Hukumar Kwallon Ƙafa ta Nijeriya (NFF) ta umarci babban kocin Super Falcons, Justin Madugu, da sauran mambobin tawagar horaswar ƙungiyar da su sauka daga muƙamansu nan take, bayan rashin nasarar ƙungiyar a gasar Kofin Afrika ta Mata ta 2026 (WAFCON) da aka gudanar a Morocco.
NFF ta sanar da matakin ne a ranar Litinin ta shafinta na X, inda ta ce kwamitin zartarwar hukumar ya umarci dukkan mambobin tawagar horaswar Super Falcons da su bar muƙamansu nan take. Matakin ya zo ne bayan Nijeriya ta kasa samun tikitin zuwa gasar Kofin Duniya ta Mata ta 2027 da za a gudanar a Brazil.
Super Falcons ta fara gasar da rashin nasara mai ban mamaki a hannun Malawi, wadda ta fara halartar gasar a karon farko, duk da cewa daga baya Malawi ta kai wasan ƙarshe, inda Cameroon ta doke ta ta lashe kofin. Nijeriya ta samu damar kaiwa matakin kwata-fainal, amma Cameroon ta fitar da ita daga gasar.
Bayan ficewarta, Nijeriya ta samu wata damar neman tikitin Kofin Duniya ta hanyar buga wasan neman gurbi da Afirka ta Kudu, amma Super Falcons ta sake samun rashin nasara, lamarin da ya ƙara jefa damar Nijeriya ta zuwa Brazil 2027 cikin mawuyacin hali. Madugu ya kasance cikin tawagar horaswar Super Falcons tun bayan da NFF ta naɗa shi tare da Edwin Okon a watan Nuwamba 2021.
Sauke Madugu da tawagar horaswar ya zo ne a daidai lokacin da NFF ke fuskantar matsin lamba kan koma bayan ƙwallon ƙafa a ƙasar. Tawagar maza, da Super Eagles, ma ta kasa samun tikitin kai tsaye zuwa Kofin Duniya na 2026 bayan ta sha kashi a hannun Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo a wasan neman gurbi na Afrika, lamarin da ya sa ake ƙara kira ga NFF ta sake duba tsarin horaswa da gudanar da tawagogin ƙasa.














