorin da aka samu ba.”

Yilwatda ya bayyana cewa APC ta zama jam’iyya mai dogaro da matasa, inda fiye da rabin mambobinta matasa ne, abin da ya ce ya nuna tsari na musamman na haɗa kowa da kowa, sabunta shugabanci da kuma bunƙasa matasa.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Ya ƙara da cewa fitowar matashi a matsayin shugaban jam’iyyar na ƙasa a karon farko tun bayan kafuwarta alama ce ta ƙudirin bai wa matasa dama da kuma daidaita tsarin jam’iyyar da yanayin yawan al’ummar Nijeriya.

A cewarsa, bai wa matashi wannan matsayi na nuna amincewa da ƙwarewa da hangen nesa na matasa, tare da ƙarfafa ra’ayin cewa dorewar dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa na rataye ne a kan shigar su a harkokin mulki da sauye-sauye.

Shugaban APC ya kuma yi gargaɗi game da bai wa mutanen da ke bin son rai makomar ƙasa, musamman waɗanda ya zarga da neman shugabanci “ko ta halin kaka,” yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasa cikin rashin tabbas.

Ya amince cewa sauye-sauyen da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na tattare da ƙalubale, amma ya jaddada cewa suna da muhimmanci domin samar da daidaiton tattalin arziki da ci gaba mai ɗorewa.

Yilwatda ya ce alamun farko sun nuna cewa sauye-sauyen na taimakawa wajen sake fasalin Nijeriya zuwa tafarkin ci gaba mai ɗorewa, ladabtar da harkokin kuɗi da kuma ƙara ƙwarewa a kasuwannin duniya.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
An Nuna Al’Adun Gargajiyar Kasar Sin A Karon Farko Yayin Bikin Murnar Samun ’Yancin Kan Kasar Togo

An Nuna Al’Adun Gargajiyar Kasar Sin A Karon Farko Yayin Bikin Murnar Samun ’Yancin Kan Kasar Togo

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.