ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta’addanci: Ko Matakan Shawo Kan Taɓarɓarewar Tsaro Za Su Yi Tasiri?

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
6 months ago
tsaro

A yayin da yankin Arewa ke ci-gaba da kamawa da wuta ba ƙaƙƙautawa a bisa ga ƙaruwar taɓarɓarewar sha’anin tsaro; shugabannin Arewa da al’ummar ƙasa na ci-gaba da nuna damuwa kan yadda yankin Arewa ya zama tarkon mutuwa.

A baya- bayan nan mayaƙan ISWAP da Boko- Haram a Arewa- Maso- Gabas da ɓarayin daji a Arewa- Maso- Yamma da Arewa ta Tsakiya sun ƙara zafafa kai hare- haren ta’addanci, garkuwa da ɗalibai da kisan gillar jami’an tsaro ta hanyar fito na fito da hukumomin tsaro tare da cin karen su ba babbaka.

  • Borno Ta Kashe Naira Biliyan 100 Kan Samar Da Tsaro A 2025 – Gwamna Zulum
  • Ƴan Majalisar Dokokin Amurka Da Na Nijeriya Sun Gudanar Da Taro Kan Ƙaruwar Rashin Tsaro

Nijeriya wadda ta kasafta kashe naira tiriliyan 2.98 a sha’anin tsaro a kasafin kuɗin 2023 da naira tiriliyan 3.25 a 2024 da kuma naira tiriliyan 4.91 a 2025 duk da jajirtattun jami’an soji amma jama’a na kuka da kokawar rashin gani a ƙasa a bisa ga yadda ake ci-gaba da fuskantar mummunan ƙalubalen taɓarɓarewar sha’anin tsaro ta yadda dubun- dubatar al’umma ke bacci da idanu ɗaya.

ADVERTISEMENT

tsaro

Kisan gillar da mayaƙan ISWAP suka yi wa babban jami’in sojin Nijeriya Birgediya Janar Musa Uba ba tare da ceto rayuwarsa ba duk da samun rahoton halin da  yake ciki gabanin faruwar bahagon lamarin ya nuna rayuwar jami’an tsaro na cikin haɗari mafi muni.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Sace ɗalibai mata 24 a Maga da ke Kebbi, da yadda ‘yan ta’addan suka kai farmaki a sakandiren katolika da ke Papiri a jihar Neja suka yi awon gaba da ɗalibai 300 da malamai 12 ya nuna kasawar hukumomin tsaro wajen sauke nauyin da ke kan su.

Ta’addancin bai tsaya a nan ba domin kuwa wasu mayaƙan sun kai farmaki a cocin CAC a jihar Kwara a inda suka kashe mutane biyu da ke ibada da garkuwa da mutane 38, sai dai an samu ceto su bayan kwanaki.

Garkuwa da ɗaliban ta tilasta rufe makarantu da dama a jihohin Kebbi, Bauchi, Yobe, Adamawa, Taraba, Filato, Neja, Kastina da Kwara a bisa ga barazanar abin da zai iya biyowa baya.

A kan hakan gwamnatin tarayya ta rufe makarantun sakandiren haɗin guiwa na tarayya 41 a faɗin ƙasa domin kare ɗaliban daga farmakin da ‘yan ta’addan ke iya kaiwa a kowane lokaci.

Dokar Ta Ɓaci

A bisa ga yadda matsalar tsaro ta kasa ci ta kasa cinyewa da yadda al’ummar ƙasa ke neman ɗauki ne dalilin da ya sa Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya kafa dokar ta ɓaci kan sha’anin tsaro da manufar kakkaɓe ayyukan ta’addanci a Nijeriya.

Tuni dai al’ummar ƙasa suka yabawa matakin gwamnatin tarayya na kafa dokar ta ɓaci kan sha’anin tsaro da zummar sake ɗaura ɗamara da sa ƙafa wando ɗaya da ‘yan ta’addan da suka jima suna gasawa jama’a aya a tafin hannu.

