Sojojin rundunar Operation Enduring Peace sun ceto wata mata da aka yi garkuwa da ita tare da kwato kuɗin fansa har Naira miliyan 8 a ƙaramar hukumar Qua’an Pan ta jihar Filato.
A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Kyaftin Chinonso Polycarp Oteh ya fitar, an bayyana cewa nasarar ta biyo bayan wani sumame da aka kai ranar 25 ga Afrilu, 2026, bayan tattara sahihan bayanan sirri.
Sanarwar ta ce an sace matar ne a yankin Bauna da ke ƙaramar hukumar Shendam a ranar 19 ga Afrilu, amma bayan kama wani da ake zargi da kuma yi masa tambayoyi, ya tona asirin inda aka ɓoye ta a dajin Padam, inda daga nan sojoji suka ceto ta.

Haka kuma, rundunar ta tabbatar da kwato Naira miliyan 8 da iyalan matar suka biya a matsayin kuɗin fansa, inda daga bisani aka mayar musu da kuɗin bayan nasarar aikin.
Bayan ceton nata, an kai matar asibitin gwamnati da ke Shendam domin duba lafiyarta kafin a miƙa ta ga iyalanta.
A halin yanzu, sojoji na ci gaba da sintiri da farautar sauran ‘yan ƙungiyar masu garkuwa da mutane a yankunan Shendam da Qua’an Pan.















Discussion about this post