ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Shell Ya Yi Alƙawarin Zuba Jarin Dala Biliyan 20 A Najeriya Bayan Dala Biliyan 7 Da Aka Kashe – NNPCL GCEO

by Sani Anwar and Sulaiman
4 months ago
Shell

Shugaban Gudanarwa na Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), Mista Bashir Bayo Ojulari, ya bayyana cewa Kamfanin ‘Shell Petroleum Development Company’ ya kuduri aniyar neman ƙarin damar zuba jari na kimanin dala biliyan 20 a Nijeriya cikin shekaru biyu masu zuwa, bayan sabunta ƙwarin-gwiwar masu zuba jari da gyare-gyaren Gwamnati suka haifar kwanan nan.

 

Ojulari ya bayyana hakan ne yayin da yake yi wa manema labarai bayani a Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja, game da manufar wani ƙudiri da aka gabatar wa Shugaba Bola Tinubu, yana mai nuna tasirin Umarnin Zartarwa da aka bayar a shekarar 2025 don jawo hankalin zuba jari kai-tsaye na ƙasashen waje (FDI) a fannin Mai da iskar Gas na Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • Mazauna Bauchi Na Kokawa Kan Tsadar Farashin Acaba Duk Da Raguwar Farashin Mai
  • Cinikayyar Waje Ta Jihar Xinjiang Ta Kai Sabon Matsayin Ci Gaba A 2025

A cewarsa, Umarnin Zartarwa, wanda aka gabatar bayan aiwatar da Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA), an tsara su ne don inganta gasa a Najeriya a fannin zuba jarin makamashi a duniya, a tsakanin gasa mai tsauri daga wasu ƙasashen Afirka, Guyana da wasu sassan Gabas mai nisa.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

A cewarsa: “Gasar saka hannun jari ta duniya ce; kuma wasu ƙasashe suna canza manufofinsu ta hanyar da ta dace don jawo hankalin masu zuba jari. Ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da Shugaba Tinubu ya yi shi ne gabatar da Umarnin Zartarwa (Executive Order), wanda ya ƙara wa masu zuba jari ƙwarin-gwiwa”, in ji Ojulari.

 

Ya bayyana cewa, bayyana manufofi da sassaucin da Gwamnatin Tarayya ta nuna sun bai wa Shell damar kammala raba kadarorin haɗin-gwiwa na ƙasashen waje, waɗanda aka mayar wa Kamfanin Renaissance Africa Energy Company. “Kammala wannan ciniki ya nuna wa duniya jajircewar Shugaban Ƙasa na baiwa masu zuba jari damar saka hannun-jari ba kawai ba, har ma da fita idan ya zama dole – saboda duniyar saka hannun jari tana da ƙarfi sosai”, in ji shi.

 

Ojulari ya ce nasarar da aka samu wajen rage farashin ya ƙara wa ƙasashen duniya ƙwarin-gwiwa; kuma ya yi tasiri kai-tsaye kan shawarwarin saka hannun jari na Shell a Najeriya. Ya bayyana cewa Shell ta ɗauki Matakin Zuba Jari na Ƙarshe (FID) na dala biliyan 5 don haɓɓaka filin Mai na Bonga, sannan kuma ta sake zuba jari na dala biliyan 2 a wani aikin haɓɓaka iskar Gas mai zurfi wanda aka sani da HI. “A jimilla, Shell ta riga ta zuba jari sama da dala biliyan 7 tun bayan sanarwar wannan tallafin. Za ku iya fahimtar abin da wannan ke nufi idan aka kwaikwayi irin wannan ƙwarin-gwiwa ga sauran masu zuba jari”, in ji shi.

 

Shugaban NNPCL ya bayyana cewa Shell yanzu ta tabbatar wa Shugaba Tinubu shirye-shiryen neman sabbin damar saka hannun-jari da darajarsu ta kai dala biliyan 20 a cikin shekaru masu zuwa; wanda hakan zai kara ƙarfafa sha’awar Najeriya a matsayin wurin zuba jari a makamashi.

 

Ojulari ya kuma bayyana cewa ana cigaba da tattaunawa kan babban aikin Shell na gaba – aikin Bonga South-West – wanda aka ƙiyasta zai buƙaci kashe jari kusan dala biliyan 10, banda manyan kuɗaɗen gudanarwa.

 

Ya jaddada cewa bayan alƙaluman kuɗi, jarin zai sami fa’idodi masu yawa na zamantakewa da tattalin arziki ga ƴan Najeriya, gami da samar da ayyukan-yi, da kuma farfaɗo da ƙarfin masana’antu na gida.

 

“Waɗannan manyan alƙaluma suna fassara zuwa ƙarin ayyuka, yayin gini da aiwatar da ayyuka. Ƴan Najeriya za su sami damarmaki dayawa don shiga; kuma wuraren masana’antu waɗanda suka kasance ba tare da aiki ba na tsawon shekaru saboda rashin ayyuka za su dawo rayuwa”, in ji shi.

 

Ojulari ya yabawa shugabancin Shugaba Tinubu, yana mai bayyana shi a matsayin mai amfani da tasiri maimakon yin magana mai daɗi, musamman a fannin gaskiya da jajircewa ga shirin gwamnati na ‘Sabuntawa da Fata’.

 

Ya bayyana fatan cewa ɗorewar manufofi za ta cigaba da buɗe sabbin hanyoyin saka hannun-jari kai-tsaye ga masana’antar Mai da iskar Gas ta Nijeriya.

Shell
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba
Shell
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post

Gwamnatin Zamfara Ta Ɓullo Da Shirin Amfana Da Ma'adanai Ga Al'umma Jihar

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.