Daga cikin matakan da shugaban ƙasa ya ɗauka kan dokar agajin gaggawa kan sha’anin tsaro akwai baiwa rundunar ‘yan sanda damar ƙarin ɗaukar jami’ai 20, 000 ta yadda adadin jami’an za su koma dubu 50, 000.

Sai dai kasancewar adadin jami’an ‘yan sanda bakiɗaya a matakin ƙasa bai wuce 300, 000 ba da ke kariyar al’umma sama da miliyan 250, masu ruwa da tsaki a sha’anin tsaro na ganin akwai buƙatar ɗaukar dubban ɗaruruwan jami’an a kowace shekara domin yaƙi da matsalar tsaro yadda ya kamata.

Haka ma jama’a na bayyana cewar jaye jami’an ‘yan sanda daga bayar da kariyar manyan mutane da shugaba Tinubu ya yi muhimmin mataki ne da ya zo daidai lokacin da ya kamata musamman kasancewar babu wadatattun jami’an tsaro da za su tunkari matsalar tsaro gadan- gadan.

Bugu da ƙari shugaban ya kuma buƙaci Majalisar Ƙasa da ta fara aikin tabbatar da dokokin kafa rundunar ‘yan sandan jihohi da aka jima a na cece- kuce a kai domin shawo kan yawaitar ayyukan ta’addanci a faɗin ƙasa.

Dokar ta ɓacin ta kuma bayar da umurni ga hukumar jami’an tsaron farin kaya na DSS da ta tura jami’an tsaron gandun daji a cikin dazuka domin artabu da ‘yan ta’adda da ɓarayin daji tare da ɗaukar sababbin jami’ai domin tunkarar miyagun da ke aika- aika a cikin duhun daji.

Matakin shugaban ƙasa ya nuna sabon ƙudurin sake fasalin tsarin tsaron ƙasar bakiɗaya ta hanyar ƙara yawan jami’ai, inganta hanyoyin leƙen asiri da daidaita dabarun tsaro domin fuskantar sabbin barazanar da ke tasowa.

A cikin manyan sauye- sauyen da ake shirin aiwatarwa, Shugaban Ƙasa na ƙoƙarin ganin an samar da dokokin da za su ba jihohi damar kafa ’yan sandar jiha, matakin da masana ke ganin zai ƙarfafa sha’anin tsaro a jihohi da ƙananan hukumomi.

Sai dai akasin nuna goyon bayan gwamnati kamar yadda suka saba, mafi yawan wakilan Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai sun soki matakin gwamnatin tarayya kan daidaitawa da ‘yan ta’adda wajen biyan kuɗin fansar waɗanda aka yi garkuwa da su a a jihohin Kwara da Kebbi.

‘Yan majalisar sun buƙaci gwamnati ta dakatar da sulhu da ‘yan ta’adda tare da ɗaukar matakin ladabtarwa ga jami’in da ya ba da umurnin jaye jami’an tsaro da ke hadin makarantar ‘yan mata ta Maga da ke Kebbi wanda ya zama silar garkuwa da ɗalibai 24 a watan Nuwanba. Sai dai gwamnatin tarayya ta kare sulhu da ɓarayin dajin ta hanyar bayyana cewar ta ɗauki matakin ne domen kare ɗaliban daga kowace irin cutarwa.

Bugu da ƙari a na gani da kallon murabus ɗin Ministan Tsaro, Muhammad Badaru Abubakar a kwanan nan da maye gurbin sa da tsohon babban hafsan sojojin Nijeriya, Janar Christopher Musa ƙasa da kwana ɗaya wani mataki ne da Shugaba Tinubu ya ɗauka domin ƙalubalantar matsalar tsaron gadan- gadan.

Sai dai a yayin da jama’a da dama ke tambayar dalilin sake baiwa Janar Musa babban muƙamin a makwanni biyar bayan cire shi daga shugaban hafsan sojoji, wata ƙwaƙƙwarar majiya ta bayyanawa manema labarai cewar mataki ne da Tinubu ya ɗauka domin bunƙasa sha’anin tsaro.

