ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Shell Ya Yi Alƙawarin Zuba Jarin Dala Biliyan 20 A Najeriya Bayan Dala Biliyan 7 Da Aka Kashe – NNPCL GCEO

by Sani Anwar and Sulaiman
6 months ago
Shell

Shugaban Gudanarwa na Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), Mista Bashir Bayo Ojulari, ya bayyana cewa Kamfanin ‘Shell Petroleum Development Company’ ya kuduri aniyar neman ƙarin damar zuba jari na kimanin dala biliyan 20 a Nijeriya cikin shekaru biyu masu zuwa, bayan sabunta ƙwarin-gwiwar masu zuba jari da gyare-gyaren Gwamnati suka haifar kwanan nan.

 

Ojulari ya bayyana hakan ne yayin da yake yi wa manema labarai bayani a Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja, game da manufar wani ƙudiri da aka gabatar wa Shugaba Bola Tinubu, yana mai nuna tasirin Umarnin Zartarwa da aka bayar a shekarar 2025 don jawo hankalin zuba jari kai-tsaye na ƙasashen waje (FDI) a fannin Mai da iskar Gas na Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • Mazauna Bauchi Na Kokawa Kan Tsadar Farashin Acaba Duk Da Raguwar Farashin Mai
  • Cinikayyar Waje Ta Jihar Xinjiang Ta Kai Sabon Matsayin Ci Gaba A 2025

A cewarsa, Umarnin Zartarwa, wanda aka gabatar bayan aiwatar da Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA), an tsara su ne don inganta gasa a Najeriya a fannin zuba jarin makamashi a duniya, a tsakanin gasa mai tsauri daga wasu ƙasashen Afirka, Guyana da wasu sassan Gabas mai nisa.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

A cewarsa: “Gasar saka hannun jari ta duniya ce; kuma wasu ƙasashe suna canza manufofinsu ta hanyar da ta dace don jawo hankalin masu zuba jari. Ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da Shugaba Tinubu ya yi shi ne gabatar da Umarnin Zartarwa (Executive Order), wanda ya ƙara wa masu zuba jari ƙwarin-gwiwa”, in ji Ojulari.

 

Ya bayyana cewa, bayyana manufofi da sassaucin da Gwamnatin Tarayya ta nuna sun bai wa Shell damar kammala raba kadarorin haɗin-gwiwa na ƙasashen waje, waɗanda aka mayar wa Kamfanin Renaissance Africa Energy Company. “Kammala wannan ciniki ya nuna wa duniya jajircewar Shugaban Ƙasa na baiwa masu zuba jari damar saka hannun-jari ba kawai ba, har ma da fita idan ya zama dole – saboda duniyar saka hannun jari tana da ƙarfi sosai”, in ji shi.

 

Ojulari ya ce nasarar da aka samu wajen rage farashin ya ƙara wa ƙasashen duniya ƙwarin-gwiwa; kuma ya yi tasiri kai-tsaye kan shawarwarin saka hannun jari na Shell a Najeriya. Ya bayyana cewa Shell ta ɗauki Matakin Zuba Jari na Ƙarshe (FID) na dala biliyan 5 don haɓɓaka filin Mai na Bonga, sannan kuma ta sake zuba jari na dala biliyan 2 a wani aikin haɓɓaka iskar Gas mai zurfi wanda aka sani da HI. “A jimilla, Shell ta riga ta zuba jari sama da dala biliyan 7 tun bayan sanarwar wannan tallafin. Za ku iya fahimtar abin da wannan ke nufi idan aka kwaikwayi irin wannan ƙwarin-gwiwa ga sauran masu zuba jari”, in ji shi.

 

Shugaban NNPCL ya bayyana cewa Shell yanzu ta tabbatar wa Shugaba Tinubu shirye-shiryen neman sabbin damar saka hannun-jari da darajarsu ta kai dala biliyan 20 a cikin shekaru masu zuwa; wanda hakan zai kara ƙarfafa sha’awar Najeriya a matsayin wurin zuba jari a makamashi.

 

Ojulari ya kuma bayyana cewa ana cigaba da tattaunawa kan babban aikin Shell na gaba – aikin Bonga South-West – wanda aka ƙiyasta zai buƙaci kashe jari kusan dala biliyan 10, banda manyan kuɗaɗen gudanarwa.

 

Ya jaddada cewa bayan alƙaluman kuɗi, jarin zai sami fa’idodi masu yawa na zamantakewa da tattalin arziki ga ƴan Najeriya, gami da samar da ayyukan-yi, da kuma farfaɗo da ƙarfin masana’antu na gida.

 

“Waɗannan manyan alƙaluma suna fassara zuwa ƙarin ayyuka, yayin gini da aiwatar da ayyuka. Ƴan Najeriya za su sami damarmaki dayawa don shiga; kuma wuraren masana’antu waɗanda suka kasance ba tare da aiki ba na tsawon shekaru saboda rashin ayyuka za su dawo rayuwa”, in ji shi.

 

Ojulari ya yabawa shugabancin Shugaba Tinubu, yana mai bayyana shi a matsayin mai amfani da tasiri maimakon yin magana mai daɗi, musamman a fannin gaskiya da jajircewa ga shirin gwamnati na ‘Sabuntawa da Fata’.

 

Ya bayyana fatan cewa ɗorewar manufofi za ta cigaba da buɗe sabbin hanyoyin saka hannun-jari kai-tsaye ga masana’antar Mai da iskar Gas ta Nijeriya.

Shell
Sani Anwar
+ posts Bio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe
Shell
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
Next Post

Gwamnatin Zamfara Ta Ɓullo Da Shirin Amfana Da Ma'adanai Ga Al'umma Jihar

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.