ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Saurayi Ya Raunata Budurwa Tare Da Barazanar Kisa Saboda Ta Ki Son Sa A Maiduguri

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Maiduguri

Wani saurayi, Saleem Ibrahim, da ya kamu da tsananin kaunar wata budurwa, Hauwa Abatcha Ngala dukkansu daliban Jami’ar Maiduguri, ya yi mata mummunan rauni a kai saboda kin amincewa da soyayyarsa.

Kamar yadda majiyar Zagazola Makama, wani masani a kan fannin yaki da ta’addanci a yankin tafkin Chadi ta ruwaito, an ce Saleem ya dade yana kokarin tilasta wa Hauwa son sa, amma bai samu hakan ba, domin Hauwa ta yi iya kokarinta wajen cusa sa shi a zuciyarta abin ya gagara, har dai ta yanke hukuncin cewa duk irin kokarin da za ta yi na shawo kan zuciyarta ta so Saleem Ibrahim ba zai yiwu ba don ba ta jin son sa a ranta ko miskala zarratin.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Goyi Bayan Sabuwar Gwamntin Palasdinu
  • Kano Pillars Ta Kasa Zuwa Taka Leda Saboda Rashin Kuɗi 

Sakamakon haka, Hauwa ta nemi hanyoyin da za ta rabu da Saleem salim-alim don ta huta da takurawar da yake mata a kokarinsa na ganin ta so shi amma sai ya ci gaba da nuna mata naci.

ADVERTISEMENT

Duk yadda ta yi kokarin kubutar da kanta daga abubuwan da ya ke yi mata da sunan lallashinta ta so shi, amma hakan bai kara komai ba sai kinsa a ranta.

Saleem ya ki hakura har dai ya fara yi mata mummunar barazana ciki har da cewa zai iya kashe ta idan har ba ta karbi soyayyarsa.
An ruwaito cewa, ya gaya mata ko dai ta karbi soyayyarsa ko kuma ta gamu da gamonta.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

“Zan iya kashe ki kuma babu abin da zai faru,” Saleem ya yi mata kashedi kamar yadda aka ruwaito.

Wannan al’amari ya jefa Hauwa cikin tsananin bacin rai, inda ta zauna cikin wannan hali har zuwa ranar Litinin, 26 ga Fabrairu, 2024.

A ranar Litinin ta makon jiya, da misalin karfe 8:30 na dare Saleem Ibrahim ya tare Hauwa Abatcha Ngala inda ya buge ta da wani karfe har sau biyu ta fadi nan take ta suma, jini na ta zuba.

A maimakon ya yi duk wani kokari na ceto rayuwarta, saboda son da ya ke mata, kawai sai ya gudu ya bar ta nan tare da ‘yan uwanta, wadanda suka yi kokarin ceto rayuwarta ta hanyar kai mata agajin gaggawa.

Bayan ta farfado ne, ’yan uwanta suka kai rahoton lamarin ga ‘yansanda a daren wannan rana.

A dalilin haka ciki wannan dare ‘yan sa kai na JTF suka kama Saleem Ibrahim tare da mika shi ga ‘yansanda da ke ofishin Dibision na Gomari.

Sai dai kuma a ranar Juma’a 1 ga Maris, 2024, wato kwana uku da faruwar lamarin tare da kama shi, ‘yansanda sun saki Saleem bisa zargin sa hannun wasu ‘yan siyasa, ba tare da daukar wani mataki na nuna cewa dokar ta kama shi da laifi ba.

Bayan ‘yansanda sun sako Saleem, sai ya shiga shafinsa na Facebook ya aika wa Hauwa sako na sirri yana yi mata ba’a, yana mai cewa “Na na fi karfin na yi barazana a banza, duk abin da na ce zan aikata sai na yi kuma ba abin da zai faru. Na rantse da Allah, talaka ne kawai za ki ja da shi ki ci riba a kansa amma ba mutumin da ke ji da kansa kamar Saleem ba.

