Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya amsa tambayar da aka yi masa a yau Asabar 15 ga watan nan, dangane da ziyarar da wasu manyan jami’an gwamnatin kasar Japan suka yi a haikalin Yasukuni a ranar, wato wurin da aka ajiye alluna masu dauke da sunayen manyan kusoshin kasar da suka aikata munanan laifukan yaki yayin yakin duniya na biyu, inda ya yi Allah wadai da wannan aika-aika, tare da nuna matukar rashin jin dadi da takaici ga Japan.
Kakakin ya ce, Japan ta taba kaddamar da yake-yake na kutse a yayin yakin duniya na biyu, inda ta aikata munanan laifukan yaki na rashin mutunci. Haikalin Yasukuni, ya kasance alama kuma hanyar da Japan take bi wajen ci gaba da yayata ra’ayin nuna fin karfin soja. Wasu mutane 14 da aka rubuta sunayensu a alluna na haikalin, jagorori ne da suka aikata munanan laifukan kaddamar da yakin kutse, al’amarin da ya sa wurin ya kasance ainihin haikalin masu aikata laifukan yaki.
Kakakin ya kara da cewa, kara fahimtar abubuwan tarihi daidai, babban abu ne mafi muhimmanci game da dawowar Japan cikin sassan kasa da kasa bayan yakin duniya na biyu, kana tushen siyasa na raya dangantaka tsakanin Japan da kasashe makwabtanta, kuma muhimmin ma’aunin tantance cewa shi ne ko Japan za ta iya cika alkawarinta na samar da ci gaba cikin lumana ko kuma a’a.
Albarkacin ranar cika shekaru 81 da mika wuya da Japan ta yi a yakin duniya na biyu, firaministar kasar, Sanae Takaichi, ta bayar da kudin hadaya ga haikalin Yasukuni. Kazalika, akwai wasu manyan ’yan siyasar Japan wadanda suka ziyarci wurin, ciki har da ministan tsaron kasar, al’amarin da ya gamu da babbar adawa daga wurin masu son zaman lafiya na cikin gidan kasar Japan. (Murtala Zhang)