Ƴan Majalisar Dokokin Amurka Da Na Nijeriya Sun Gudanar Da Taro Kan Ƙaruwar Rashin Tsaro

Ta’addanci: Ko Matakan Shawo Kan Taɓarɓarewar Tsaro Za Su Yi Tasiri?

Majiyar ta bayyana cewar wasu Ministoci da ke kusa da Tiinubu sun ba shi shawarar sanya ɗaya daga cikin tsofaffin sojoji da ke da ƙwarewa da gogewa a matsalar tsaro da ke addabar ƙasa a matsayin ministan tsaro

A yayin da aka tuntuɓi ra’ayin Birgediya Janar Muhammad Kabir Galadanchi (mai ritaya) ya bayyana cikakken tabbaci kan ƙwarewar Janar Musa wajen tallafawa shugaban ƙasa wajen magance matsalolin tsaro a Nijeriya.

Ya ce “Muna buƙatar wanda ke da cikakkiyar fahimtar rundunar soji da ayyukan ta domin taimakawa Shugaban Ƙasa wajen aiwatar da yawancin manufofin da suka shafi magance matsalar tsaro kuma Janar Musa na da cikakken horo da laƙantar dabarun magance wannan matsalar.”

Ya ce “Musa ya taɓa kasancewa kwamandan Depot wato cibiyar rundunar sojoji a inda ake horas da sojoji domin shiga fagen yaƙi, ya kuma kasance kwamandan yaƙi da abokan gaba, babban jami’in runduna, sannan daga baya ya zama shugaban rundunar tsaro ta ƙasa waɗanda suka nuna Janar Musa na da duk wata ƙwarewa da ake buƙata.” Ya bayyana.

Sai dai daga cikin ƙalubalen da ake ganin zai fuskanta shi ne yawaitar matsalolin tsaro a Arewa- maso- Yamma, ƙaruwar ayyukan Boko- Haram da suka sake kunno kai a Arewa- maso- Gabas tare da sake ɓullar ayyukan ta’addanci a Arewa ta Tsakiya da ƙarin sace-sace a jihohin Kudu-maso- Kudu kamar Edo da Delta da kuma wasu sassan Kudu- maso Yamma.

Sai dai akwai masu ra’ayin a bisa ga zamansa babba a kan dukkanin shugabannin hukumomin tsaro hakan zai taimaka masa ba tare da samun wani saɓani tsakaninsa da waɗanda za su yi aiki a tare.

A bayyane yake dai bayyana sanarwar dokar ta- ɓaci kan rashin tsaro da Shugaba Tinubu ya ayyana a faɗin ƙasar ta jawo muhawara mai zafi daga ɓangarori daban- daban na al’umma da masana a arewacin Nijeriya.

Yayin da yawancin masana ke ganin shugaban ya ɗauki mataki mafi dacewa domin kakkaɓe ayyukan ta’addanci, wasu kuma na ganin akwai kuskure saboda rashin sauke Gwamnonin ta hanyar miƙa mulkin jihohin da rashin tsaro ya yi mummunan ƙamari ga tsofaffin jami’an rundunar soji domin gudanar da aikin kakkaɓe ayyukan ta’addanci domin tabbatar da tsaro da kariyar rayukan al’umma kamar yadda ya yi a jihar Ribas.

tsaro
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    A Yayin Da Babban Bankin Ƙasa (CBN) Ke Yaƙi Da Laifukan Intanet
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Halin Da Matsalar Tsaro Ta Jefa ‘Yan Gudun Hijira A Arerwacin Nijeriya
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Sanata Tambuwal Ya Sadaukar Da Takararsa Ga Faruku Yabo
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dan-Iya Ya Zama Ɗan Takarar Gwamnan ADC A Sakkwato

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
’Yansanda Sun Kama Tsohon Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

’Yansanda Sun Kama Tsohon Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.