ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 months ago
Bauchi

Wasu magoya bayan jam’iyyar APC a jihar Bauchi sun ce ba za su taɓa lamuncewa da dukkanin wani yunƙuri na ƙaƙaba ɗan takara gabanin gwamna na jam’iyyar ba, inda suka ƙafe kai da fata kan cewa dole ne a gudanar da sahihin zaɓe fidda gwanin gwamnan cikin gaskiya da adalci.

Da ya ke magana a ranar Alhamis yayin da suka ziyarci otal ɗin da ake tunanin mambobin kwamitin zaɓen jam’iyyar suka sauƙa domin neman ƙarin haske kan yadda za a gudanar da zaɓen fidda gwanin zai gudana, wani jigo a APC, Musa Buba Mohammed wanda aka fi sani da “Civilian General,” ya ce mambobin jam’iyyar ba za su amince da duk wani yunƙuri daga wasu tsirarun mutane na musu ɗauki-ɗoran ɗan takara maimakon bai wa dimokuraɗiyya damar tafiya yadda ya kamata ba.

Ya jaddada cewa dimokuraɗiyya dole ne ta wakilci muradin mafi rinjayen mambobin jam’iyya, ba wai buƙatun wasu tsirarun mutane kaɗai ba.

ADVERTISEMENT

A cewarsa, babban abin da magoya bayan APC a Bauchi ke nema shi ne gudanar da sahihin zaɓen fidda gwani cikin gaskiya da adalci wanda zai samar da ɗan takarar da mambobin jam’iyyar da al’ummar jihar za su amince da shi har a samu nasara a 2027.

Musa ya bayyana cewa duk da cewa an ɗage zaɓen fidda gwanin daga ranar Alhamis zuwa Juma’a, har yanzu mambobin jam’iyyar na da kyakkyawan fata cewa za a gudanar da zaɓen cikin gaskiya, adalci da sahihanci, inda ya yi gargaɗi kan yin wani abu saɓanin hakan. Ya ce abin da magoya bayan jam’iyyar ke nema kawai shi ne adalci da gaskiya, yana mai bayyana kwarin gwiwar cewa ɗan takara Nura Manu Soro zai yi nasarar zama ɗan takarar jam’iyyar APC muddin aka gudanar da sahihi kuma zaɓe cikin gaskiya da adalci.Haka kuma ya yi kira ga shugabannin APC da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da su tabbatar an yi wa mambobin jam’iyyar a Bauchi adalci da gaskiya.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

A cewarsa, an sanar da magoya bayan jam’iyyar cewa an ɗage zaɓen fidda gwani a jihohin Bauchi da Kwara, lamarin da ya haifar da fargaba kan ingancin zaben da za a gudanar ɗin.”Abin da muke so shi ne sahihin zaɓe cikin lumana, gaskiya da adalci. Ba ma son kakabawa. Wannan shi ne kawai buƙatarmu,” in ji shi.

Jigon APC ɗin ya kuma yi tambaya kan dalilin ɗage zaɓen fidda gwani a Bauchi, yana mai cewa hakan ya ƙara haifar da damuwa a tsakanin magoya bayan jam’iyyar.

“Me ya sa aka ɗage zaɓen? Dole akwai wani dalili a bayan hakan. Sauran jihohi sun gudanar da nasu zaɓukan, amma Bauchi da Kwara aka ɗage. Shi ya sa mutane da dama ke fara zargin akwai wata manufa a ciki,” in ji shi.

Ya buƙaci shugabannin jam’iyyar da su mutunta ƙa’idojin dimokuraɗiyya, yana mai tuna cewa Shugaba Tinubu ya samu nasara ne ta hanyar sahihin zaɓe ba ta hanyar yarjejeniya ko kakabawa ba.

“Shugaban ƙasa ya yi nasara ne ta hanyar ƙuri’a, ba ta hanyar yarjejeniya ba. Wannan irin tsarin dimokuraɗiyyar ne muke nema a nan Bauchi,” in ji shi.

Shi ma da yake magana, Kwamared Abdul’Aziz Nasrullah ya ce Jihar Bauchi na buƙatar sahihan ‘yan takara waɗanda za su wakilci muradun al’umma da gaske da adalci, ba waɗanda ake zargin wasu masu ƙarfin fada a ji suna ƙoƙarin kakaba su domin biyan buƙatun kansu ba.

Ya sake jaddada ƙudirin magoya bayan APC na tabbatar da adalci, gaskiya da sahihanci a tsarin zaɓen fidda gwani na gwamna a Jihar Bauchi.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
Bauchi
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani
  • Sulaiman
    Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

MASU ALAKA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Next Post
Sin Za Ta Gudanar Da Babban Taron Kwamitin Sulhun MDD A Ranar 26 Ga Watan Mayu

Sin Za Ta Gudanar Da Babban Taron Kwamitin Sulhun MDD A Ranar 26 Ga Watan Mayu

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.