Wasu magoya bayan jam’iyyar APC a jihar Bauchi sun ce ba za su taɓa lamuncewa da dukkanin wani yunƙuri na ƙaƙaba ɗan takara gabanin gwamna na jam’iyyar ba, inda suka ƙafe kai da fata kan cewa dole ne a gudanar da sahihin zaɓe fidda gwanin gwamnan cikin gaskiya da adalci.
Da ya ke magana a ranar Alhamis yayin da suka ziyarci otal ɗin da ake tunanin mambobin kwamitin zaɓen jam’iyyar suka sauƙa domin neman ƙarin haske kan yadda za a gudanar da zaɓen fidda gwanin zai gudana, wani jigo a APC, Musa Buba Mohammed wanda aka fi sani da “Civilian General,” ya ce mambobin jam’iyyar ba za su amince da duk wani yunƙuri daga wasu tsirarun mutane na musu ɗauki-ɗoran ɗan takara maimakon bai wa dimokuraɗiyya damar tafiya yadda ya kamata ba.
Ya jaddada cewa dimokuraɗiyya dole ne ta wakilci muradin mafi rinjayen mambobin jam’iyya, ba wai buƙatun wasu tsirarun mutane kaɗai ba.
A cewarsa, babban abin da magoya bayan APC a Bauchi ke nema shi ne gudanar da sahihin zaɓen fidda gwani cikin gaskiya da adalci wanda zai samar da ɗan takarar da mambobin jam’iyyar da al’ummar jihar za su amince da shi har a samu nasara a 2027.
Musa ya bayyana cewa duk da cewa an ɗage zaɓen fidda gwanin daga ranar Alhamis zuwa Juma’a, har yanzu mambobin jam’iyyar na da kyakkyawan fata cewa za a gudanar da zaɓen cikin gaskiya, adalci da sahihanci, inda ya yi gargaɗi kan yin wani abu saɓanin hakan. Ya ce abin da magoya bayan jam’iyyar ke nema kawai shi ne adalci da gaskiya, yana mai bayyana kwarin gwiwar cewa ɗan takara Nura Manu Soro zai yi nasarar zama ɗan takarar jam’iyyar APC muddin aka gudanar da sahihi kuma zaɓe cikin gaskiya da adalci.Haka kuma ya yi kira ga shugabannin APC da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da su tabbatar an yi wa mambobin jam’iyyar a Bauchi adalci da gaskiya.
A cewarsa, an sanar da magoya bayan jam’iyyar cewa an ɗage zaɓen fidda gwani a jihohin Bauchi da Kwara, lamarin da ya haifar da fargaba kan ingancin zaben da za a gudanar ɗin.”Abin da muke so shi ne sahihin zaɓe cikin lumana, gaskiya da adalci. Ba ma son kakabawa. Wannan shi ne kawai buƙatarmu,” in ji shi.
Jigon APC ɗin ya kuma yi tambaya kan dalilin ɗage zaɓen fidda gwani a Bauchi, yana mai cewa hakan ya ƙara haifar da damuwa a tsakanin magoya bayan jam’iyyar.
“Me ya sa aka ɗage zaɓen? Dole akwai wani dalili a bayan hakan. Sauran jihohi sun gudanar da nasu zaɓukan, amma Bauchi da Kwara aka ɗage. Shi ya sa mutane da dama ke fara zargin akwai wata manufa a ciki,” in ji shi.
Ya buƙaci shugabannin jam’iyyar da su mutunta ƙa’idojin dimokuraɗiyya, yana mai tuna cewa Shugaba Tinubu ya samu nasara ne ta hanyar sahihin zaɓe ba ta hanyar yarjejeniya ko kakabawa ba.
“Shugaban ƙasa ya yi nasara ne ta hanyar ƙuri’a, ba ta hanyar yarjejeniya ba. Wannan irin tsarin dimokuraɗiyyar ne muke nema a nan Bauchi,” in ji shi.
Shi ma da yake magana, Kwamared Abdul’Aziz Nasrullah ya ce Jihar Bauchi na buƙatar sahihan ‘yan takara waɗanda za su wakilci muradun al’umma da gaske da adalci, ba waɗanda ake zargin wasu masu ƙarfin fada a ji suna ƙoƙarin kakaba su domin biyan buƙatun kansu ba.
Ya sake jaddada ƙudirin magoya bayan APC na tabbatar da adalci, gaskiya da sahihanci a tsarin zaɓen fidda gwani na gwamna a Jihar Bauchi.















Discussion about this post