ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Faransa Sun Ƙarfafa Haɗin Gwuiwar Tsaro

by Abubakar Sulaiman
6 months ago
Nijeriya

Rundunar Sojin Nijeriya da ta Faransa sun ƙara ƙarfafa haɗin gwuiwar tsaro domin yaƙi da ta’addanci da sauran barazanar tsaro. An cimma wannan matsaya ne yayin ganawar Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Nijeriya, Laftanar Janar Waidi Shaibu, da wakilin Tsaron Faransa a Nijeriya, Kanal Stéphane Useo, a shalƙwatar rundunar soji da ke Abuja.

Laftanar Janar Shaibu ya yaba wa Faransa kan ci gaba da tallafa wa Rundunar Sojin Nijeriya, musamman a fannonin musayar bayanan sirri, horaswar ƙwararrun sojoji da kuma ƙarfafa shirin aiki. Ya ce irin wannan haɗin gwiwa na da matuƙar muhimmanci wajen tunkarar ƙalubalen tsaro da ke addabar ƙasar da yankin gaba ɗaya.

  • Shugaban Kasar Sin Ya Tattauna Da Takwaransa Na Faransa
  • Tsaro: Sojoji Sun Gano Masana’antar Ƙera Makamai A Nasarawa

Babban Hafsan ya jaddada aniyar rundunar na ci gaba da inganta ƙwarewar jami’anta a kowane sashi, tare da buƙatar ɗorewar haɗin gwuiwar tsaro tsakanin ƙasashen biyu bisa moriyar juna. Ya bayyana fata ln cewa haɗin gwuiwar ya zama na dogon lokaci da Faransa, musamman a fannin gina ƙarfi da horaswa ta zamani, zai ƙara inganta ingancin ayyukan rundunar.

ADVERTISEMENT

A nasa jawabin, Kanal Stéphane Useo ya yaba da jajircewa da ƙwazon Rundunar Sojin Nijeriya wajen fuskantar sabbin barazanar tsaro. Ya kuma buƙaci faɗaɗa damar samun manyan kwasa-kwasan soji, musamman a fannonin hulɗa da jama’a da harkokin jiragen sama.

Kanalan ya sake tabbatar da ƙudirin Faransa na zurfafa haɗin gwuiwar tsaro da Nijeriya, yana mai cewa wannan alaƙa na taimakawa wajen samar da zaman lafiya a yankin da kuma ƙarfafa ƙarfin rundunonin ƙasashen biyu.

LABARAI MASU NASABA

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

Nijeriya
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro
  • Abubakar Sulaiman
    Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama
  • Abubakar Sulaiman
    NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano
  • Abubakar Sulaiman
    Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

MASU ALAKA

Nijeriya
Manyan Labarai

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Manyan Labarai

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Nijeriya
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Next Post
Yanzu- Yanzu An Sako Masu Ibadar da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

Yanzu- Yanzu An Sako Masu Ibadar da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya

Tinubu Zai Ƙara Wa Sojoji Albashi Nan Ba Da Jimawa Ba – Ministan Tsaro

July 27, 2026
Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

Har Kullum Sin Na Adawa Da Yadda Amurka Ke Siyasantar Da Batutuwan Fasaha Da Na Tattalin Arziki

July 27, 2026
Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

Kasar Sin Ta Gabatar Da Matsaya Game Da Matakan Karshe Na Bincike Mai Lamba 301 Kan Tilasta Yin Kwadago Da Amurka Ta Fitar

July 27, 2026
Nijeriya

Taimakon Ƴan Bindiga: Kotu Ta Yanke Wa Mata 3 Hukuncin Shekaru 14 A Magarƙama

July 27, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Nijeriya

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Nijeriya

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.