Rahotanni daga Gatawa, wani ƙauye da ke ƙaramar hukumar Sabon Birni a Jihar Sokoto, sun tabbatar da cewa wani mummunan hari da ƴan bindiga suka kai a safiyar ranar ya yi sanadiyyar mutuwar mutune biyar.
Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na dare, lokacin da maharan suka mamaye ƙauyen tare da yin harbe-harbe ba kakkautawa. Wasu masu gadin ƙauyen sun yi yunƙurin daƙile su, amma harin ya yi muni inda mutum huɗu daga cikinsu suka rasu nan take.
- Harin Ƴan Bindiga Ya Halaka Mutum 11 A Pretoria
- Mutum 4 Sun Mutu Yayin Da ’Yan Bindiga Sake Kai Hari Kogi
Baya ga waɗanda suka mutu a wurin, an ce wasu biyu sun samu raunuka sakamakon harbin bindiga, inda aka garzaya da su asibiti domin kulawa. Daga cikin waɗanda aka jikkata, ɗaya daga cikinsu ya rasu daga bisani, lamarin da ya ƙara adadin waɗanda suka mutu zuwa biyar. Mazauna yankin sun bayyana cewa harin ya jefa al’umma cikin firgici, tare da barin iyalai da dama cikin ƙunci sakamakon asarar dangi da makota.
A cewar wani da ya nemi a sakaya sunansa, maharan sun kuma sace mutane shida, ciki har da matan aure biyu, ƴan mata biyu da kuma samari biyu. Ya ce bayan kammala harin, ƴan bindigar sun yi awon gaba da dabbobi kafin su tsere daga yankin ba tare da jami’an tsaro sun iso ba. Ya ce an ji ƙarar musayar wuta daga nesa tsakanin jami’an tsaro da maharan, amma babu wanda aka kuɓutar daga cikin waɗanda aka sace.
Al’ummar ƙauyen sun nuna damuwa kan yadda hare-haren ƴan bindiga ke ci gaba da ta’azzara a yankin, suna kuma kira ga hukumomi da su ƙara kula. Har zuwa lokacin wallafa wannan rahoto, ba a samu ƙarin bayani kan martanin hukumomi ba, sai dai mazauna ƙauyen na cigaba da neman taimako wajen ceto waɗanda aka yi awon gaba da su.














