ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NiDCOM Ta Nemi A Saki ‘Yan Nijeriya 42 Da Ake Tsare Da Su A Mozambikue

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago
NiDCOM

Shugabar kuma Babbar Daraktar Kungiyar ‘yan Nijeriya Mazauna Kasar Waje, (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa, ta yi Allah-wadai da rahoton kama ‘yan Nijeriya 42 a kasar Mozambikue ba tare da gabatar musu da wata tuhuma a hukumance ba, tana mai bayyana lamarin a matsayin abin damuwa da kuma abin da ba za a amince da shi ba.

Dabiri-Erewa ta bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da aka fitar a Abuja ta hannun Daraktan Yada Labarai, Hulda da Jama’a da Kuma Tsare-tsare na Hukumar, Abdur-Rahman Balogun.

  • Yawan Dazuzzuka Da Filin Ciyayi a Kasar Sin Ya Wuce Kashi 56%
  • Sin Ta Himmatu Wajen Raya Ci Gaban Duniya Na Bai Daya

Ta nuna damuwa cewa an zargi jami’an tsaro da ware ‘yan Nijeriya ne kadai domin kamawa a cikin wasu ‘yan kasuwa da ke kasuwancin kayan gyaran motoci (spare parts).

ADVERTISEMENT

A cewarta, abin takaici ne yadda aka ce an ware ‘yan Nijeriya kadai aka kama tare da tsare su ba tare da wani bayani daga hukumomi ba.

Shugabar kungiyar, Abike Dabiri-Erewa, ta ce idan har wasu daga cikin wadanda aka kama sun karya dokokin Mozambikue, to ya kamata a tuhume su a hukumance sannan a gurfanar da su a gaban kotu mai iko.

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Ta kara da cewa kamun da aka yi musu ba zato ba tsammani tare da ware su musamman yana tayar da damuwa kan yiwuwar nuna kiyayya ga baki (denophobia) ga ‘yan Nijeriya da ke zaune a kasar.

Saboda haka, ta bukaci hukumomin Mozambikue da su saki wadanda aka tsare nan take, ko kuma su tabbatar an bi dukkan matakan doka yadda ya kamata.

Rahotanni sun nuna cewa an ware ‘yan Nijeriyar ne aka kama a kasuwar kayan gyaran motoci (spare parts) duk da cewa akwai ‘yan kasuwa daga wasu kasashe daban-daban a wurin.

An kuma ce mutanen da aka kama suna zaune a Mozambikue bisa ka’ida, yayin da aka ruwaito cewa Babban Lauyan kasar bai ma san da wata tuhuma da aka shigar a kansu ba.

Har ila yau, an yi zargin cewa an ci zarafin wasu daga cikin wadanda aka kama yayin aikin, tare da kwace musu kayayyakinsu na kashin kai. An kuma ce wasu daga cikinsu sun kamu da rashin lafiya kuma suna bukatar kulawar likita cikin gaggawa.

Dabiri-Erewa ta bukaci hukumomin Mozambikue da su mutunta hakkoki da martabar ‘yan Nijeriya da ke kasar, tare da tabbatar da cewa adalci da gaskiya sun yi rinjaye.

NiDCOM
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Nasarar Harba Rukunin Taurarin Dan’adam Guda Biyu 

Sin Ta Yi Nasarar Harba Rukunin Taurarin Dan’adam Guda Biyu 

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.