ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mu Tsare Martabar Aure Don Kiyaye Makomarmu

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
aure

Fili na musamman domin matasa, wanda yake bawa kowa damar tofa albarkacin bakinsa game da abin da yake ci masa tuwo a kwarya na rayuwar yau da kullum. A yau filin namu na tafe da bayanin Abba Abubakar Yakubu inda ya bayyana nasa ra’ayin game da abin da ke damunsa cikin zuciya wanda ya shafi rayuwar Aure. Ga kuma bayanin nasa kamar haka:

 

A makonin da suka gabata akwai wani muhimmin batu da ya dauki hankalin jama’a a zaurukan sada zumunta dangane da batun wata matashiya ‘yar gwagwarmaya Malama Layla Ali Othman wacce a wata hira da ta yi da wani shiri na tashar BBC Hausa ta bayyana halin da mata zawarawa ke fuskanta, tare da labarin irin halin da ita ma ta samu kanta a ciki bayan rabuwar aurenta da wasu mazaje. Babu shakka jama’a da dama sun yi tsokaci iri-iri a kai, gwargwadon fahimtar da suka yi wa jawabin nata. Akasari martani masu zafi ya fi fitowa ne daga bangaren maza, yayin da a gefen mata da dama suka rika tausaya mata da nuna mata goyon baya. Mai yiwuwa ko don su sun fi fahimtar karatun nata ne, a matsayinsu na mata, tunda an ce ciwon ‘ya mace na ‘ya mace ne? Amma dai kam lallai Layla ta sha raddi sosai, kodayake a irin yadda na fahimce ta, ko a jikinta. Sai dai kuma lokaci ya yi bayan an gama mayar da martani da raddi cikin fushi ko cikin raha, har da ‘yan tamore, kar a ce su ma basu ce komai ba.

ADVERTISEMENT
  • Rarara Bai Kawo Kudin Aurena Ba – Aisha Humaira
  • Wasu Muhimman Abubuwa Da Ba A Sani Ba Game Da Kwakwalwa

Ya kamata kuma mu dawo mu yi karatun ta natsu, mu kalli al’amarin da idanun basira. Lallai ne duk dan halak ya so aure, saboda shi ne tushen mu, shi ne gatan mu, kuma shi ya martaba mu, ya mayar da mu masu kima da mutunci a idon duniya. Don haka ne muka ji zafi da muka ji irin maganganun da ke fitowa na sukar aure, ba don mun damu mu tsoma baki a rayuwar Layla ba, sai don aure yana cikin ginshikin rayuwar mu. Dole ne mu fito mu kare mutuncinsa. Sai dai kuma duk da haka, Hausawa na cewa, bayan tiya akwai wata caca! Bayan mun yi bambamin mun gama, ya kamata mu juyo mu kalli irin riwon da muke yi wa auren, musamman a nan Arewa, ko a tsakanin Musulmi. Mu tambayi kan mu, shin muna bai wa auren muhimmancin da ya kamata? Muna kula da hakkokin auren da ke kan mu? Yaya muke rike amanar matan da muke aura, bayan mun raba su da iyayensu da danginsu? Shin muna kula da nauyin iyalinmu yadda malamai suka ce gwargwadon hali.

 

LABARAI MASU NASABA

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

Amsoshin wadannan tambayoyi su ne za su kai mu ga fahimtar abin da Layla ta tono, wato a turance ake cewa, ‘A CAN OF WORMS!’ Ban kawar da batun yahudanci ko wayewar zamani na sa wasu matan Arewa tunanin rayuwarsu za ta fi kyau idan sun yar da kwallon mangwaro sun huta da kuda ba. Amma zance na gaskiya duk macen da ka ji ta fito bainar jama’a tana gayawa duniya ta hakura da aure a rayuwarta to, ka bincika da kyau ka gani, ba a banza ba ne. Ba lallai uzurin Layla na rabuwa da mazajenta biyu na aure ya samu karbuwa a wajena ko kai ba, amma lallai mu duba a kusa da mu ba da nisa ba. Ba mu da kannai ko yayu mata, kai ko ma ‘ya’ya, (tunda mu ma yanzu mun fara aurar da na ‘yan uwa) ko wata mace a ‘yan uwanmu ko a makwafta, wadanda aure ya birkita rayuwarsu, suka fita hayyacinsu, wasu ma ciwon zuciya da hawan jini ya yi sanadin barin su duniya?

 

A dalilin halayen wasu mazan ne da ba su iya rikon aure ba, ko ba su kula da rikon amanar aure ba, haka take faruwa. Wani lokaci muna sane za mu rufe ido mu tilasta su komawa dakin mazajensu, ba don ba mu fahimci halin da suke ciki ba, sai don ba ma son su kashe auren su dawo gida zaman zawarci, ko ba ma son rayuwarsu ta kara shiga wani hali saboda rashin auren.

 

Sai dai wani lokaci mu rarrashe su, ko mu tallafa musu da wani abu da za su rage zafi ko su kama sana’a a dakunansu na aure. Kamar yadda muka tashi muka ji iyayenmu na fada ne, kuma masana zamantakewa suka tabbatar da haka. Aure dan hakuri, kuma zo mu zauna ne zo mu saba. Ko da ma’auratan da za ka ji ana cewa sun shafe tsawon shekaru suna zaune ba tare da sun rabu ko sun kashe auren su ba, idan ka yi bincike a tsanake za ka ji irin yadda suke kokarin fahimtar junansu da warware sabanin da suke samu a sirrance ba tare da barin wani ya sani ba.

Aure
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya
Aure
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Aure
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 27, 2026
Wasu Abubuwa Da Ke Sa Maza Hana Mata Fita Unguwa (Uwargida)
Uwargida Sarautar Mata

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

June 21, 2026
Next Post
Tinubu Zai Tafi Brazil Kwana Biyar Bayan Dawo Wa Daga Saudiya

Tinubu Zai Tafi Brazil Kwana Biyar Bayan Dawo Wa Daga Saudiya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.