ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗantsoho Ya Zayyana Nasarorin Da Tsarin e-Call Up System Ya Samar A Tashoshin Jiragen Ruwa

by Bello Hamza
8 months ago
Ruwa

Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Ƙasa  NPA, ta ƙara nanata ƙudurinta, na ci gaba da yin amfani da tsarin fasahar zamani da a turance ake kira da, e-Call Up, domin ci gaba da magance cunkoson Jiragen Ruwa, a Tashohinta da ke a faɗin ƙasar.

Shugaban Hukumar Dakta Abubakar Ɗantsoho ne, ya bayar da wannan tabbacin a yayin da ya gabatar da wata ƙasida taron da ƙungiyar ƴan jarida mawallafa labaran fannin ta ƙasa, ta shirya.

Taken taron shi ne, dabarun yin amfai da kimiyyar zamani a ɓangaren fitar da kaya daga ƙasar da kuma shigo da su, cikin ƙasar

ADVERTISEMENT

Taron wanda ya gudana a kwanan bayam an yi shi ne a otle ɗin De Marii da ke a jihar Legas.

Dakta Ɗantsoho, ya dantanta wannan tsarin wanda ake fi sani da ETO, a matsayin wata baabbar madafa, da ya samar da sauyi a fannin sufurin Jiragen Ruwa na ƙasar, musamman wajen samar da hanyoyin yin safara a Tashohin Jiragen Ruwa na Apapa da kuma ta Tin Can Island.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

  • Yadda Tsare-tsaren Tinubu Na Fitar Da Kaya Ketare Suka Ƙara Wa NPA Ƙwarin Guiwa
  • Shugaba Tinubu Ya Karrama Shugaban NPA Da Lambar Yabo Ta Musamman

Shugaban wanda ya Manajan Darakta da ke kula da zirga-zirgar ababen hawa na Hukumar Jimoh Anthony ya wakilce shi a wajen taron ya ci gaba da cewa, yin amfani da wannna fasahar a Tashohin Jiragen Ruwan, ya taimaka matuƙa, wajen magance cunkoson na Jiragen Ruwa da ke sauka a Tashohin ƙasar.

Ɗantsoho ya ci gaba da cewa, hakan ya kuma ƙara taimaka wa, wajen samar da sauƙin gudanar da hada-hada kuma a kan lokaci, ba tare da wata tangarɗa ba, da kuma ƙara bunƙasa tattalin arzikin ƙasar nan.

“Ayau wannan kimiyyar na samar da sauƙi wajen zirga-zirga, musamman a tsakanin manyan motoci da ke shiga da kuma fita daga cikin Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar, “ Inji Shugaban.

A cewar shugaban samar da wannan fasahar zamanin, na daga cikin manyan nasarorin, da Hukumar ke tunƙaho da shi.

Ya ƙara da cewa, yin amfani da kimiyyar, ta kuma taimaka wajen magance dogon layi tare da kuma tabbatar da samar da kyakyawan yanyi da kuma gudanar da ayyukan Hukumar a cikin sauƙi.

Wani ƙarin cin nasarar ya haɗa da, kafa tsarin ganowa da kuma yin amfani da fasahar tsarin shige da fice, na manyan motocin.

Tsarin Shigar Manyan Motoci Tashoshin Na TTP:

Wannan kimiyyar za ta taimaka wajen kula da shige da kum aficen manyan motocin cikin Tashoshin Jiragen Ruwan da kuma magance cunksoson da ake samu a kan hanyoyi.

Dakta Ɗantsoho ya ƙara da cewa, fasahar ta taimaka wajen rage cunkson manyan motoci a Tashoshin Apapa da kuma ta Tin Can, inda yayi nuni da cewa, hakan ya nuna cewa, fasahar, na da matuƙar mahimmanci.

Shugaban ya ci gaba da cewa, bisa haɗakar da Hukumar ta yi da Hukumomin tsaro da kuma masu ruwa da tsaki, hakan ya ƙara taimaka wa wajen wanzar da tsarin tare da kuma magance cuinkson manyan motocin, wanda kuma hakan ke bai wa manyan motocin damar ajiye su, a wajen da ya dace.

A cewarsa, ci gaba da haɗakar da Hukumar ta NPA ke yi da masu ruwa da tsaki a fannin na sufurin Jiragen Ruwan ƙasar, hakan ya samar da nasara, wajen aiwatar da tsarin.

Kazalika, ya sanar da cewa, yin haɗaka da sauran ƙungiyoyin  ƙwadago da ke kula da wajejen ajiya manyan kaya a Tashar da kuma sauran Hukumomi, hakan ya ƙara taimaka wa tsarin, inda hakan ya kuma ƙara bunƙasa gudanar da ayyukan Hukumar a cikin nasara.

Da yake yin bayani kan ci gaban da aka samar a Hukumar ta NPA, Xantsho ya bayyana cewa, a kwanan baya, NPA ta gudanar da nazari a tsarin na E-Call Up, ya taimaka wajen toshe dukkan matsaloli da kuma ƙara ƙarfafa tsarin.

Ya sanar da cewa, ɗaya daga cikin sakamakon da aka samu shi ne, domin ƙara ƙarfafa bayar da tikiti, ga manyan motocin da ke shiga Tashoshin, ta hanyar amfani da tsarin na ETO.

A bisa ƙarƙashin tsarin na ETO, za a rinƙa sayen tikitin kai tsaye, musamman domin a toshe duk wata kafa, ta aikata almundana.

Kazalika, wani ƙarin ci gaban da aka samu shi ne, na samar da tsarin kimiyya a ƙofar shiga Tashoshin, domin karvar tiktin kai tsaye.

Hakazalika, tsarin zai ƙara rage cunkosn da kuma ƙara bunƙasa hada-hada a Tashohin.

Dakta Ɗantsoho ya ƙara jaddada cewa, tsarin na  e-Call Up wanda ya kasance na gaggawa ya taimaka wajen ƙara haɓaka ayyukan Hukumar ta NPA, ɗaukacin Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar.

Ya bai wa masu ruwa da tsaki tabbacin cewa, a ƙarƙashin shugabancinsa, Hukumar ta NPA za ta ƙara mayar da hankali, wajen samar da sauye-sauye, musamman domin a ɗora kan wannan ci gaban da aka samar a Hukumar.

“Burin shi ne, mu taimaka wa ƙasar nan, na ƙoƙarinta na dogon zango na bunƙasa gasa a fannin a tsakanin ƙasashen duniya,” Inji Ɗantsoho.

A taron, ƙungiyarta kuma karrama Shugaban na Hukumar NPA, da lambar yabo ta MARCON kan irin ɗimbin nasarorin da ya samar a NPA.

Ƙungiyar ta sanar da cewa, Ɗantsoho, ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen saita Tashoshin Jiragen Ruwa na ƙasar, inda hakan ya ƙara bunƙasa ayyukanta.

Bugu da ƙari, ƙungiyar ta kuma karrama Janar Manaja na sashen dabarun sadawar na NPA Ikechukwu Onyemekara da lambar yabo ta yaɗa labarai.

 

Ruwa
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
GORON JUMA’A 12/12/2025

GORON JUMA'A 23-01-2026

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.