Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da harin da aka kai wa mazauna ƙauyen Naridon da ke Unguwar Kamaru, Ƙaramar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna.
Shugaban Ƙasan ya kuma umarci hukumomin tsaro da na leƙen asiri da su ƙara tsaurara ayyukansu a al’ummomin da lamarin ya shafa domin gano waɗanda suka aikata harin tare da tabbatar da kuɓutar da duk wani mutum da aka yi garkuwa da shi.
Harin, wanda ya faru da sanyin safiyar Litinin, ya yi sanadin mutuwar kusan mazauna 30, ciki har da mata da yara, yayin da aka ƙona gidaje da dama.
A cikin wata sanarwa da mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara na musamman kan yaɗa labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata, Shugaba Tinubu ya bayyana harin a matsayin wani ta’addanci marar dalili da aka kai wa fararen hula marasa galihu.
Shugaba Tinubu ya jaddada cewa za a gurfanar da duk waɗanda ke ƙoƙarin kawo cikas ga zaman lafiya da tsaron da Jihar Kaduna ta samu kanta a cikin ƴan shekarun nan a gaban kotu.
Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasu, Gwamna Uba Sani, gwamnatin Jihar Kaduna da al’ummar jihar bisa wannan mummunan lamari.
Shugaban Ƙasa ya tabbatar wa gwamnatin jihar da al’ummomin da lamarin ya shafa cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da ba su goyon baya, yana mai cewa gwamnati ta ƙuduri aniyar magance ƙalubalen tsaro da ke addabar ƙasar.
Ya ce: “Na umarci Rundunar Sojin Nijeriya, ƴansanda da hukumomin leƙen asiri da abin ya shafa da su ƙara tsaurara ayyukansu a dukkan yankunan da lamarin ya shafa domin gano waɗanda suka aikata wannan aika-aika cikin gaggawa, tabbatar da kuɓutar da mutanen da aka yi garkuwa da su, da kuma dawo da zaman lafiya a yankin.”
Shugaba Tinubu ya kuma ce gwamnatinsa “ta ƙuduri aniyar ƙarfafa ababen more rayuwar tsaro, samar da kayan aiki ga jami’an da ke mayar da martani ga barazanar tsaro, da kuma kawar da ƙungiyoyin masu aikata laifuka da ke ƙoƙarin kawo cikas ga zaman lafiyar ƙasa.”
Sanarwar ta ce: “Ina kira ga al’ummomin yankunanmu da su ba jami’an tsaro haɗin kai ta hanyar samar musu da sahihan bayanan sirri da za su taimaka wajen ɗaukar matakin gaggawa.”














