ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 month ago
Bauchi

Wasu magoya bayan jam’iyyar APC a jihar Bauchi sun ce ba za su taɓa lamuncewa da dukkanin wani yunƙuri na ƙaƙaba ɗan takara gabanin gwamna na jam’iyyar ba, inda suka ƙafe kai da fata kan cewa dole ne a gudanar da sahihin zaɓe fidda gwanin gwamnan cikin gaskiya da adalci.

Da ya ke magana a ranar Alhamis yayin da suka ziyarci otal ɗin da ake tunanin mambobin kwamitin zaɓen jam’iyyar suka sauƙa domin neman ƙarin haske kan yadda za a gudanar da zaɓen fidda gwanin zai gudana, wani jigo a APC, Musa Buba Mohammed wanda aka fi sani da “Civilian General,” ya ce mambobin jam’iyyar ba za su amince da duk wani yunƙuri daga wasu tsirarun mutane na musu ɗauki-ɗoran ɗan takara maimakon bai wa dimokuraɗiyya damar tafiya yadda ya kamata ba.

Ya jaddada cewa dimokuraɗiyya dole ne ta wakilci muradin mafi rinjayen mambobin jam’iyya, ba wai buƙatun wasu tsirarun mutane kaɗai ba.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, babban abin da magoya bayan APC a Bauchi ke nema shi ne gudanar da sahihin zaɓen fidda gwani cikin gaskiya da adalci wanda zai samar da ɗan takarar da mambobin jam’iyyar da al’ummar jihar za su amince da shi har a samu nasara a 2027.

Musa ya bayyana cewa duk da cewa an ɗage zaɓen fidda gwanin daga ranar Alhamis zuwa Juma’a, har yanzu mambobin jam’iyyar na da kyakkyawan fata cewa za a gudanar da zaɓen cikin gaskiya, adalci da sahihanci, inda ya yi gargaɗi kan yin wani abu saɓanin hakan. Ya ce abin da magoya bayan jam’iyyar ke nema kawai shi ne adalci da gaskiya, yana mai bayyana kwarin gwiwar cewa ɗan takara Nura Manu Soro zai yi nasarar zama ɗan takarar jam’iyyar APC muddin aka gudanar da sahihi kuma zaɓe cikin gaskiya da adalci.Haka kuma ya yi kira ga shugabannin APC da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da su tabbatar an yi wa mambobin jam’iyyar a Bauchi adalci da gaskiya.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

A cewarsa, an sanar da magoya bayan jam’iyyar cewa an ɗage zaɓen fidda gwani a jihohin Bauchi da Kwara, lamarin da ya haifar da fargaba kan ingancin zaben da za a gudanar ɗin.”Abin da muke so shi ne sahihin zaɓe cikin lumana, gaskiya da adalci. Ba ma son kakabawa. Wannan shi ne kawai buƙatarmu,” in ji shi.

Jigon APC ɗin ya kuma yi tambaya kan dalilin ɗage zaɓen fidda gwani a Bauchi, yana mai cewa hakan ya ƙara haifar da damuwa a tsakanin magoya bayan jam’iyyar.

“Me ya sa aka ɗage zaɓen? Dole akwai wani dalili a bayan hakan. Sauran jihohi sun gudanar da nasu zaɓukan, amma Bauchi da Kwara aka ɗage. Shi ya sa mutane da dama ke fara zargin akwai wata manufa a ciki,” in ji shi.

Ya buƙaci shugabannin jam’iyyar da su mutunta ƙa’idojin dimokuraɗiyya, yana mai tuna cewa Shugaba Tinubu ya samu nasara ne ta hanyar sahihin zaɓe ba ta hanyar yarjejeniya ko kakabawa ba.

“Shugaban ƙasa ya yi nasara ne ta hanyar ƙuri’a, ba ta hanyar yarjejeniya ba. Wannan irin tsarin dimokuraɗiyyar ne muke nema a nan Bauchi,” in ji shi.

Shi ma da yake magana, Kwamared Abdul’Aziz Nasrullah ya ce Jihar Bauchi na buƙatar sahihan ‘yan takara waɗanda za su wakilci muradun al’umma da gaske da adalci, ba waɗanda ake zargin wasu masu ƙarfin fada a ji suna ƙoƙarin kakaba su domin biyan buƙatun kansu ba.

Ya sake jaddada ƙudirin magoya bayan APC na tabbatar da adalci, gaskiya da sahihanci a tsarin zaɓen fidda gwani na gwamna a Jihar Bauchi.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Sin Za Ta Gudanar Da Babban Taron Kwamitin Sulhun MDD A Ranar 26 Ga Watan Mayu

Sin Za Ta Gudanar Da Babban Taron Kwamitin Sulhun MDD A Ranar 26 Ga Watan Mayu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.