ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar APC Ta Bukaci Matasa Su Jagoranci Kare Dimokuraɗiyyar Nijeriya

by Muhammad
3 months ago

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya buƙaci matasan Nijeriya da su taka muhimmiyar rawa a gaba wajen kare wa da kuma ƙarfafa dimokuraɗiyyar ƙasar, yana mai bayyana su a matsayin ginshiƙi da tasiri ga zaman lafiya da makomar ƙasa.

Da yake jawabi a kan sauye-sauyen da ake yi a ƙasa a halin yanzu, Yilwatda ya ƙarfafa matasa musamman masu shekaru tsakanin 25 zuwa 55 da su ɗauki alhakin kare tsarin dimokuraɗiyya, tare da ƙin amincewa da yunƙurin wasu ’yan siyasa masu son zuciya da ke ƙoƙarin kawo cikas ga ci gaban ƙasa.

Ya ce wannan kira ya zama dole duba da yadda wasu ɓangarorin siyasa ke yunƙurin yaɗa manufofi na son rai, tare da ruɗar da jama’a game da manufar da sakamakon sauye-sauyen da gwamnatin yanzu ke aiwatarwa.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara na musamman kan yaɗa labarai, Abimbola Tooki, ya rattaba wa hannu, ya ce: “Dimokuraɗiyyar Nijeriya na cikin wani muhimmin mataki. Nauyin kare ta da kuma tabbatar da dorewarta yana kan matasa, waɗanda ke da ƙarfi, ƙirƙira da kishin ƙasa da ake buƙata domin ciyar da ƙasa gaba. Bai kamata mu bari waɗanda ba su da sahihan mafita su ruɗi jama’a ko su dakile nasarorin da aka samu ba.”

Yilwatda ya bayyana cewa APC ta zama jam’iyya mai dogaro da matasa, inda fiye da rabin mambobinta matasa ne, abin da ya ce ya nuna tsari na musamman na haɗa kowa da kowa, sabunta shugabanci da kuma bunƙasa matasa.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Ya ƙara da cewa fitowar matashi a matsayin shugaban jam’iyyar na ƙasa a karon farko tun bayan kafuwarta alama ce ta ƙudirin bai wa matasa dama da kuma daidaita tsarin jam’iyyar da yanayin yawan al’ummar Nijeriya.

A cewarsa, bai wa matashi wannan matsayi na nuna amincewa da ƙwarewa da hangen nesa na matasa, tare da ƙarfafa ra’ayin cewa dorewar dimokuraɗiyya da ci gaban ƙasa na rataye ne a kan shigar su a harkokin mulki da sauye-sauye.

Shugaban APC ya kuma yi gargaɗi game da bai wa mutanen da ke bin son rai makomar ƙasa, musamman waɗanda ya zarga da neman shugabanci “ko ta halin kaka,” yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasa cikin rashin tabbas.

Ya amince cewa sauye-sauyen da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na tattare da ƙalubale, amma ya jaddada cewa suna da muhimmanci domin samar da daidaiton tattalin arziki da ci gaba mai ɗorewa.

Yilwatda ya ce alamun farko sun nuna cewa sauye-sauyen na taimakawa wajen sake fasalin Nijeriya zuwa tafarkin ci gaba mai ɗorewa, ladabtar da harkokin kuɗi da kuma ƙara ƙwarewa a kasuwannin duniya.

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
  • Muhammad
    ‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Next Post
An Nuna Al’Adun Gargajiyar Kasar Sin A Karon Farko Yayin Bikin Murnar Samun ’Yancin Kan Kasar Togo

An Nuna Al’Adun Gargajiyar Kasar Sin A Karon Farko Yayin Bikin Murnar Samun ’Yancin Kan Kasar Togo

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.