ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mai Yiwuwa Farashin Shinkafar Da Ake Nomawa A Wasu Jihohin Arewa Ya Kara Tashi

by Abubakar Abba
3 years ago
Shinkafa

Masu amfani da Shinkafar da ake nomawa a kasar nan na ci gaba da jin tsoron kara tashin farashinta.

Masu sarrafa ta a kasar nan, sun danganta yuwuwar farashinta yadda ta yi tsada a kasuwannin da ke a cikin kasar.

  • Abin Da Ya Zama Wajibi Manoman Rogo Su Yi Don Samun Amfani Mai Yawa
  • Yadda Dawo Da Tsaffin Takardun Kudi Ya Kara Bunkasa Kasuwar Hatsi A Jihar Katsina

Farashin buhunta mai nauyin kilo 50 a garin Abuja a yanzu Wanda ya danganta da irin Shinkafar, ya kai daga Naira 38,000 zuwa Naira 43,000, inda wannan farashin ya kai tun 1960 a lokacin da Nijeriya ta samu ‘yancin kanta.

ADVERTISEMENT

Ana ci gaba da nuna damuwa cewar, mai farashin ya karu, saboda nomanta na rani da za a yi, ba zai iya cike gibin da aka samu a 2022 saboda aukuwar annobar ambaliyar Ruwa.

Bugu da kari, masu sarrafa ta a jihar Kano sun danganta karancinta kan ambaliyar Ruwa da aka sanu a daminar bara, inda hakan ya lalata gonakan Shinkafa a yankunan da ake nomanta.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Bincike a jihar ya nuna cewa, duk da sayar da ita da aka yi kan farashi mai tsada, an samu karancinta a kasuwannin da ake sayar da ita.

Hakazalika, bincike ya nuna cewa, buhunta mai cin kilo 100, ana sayar da ita kan Naira 25,000, sabanin yadda ake sayar da ita  daga Naira 18,000 zuwa Naira 19,000 a shekarar da ta wuce.

Wani dilanta a karamar hukumar Kura da ke a jihar Kano Malam Shehu Buba ya ce, akasarin kamfanoin da ke sarrafa ta a jihar sun tara ta da yawa.

Lamarin ma haka yake a jihar Benuwe, inda masu sarrafa ta suka bayyana tashin farashin Shinkara da ake nomawa a ckin jihar, duk da karancinta da ake fuskanta.

An ruwaito cewa, a kakar yin girbin shekarar da ta wuce, ana samun babban buhunta kan Naira 30,000, inda bayan wattani sun ci gaba farshinta ya kai Naira 35,000, daga baya kuma farshinta ya kara tashi zuwa Naira 37,000.

Bugu da kari a jihar Neja, gasar da ke akuwa a tsakanin amsu sarrafa Shinkafar a jihar, na kara janoyo karancin ta.

Misali, Buhunta mai nauyin kilo 100 a yanzu ana sayarwa kan Naira 22,000, sabanin yadda a shekarar data wuce, aka sayar da shi kan Naira 16,000

Wani mai sarrafa Shinkafar mai suna, Ibrahim Adamu ya sanar da cewa, a shekarun baya yana sayen Buhunhuna 10,000 Shinkafar wacce kuma yake sarrafa ta ya kai kasuwa don sayarwa.

“A shekarun baya yana sayen Buhunhuna 10,000 Shinkafar wacce kuma yake sarrafa ta ya kai kasuwa don sayarwa.”

“A shekarun baya yana sayen Buhunhuna 10,000 Shinkafar wacce kuma yake sarrafa ta ya kai kasuwa don sayarwa.”

Sai dai, Ibrahim ya bayyana cewa, a yanzu yana iya sayen Buhunhuna 2,300 ne kacal na Shinfar ta cikin gida, saboda yadda ta yi karanci matuka, inda ya kara da cewa, a bana farashinta ya yi tsada sosai.

A cewarsa, a shekarun baya farashin Buhunta mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi daga Naira 14,000 zuwa Naira 16,000, amma a yanzu farshinsa ya kai har Naira 22,000.

” A yanzu yana iya sayen Buhunhuna 2,300 ne kacal na Shinfar ta cikin gida, saboda yadda ta yi karanci matuka, inda ya kara da cewa, a bana farashinta ya yi tsada sosai.”

Ibrahim ya danganta tashin farashin nata kan annobar ambaliyar ruwan sama da aka samu a bara a wasu gonakan da ke a cikin jihar.

” A shekarun baya farashin Buhunta mai nauyin kilo 100, ana sayar da shi daga Naira 14,000 zuwa Naira 16,000, amma a yanzu farshinsa ya kai har Naira 22,000.”

Wani daga cikin masu sarrafa Shinkafar a jihar  mai suna Yazid Adamu ya sanar da cewa, kafin karancin kudi a kasar nan, masu sarrafa ta sun fuskanci kalubale wajen sayen ta agun manoma, musamman manoman da suka ke a kauye wadanda suka fi a basu kudi a hannu kafin a sayi Shinkafar ta su.

Ya ce, amma muna sa ran daga  watan Yuni zuwa  Juli, Shinkar za ta kasance a wadace.

Hakazalika a jihar Taraba, wani karamin dan kasuwa a kasuwar  sayar da hatsi ta Mutum biyu mai suna Awwal Mutumbiyu ya bayyana cewa,  ana sayar da Buhu daya daga kan Naira 20,000  zuwa  Naira 22,000.

Ya kara da cewa, Farashin magungunan feshi ya karu, inda a yanzu, ake sayar da Buhu daya na takin zamani kan Naira 25,000, inda hakan ya kara janyo tashin farashin na Shikafar.”

Shinkafa
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Har Yanzu Wasu Na Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Mutanen Banza —Auwal West

Har Yanzu Wasu Na Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Mutanen Banza —Auwal West

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.