ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NiDCOM Ta Nemi A Saki ‘Yan Nijeriya 42 Da Ake Tsare Da Su A Mozambikue

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
NiDCOM

Shugabar kuma Babbar Daraktar Kungiyar ‘yan Nijeriya Mazauna Kasar Waje, (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa, ta yi Allah-wadai da rahoton kama ‘yan Nijeriya 42 a kasar Mozambikue ba tare da gabatar musu da wata tuhuma a hukumance ba, tana mai bayyana lamarin a matsayin abin damuwa da kuma abin da ba za a amince da shi ba.

Dabiri-Erewa ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da aka fitar a Abuja ta hannun Daraktan Yada Labarai, Hulda da Jama’a da Kuma Tsare-tsare na Hukumar, Abdur-Rahman Balogun.

  • Yawan Dazuzzuka Da Filin Ciyayi a Kasar Sin Ya Wuce Kashi 56%
  • Sin Ta Himmatu Wajen Raya Ci Gaban Duniya Na Bai Daya

Ta nuna damuwa cewa an zargi jami’an tsaro da ware ‘yan Nijeriya ne kadai domin kamawa a cikin wasu ‘yan kasuwa da ke kasuwancin kayan gyaran motoci (spare parts).

ADVERTISEMENT

A cewarta, abin takaici ne yadda aka ce an ware ‘yan Nijeriya kadai aka kama tare da tsare su ba tare da wani bayani daga hukumomi ba.

Shugabar kungiyar, Abike Dabiri-Erewa, ta ce idan har wasu daga cikin wadanda aka kama sun karya dokokin Mozambikue, to ya kamata a tuhume su a hukumance sannan a gurfanar da su a gaban kotu mai iko.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Ta kara da cewa kamun da aka yi musu ba zato ba tsammani tare da ware su musamman yana tayar da damuwa kan yiwuwar nuna kiyayya ga baki (denophobia) ga ‘yan Nijeriya da ke zaune a kasar.

Saboda haka, ta bukaci hukumomin Mozambikue da su saki wadanda aka tsare nan take, ko kuma su tabbatar an bi dukkan matakan doka yadda ya kamata.

Rahotanni sun nuna cewa an ware ‘yan Nijeriyar ne aka kama a kasuwar kayan gyaran motoci (spare parts) duk da cewa akwai ‘yan kasuwa daga wasu kasashe daban-daban a wurin.

An kuma ce mutanen da aka kama suna zaune a Mozambikue bisa ka’ida, yayin da aka ruwaito cewa Babban Lauyan kasar bai ma san da wata tuhuma da aka shigar a kansu ba.

Har ila yau, an yi zargin cewa an ci zarafin wasu daga cikin wadanda aka kama yayin aikin, tare da kwace musu kayayyakinsu na kashin kai. An kuma ce wasu daga cikinsu sun kamu da rashin lafiya kuma suna bukatar kulawar likita cikin gaggawa.

Dabiri-Erewa ta bukaci hukumomin Mozambikue da su mutunta hakkoki da martabar ‘yan Nijeriya da ke kasar, tare da tabbatar da cewa adalci da gaskiya sun yi rinjaye.

NiDCOM
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Nasarar Harba Rukunin Taurarin Dan’adam Guda Biyu 

Sin Ta Yi Nasarar Harba Rukunin Taurarin Dan’adam Guda Biyu 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.