ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Shell Ya Yi Alƙawarin Zuba Jarin Dala Biliyan 20 A Najeriya Bayan Dala Biliyan 7 Da Aka Kashe – NNPCL GCEO

by Sani Anwar and Sulaiman
5 months ago
Shell

Shugaban Gudanarwa na Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), Mista Bashir Bayo Ojulari, ya bayyana cewa Kamfanin ‘Shell Petroleum Development Company’ ya kuduri aniyar neman ƙarin damar zuba jari na kimanin dala biliyan 20 a Nijeriya cikin shekaru biyu masu zuwa, bayan sabunta ƙwarin-gwiwar masu zuba jari da gyare-gyaren Gwamnati suka haifar kwanan nan.

 

Ojulari ya bayyana hakan ne yayin da yake yi wa manema labarai bayani a Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja, game da manufar wani ƙudiri da aka gabatar wa Shugaba Bola Tinubu, yana mai nuna tasirin Umarnin Zartarwa da aka bayar a shekarar 2025 don jawo hankalin zuba jari kai-tsaye na ƙasashen waje (FDI) a fannin Mai da iskar Gas na Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • Mazauna Bauchi Na Kokawa Kan Tsadar Farashin Acaba Duk Da Raguwar Farashin Mai
  • Cinikayyar Waje Ta Jihar Xinjiang Ta Kai Sabon Matsayin Ci Gaba A 2025

A cewarsa, Umarnin Zartarwa, wanda aka gabatar bayan aiwatar da Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA), an tsara su ne don inganta gasa a Najeriya a fannin zuba jarin makamashi a duniya, a tsakanin gasa mai tsauri daga wasu ƙasashen Afirka, Guyana da wasu sassan Gabas mai nisa.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A cewarsa: “Gasar saka hannun jari ta duniya ce; kuma wasu ƙasashe suna canza manufofinsu ta hanyar da ta dace don jawo hankalin masu zuba jari. Ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da Shugaba Tinubu ya yi shi ne gabatar da Umarnin Zartarwa (Executive Order), wanda ya ƙara wa masu zuba jari ƙwarin-gwiwa”, in ji Ojulari.

 

Ya bayyana cewa, bayyana manufofi da sassaucin da Gwamnatin Tarayya ta nuna sun bai wa Shell damar kammala raba kadarorin haɗin-gwiwa na ƙasashen waje, waɗanda aka mayar wa Kamfanin Renaissance Africa Energy Company. “Kammala wannan ciniki ya nuna wa duniya jajircewar Shugaban Ƙasa na baiwa masu zuba jari damar saka hannun-jari ba kawai ba, har ma da fita idan ya zama dole – saboda duniyar saka hannun jari tana da ƙarfi sosai”, in ji shi.

 

Ojulari ya ce nasarar da aka samu wajen rage farashin ya ƙara wa ƙasashen duniya ƙwarin-gwiwa; kuma ya yi tasiri kai-tsaye kan shawarwarin saka hannun jari na Shell a Najeriya. Ya bayyana cewa Shell ta ɗauki Matakin Zuba Jari na Ƙarshe (FID) na dala biliyan 5 don haɓɓaka filin Mai na Bonga, sannan kuma ta sake zuba jari na dala biliyan 2 a wani aikin haɓɓaka iskar Gas mai zurfi wanda aka sani da HI. “A jimilla, Shell ta riga ta zuba jari sama da dala biliyan 7 tun bayan sanarwar wannan tallafin. Za ku iya fahimtar abin da wannan ke nufi idan aka kwaikwayi irin wannan ƙwarin-gwiwa ga sauran masu zuba jari”, in ji shi.

 

Shugaban NNPCL ya bayyana cewa Shell yanzu ta tabbatar wa Shugaba Tinubu shirye-shiryen neman sabbin damar saka hannun-jari da darajarsu ta kai dala biliyan 20 a cikin shekaru masu zuwa; wanda hakan zai kara ƙarfafa sha’awar Najeriya a matsayin wurin zuba jari a makamashi.

 

Ojulari ya kuma bayyana cewa ana cigaba da tattaunawa kan babban aikin Shell na gaba – aikin Bonga South-West – wanda aka ƙiyasta zai buƙaci kashe jari kusan dala biliyan 10, banda manyan kuɗaɗen gudanarwa.

 

Ya jaddada cewa bayan alƙaluman kuɗi, jarin zai sami fa’idodi masu yawa na zamantakewa da tattalin arziki ga ƴan Najeriya, gami da samar da ayyukan-yi, da kuma farfaɗo da ƙarfin masana’antu na gida.

 

“Waɗannan manyan alƙaluma suna fassara zuwa ƙarin ayyuka, yayin gini da aiwatar da ayyuka. Ƴan Najeriya za su sami damarmaki dayawa don shiga; kuma wuraren masana’antu waɗanda suka kasance ba tare da aiki ba na tsawon shekaru saboda rashin ayyuka za su dawo rayuwa”, in ji shi.

 

Ojulari ya yabawa shugabancin Shugaba Tinubu, yana mai bayyana shi a matsayin mai amfani da tasiri maimakon yin magana mai daɗi, musamman a fannin gaskiya da jajircewa ga shirin gwamnati na ‘Sabuntawa da Fata’.

 

Ya bayyana fatan cewa ɗorewar manufofi za ta cigaba da buɗe sabbin hanyoyin saka hannun-jari kai-tsaye ga masana’antar Mai da iskar Gas ta Nijeriya.

Shell
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Shell
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post

Gwamnatin Zamfara Ta Ɓullo Da Shirin Amfana Da Ma'adanai Ga Al'umma Jihar

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.