ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 weeks ago
Bauchi

Wasu magoya bayan jam’iyyar APC a jihar Bauchi sun ce ba za su taɓa lamuncewa da dukkanin wani yunƙuri na ƙaƙaba ɗan takara gabanin gwamna na jam’iyyar ba, inda suka ƙafe kai da fata kan cewa dole ne a gudanar da sahihin zaɓe fidda gwanin gwamnan cikin gaskiya da adalci.

Da ya ke magana a ranar Alhamis yayin da suka ziyarci otal ɗin da ake tunanin mambobin kwamitin zaɓen jam’iyyar suka sauƙa domin neman ƙarin haske kan yadda za a gudanar da zaɓen fidda gwanin zai gudana, wani jigo a APC, Musa Buba Mohammed wanda aka fi sani da “Civilian General,” ya ce mambobin jam’iyyar ba za su amince da duk wani yunƙuri daga wasu tsirarun mutane na musu ɗauki-ɗoran ɗan takara maimakon bai wa dimokuraɗiyya damar tafiya yadda ya kamata ba.

Ya jaddada cewa dimokuraɗiyya dole ne ta wakilci muradin mafi rinjayen mambobin jam’iyya, ba wai buƙatun wasu tsirarun mutane kaɗai ba.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, babban abin da magoya bayan APC a Bauchi ke nema shi ne gudanar da sahihin zaɓen fidda gwani cikin gaskiya da adalci wanda zai samar da ɗan takarar da mambobin jam’iyyar da al’ummar jihar za su amince da shi har a samu nasara a 2027.

Musa ya bayyana cewa duk da cewa an ɗage zaɓen fidda gwanin daga ranar Alhamis zuwa Juma’a, har yanzu mambobin jam’iyyar na da kyakkyawan fata cewa za a gudanar da zaɓen cikin gaskiya, adalci da sahihanci, inda ya yi gargaɗi kan yin wani abu saɓanin hakan. Ya ce abin da magoya bayan jam’iyyar ke nema kawai shi ne adalci da gaskiya, yana mai bayyana kwarin gwiwar cewa ɗan takara Nura Manu Soro zai yi nasarar zama ɗan takarar jam’iyyar APC muddin aka gudanar da sahihi kuma zaɓe cikin gaskiya da adalci.Haka kuma ya yi kira ga shugabannin APC da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da su tabbatar an yi wa mambobin jam’iyyar a Bauchi adalci da gaskiya.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

A cewarsa, an sanar da magoya bayan jam’iyyar cewa an ɗage zaɓen fidda gwani a jihohin Bauchi da Kwara, lamarin da ya haifar da fargaba kan ingancin zaben da za a gudanar ɗin.”Abin da muke so shi ne sahihin zaɓe cikin lumana, gaskiya da adalci. Ba ma son kakabawa. Wannan shi ne kawai buƙatarmu,” in ji shi.

Jigon APC ɗin ya kuma yi tambaya kan dalilin ɗage zaɓen fidda gwani a Bauchi, yana mai cewa hakan ya ƙara haifar da damuwa a tsakanin magoya bayan jam’iyyar.

“Me ya sa aka ɗage zaɓen? Dole akwai wani dalili a bayan hakan. Sauran jihohi sun gudanar da nasu zaɓukan, amma Bauchi da Kwara aka ɗage. Shi ya sa mutane da dama ke fara zargin akwai wata manufa a ciki,” in ji shi.

Ya buƙaci shugabannin jam’iyyar da su mutunta ƙa’idojin dimokuraɗiyya, yana mai tuna cewa Shugaba Tinubu ya samu nasara ne ta hanyar sahihin zaɓe ba ta hanyar yarjejeniya ko kakabawa ba.

“Shugaban ƙasa ya yi nasara ne ta hanyar ƙuri’a, ba ta hanyar yarjejeniya ba. Wannan irin tsarin dimokuraɗiyyar ne muke nema a nan Bauchi,” in ji shi.

Shi ma da yake magana, Kwamared Abdul’Aziz Nasrullah ya ce Jihar Bauchi na buƙatar sahihan ‘yan takara waɗanda za su wakilci muradun al’umma da gaske da adalci, ba waɗanda ake zargin wasu masu ƙarfin fada a ji suna ƙoƙarin kakaba su domin biyan buƙatun kansu ba.

Ya sake jaddada ƙudirin magoya bayan APC na tabbatar da adalci, gaskiya da sahihanci a tsarin zaɓen fidda gwani na gwamna a Jihar Bauchi.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Sayi Fom Ɗin Takarar Sanatan Bauchi ta Kudu A Jam’iyyar APM
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Sin Za Ta Gudanar Da Babban Taron Kwamitin Sulhun MDD A Ranar 26 Ga Watan Mayu

Sin Za Ta Gudanar Da Babban Taron Kwamitin Sulhun MDD A Ranar 26 Ga Watan Mayu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.