Tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya buƙaci ‘yan Nijeriya mazauna gida da ƙasashen waje da su fara ɗaukar matakai gabanin zaɓen 2027, inda ya nemi su yi rajistar zaɓe tare da shiga jam’iyyar ADC.
Kwankwaso, wanda jigo ne a ADC kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, ya yi wannan kira ne a cikin wani saƙon bidiyo da ya wallafa a shafinsa na X a daren Litinin.
A cikin saƙon, ya jaddada muhimmancin shiga harkokin dimokuraɗiyya, musamman ga matasa, yana mai cewa yin rajista da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) na da matuƙar muhimmanci wajen tsara makomar siyasar ƙasar.
Ya buƙaci duk masu cancantar yin zaɓe da kada su jinkirta yin rajista, yana mai cewa yawan masu shiga zaɓe zai taka rawa wajen tantance shugabanni a 2027.
Kwankwaso ya kuma ƙarfafa guiwar jama’a da su shiga ADC, yana mai bayyana jam’iyyar a matsayin wata hanya mai ƙarfi da ‘yan adawa ke amfani da ita domin ƙalubalantar gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a zaɓe mai zuwa.
Kwankwaso Ya ce: “’Yan Nijeriya, lokaci ya yi da kowa mai cancanta, matasa da manya, mazauna birane da ƙauyuka, na cikin gida da na ƙetare, ya ɗauki matakai guda biyu masu muhimmanci. Ku yi rajistar zaɓe da INEC ba tare da ɓata lokaci ba. Sannan ku yi rajista da jam’iyyar ADC.”















Discussion about this post