Wani sabon sauyin siyasa na kunno kai a Jihar Zamfara bayan tsohon sanata, Kabiru Garba Marafa, tare da mabiyansa sun amince da rungumar jam’iyyar ADC a matsayin dandamalin siyasar da zasu yi amfani da shi gabanin zaɓen 2027.
An cimma wannan matsaya ne bayan wani taron sirri na ƙungiyar siyasar Marafa da aka gudanar a Jihar Kaduna, inda manyan jiga-jigan ƙungiyar suka tattauna kan makomar tafiyarsu ta siyasa.
- Gwamnatin Tarayya Na Da laifin Kan Hauhawar Farashin Abinci – Marafan Gonin Gora
- Kasar Sin Na Maraba Da Shirin Tsagaita Wuta A Rikicin Iran
A wata sanarwa da sakataren ƙungiyar, Aminu A. Jelani, ya fitar, an ce matakin ya biyo bayan “dogon nazari da tuntuɓa kan halin siyasar da ake ciki,” inda aka amince baki ɗaya da ɗaukar ADC a matsayin sabuwar jam’iyyar tafiyar tasu.
Sanarwar ta ƙara da cewa an tabbatar da wannan matsaya ta hanyar ƙuri’ar amincewa daga mahalarta taron, tare da umartar mambobi a ƙananan hukumomi 14 na Zamfara da su fara rajista cikin gaggawa tare da ƙarfafa wayar da kan jama’a a matakin tushe.
Haka kuma, an bayyana cewa wannan mataki ya biyo bayan gayyata daga shugabancin ADC, inda tsohon Sufeto Janar na ’yan sanda, Mohammed Dikko Abubakar, ya taka rawa wajen haɗa ɓangarorin biyu. Ƙungiyar ta jaddada aniyarta na aiki da jam’iyyar cikin gaskiya da haɗin kai, tare da mai da hankali kan inganta shugabanci nagari, adalci da ɗora al’umma a gaba.















Discussion about this post