“Ku talakawa ba ku da gata domin ba ku da komai balle ku yi nasara a kaina. Idan kuwa har kuka yi nasara a kan wasu, na rantse da Allah Madaukakin Sarki ba za ku taba yi a kaina ba, domin muna da kudi, Hukumomin Tsaro, ‘Yan Siyasa, da Jami’an Gwamnati duk suna tare da mu. Sai dai kawai ki yi alfahari da ‘yan’uwanki, don a ci gaba da shari’ar, mu ga wane ne ke da rinjaye.”

‘Yan uwan da ransu ya baci bisa ga matakin da ‘yansandan suka dauka, sun sake shigar da kara a shalkwatar ‘yansandan Jihar Borno da ke Maiduguri, a ranar Asabar 2 ga Maris, 2024, musamman ma da ya yi zargin cewa zai kashe ta, kuma babu abin da zai faru domin shi da ne na masu hannu da shuni, wanda hakan ya fusata su.

Hakan ya sa aka sake kama Saleem tare da tsare shi tsawon mako guda a hannun ‘yansanda, amma ana zargin an sake shi kamar yadda ‘yansanda suka shaida wa iyalan cewa Sakataren gwamnatin Jihar Borno, Honarabul Bukar Tijjani ya bayar da umarnin a sake shi sannan kuma a yi watsi da karar ba tare da daukar wani mataki a kansa ba duk da ya yi wa Hauwa rauni mai tsanani na jiki da na zuciya.

Kwatsam sai ga ‘yan uwan Hauwa suka ci karo da Saleem yana yawo a titin Maiduguri cikin walwala kamar kowane dan kasa mai bin doka da oda, maimakon a ce yana hannun ‘yansanda an gurfanar da shi a gaban kotu.

Dangin Hauwa da ba su hakura ba, suka sake shigar da sabuwar kara a ofishin kwamishinan ‘yansandan Jihar Borno, (CP Yusuf Lawan) a ranar Talata, 12 ga Maris, 2024, inda suka bukaci a yi adalci a shari’ar.
Sakamakon haka ‘yansanda sun sake kama Saleem Ibrahim. A wannan karon, ‘yansanda sun gayyaci wacce lamarin ya shafa wato Hauwa kuma suka dauki rahotonta.

Daga nan ne ‘yansandan suka hada rahoto kan lamarin tare da mika shi ga ma’aikatar shari’a ta Jihar Borno.

Sai dai kawo yanzu babu wanda ya tuntubi Hauwa ko danginta, duk da Saleem ya furta cewa ya aikata laifin da kuma barazanar kashe ta.

Jummai Mshelia, Ko’odinetar Hukumar Kare Hakkin Dan Adam ta Kasa (NHRC) ta Borno, ta yi Allah-wadai da faruwar lamarin inda ta ce wannan ba komai bane illa rashin hankali, ta kuma bukaci a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu domin ya zama izna ga sauran masu aikata laifin.

Ta ce: “Mu a matsayinmu na masu kare hakkin bil’adama, hukumarmu ta kai kara ga kwamishinan ‘yansanda wanda ya bayar da umarnin a kama wanda ake zargin nan take. Muna yaba wa ’yansanda saboda saurin daukar mataki.

“An shaida mana cewa an rubuta karar zuwa ma’aikatar shari’a don neman shawararsu. Yayin da muke jiran martanin sashen, muna so mu tabbatar wa jama’a cewa za a bi diddigin shari’ar har sai mun tabbatar da an yi adalci.”

Ta shawarci jama’a da su rika kai rahoto ga hukumar kare hakkin bil’adama ta kasa ko kuma wata hukumar tsaro idan wannan ta faru domin kawar da miyagun laifuka a cikin al’umma.

Maiduguri
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Za A Bude Baje Kolin Canton Fair Na 135 A Ranar 15 Ga Watan Afrilu

Za A Bude Baje Kolin Canton Fair Na 135 A Ranar 15 Ga Watan Afrilu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.