ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, June 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Zaɓi Mataimakinsa Bayan Taron Jam’iyya – Fadar Shugaban Ƙasa 

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
Tinubu

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ba zai zaɓi wanda zai yi masa mataimaki a zaɓen 2027 ba sai bayan babban taron jam’iyyar APC da za a gudanar a 2026.

Mai ba shugaban ƙasa shawara kan dabarun watsa labarai, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wata hira da ya yi da Daily Trust, inda ya ce tsarin dimokuraɗiyya na ainihi yana buƙatar a fara da ɗan takara kafin a sanar da mataimaki.

  • Ganduje Ya Noƙe Kan Furta Ko Shettima Zai Yi Takara Da Tinubu A 2027
  • Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

Onanuga ya ƙaryata jita-jitar cewa akwai wani shiri na cire Mataimakin Shugaban ƙasa Kashim Shettima daga tikitin 2027, yana mai cewa babu wata matsala tsakanin Tinubu da Shettima, kuma suna da kyakkyawar alaƙa ta aiki. Ya ce batun musulmi da musulmi a matsayin tikiti bai kamata ya sake zama matsala ba, ganin cewa tun da farko ba a sami wata barazana ga rayuwar Kiristoci a Nijeriya ba.

ADVERTISEMENT

A baya dai an sami zazzafar muhawara a taron APC na yankin Arewa maso Gabas a Gombe, inda rashin haɗa sunan Shettima cikin jerin goyon bayan da ake baiwa Tinubu ya haifar da cikas. Duk da haka, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya sake bayyana cikakken goyon bayansa ga Shettima, yana mai cewa rawar da ya taka a gwamnatin Tinubu na da matuƙar tasiri ga cigaban ƙasa.

Shugaban APC na Arewa maso Gabas, Salihu Mustapha, wanda ya ƙi mara wa Shettima baya, ya ce yana bin ƙa’idar jam’iyya ne da tsarin zaɓe. Ya bayyana cewa wasu ‘yan siyasa ne ke ƙoƙarin kawo husuma tsakanin ɓangarorin biyu, lamarin da ake gani a kusan kowanne mataki na siyasa a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

A nasu ɓangaren, ƙungiyar kare haƙƙin Musulmi, MURIC, ta gargaɗi APC da Shugaba Tinubu da kada su sauya Shettima a matsayin mataimaki a 2027.

Shugaban ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya bayyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce duk wani yunkuri na cire Shettima zai zama matakin da bai dace ba kuma ya kamata a nemi shawara daga manyan masu ruwa da tsaki kafin ɗaukar kowanne mataki.

Tinubu
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Morocco Na Fargabar Rashin Ƴan Wasa 2 Gabanin Karawa Da Brazil
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Zata Biya Naira Biliyan 700 Ga Ƴan Kwangila 1,240 Da Aka Tantance
  • Abubakar Sulaiman
    Ɗiyar Obasanjo Ta Fice Daga APC Bayan Gaza Samun Tikitin Takarar Gwamna
  • Abubakar Sulaiman
    Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026
Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima
Manyan Labarai

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026
Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Next Post
GORON JUMA’A 16/05/2025

GORON JUMA'A 20-06-2025

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 7 Da Ake Zargin ‘Yan Bindiga Ne A Kebbi

June 9, 2026
Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

Legas Ce Ta Samar Da Dangote Da Abdulsamad Ba Kano Ba – Shettima

June 9, 2026
Sojoji

Ilimi Ne Babban Makamin Daƙile Ta’addanci — Ministan Tsaro

June 8, 2026
Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

Sin Da Koriya Ta Arewa Na Fuskantar Sabbin Damammaki Da Kudurori In Ji Shugaba Xi Jinping

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga EU Ta Hada Hannu Da Ita Domin Inganta Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakaninsu

June 8, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Gwamnatin Borno Ta Musanta Biyan Kuɗin Fansa Domin Kuɓutar da Mutane 360

June 8, 2026
Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

Kasar Sin Ta Fara Wani Aikin Hanyar Ruwa A Kogi Mafi Tsawo Na 3 A Duniya

June 8, 2026
Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji

June 8, 2026
Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

Xi Jinping Ya Tattauna Da Kim Jong Un

June 8, 2026
Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

Yari Ya Dace Da Rayuwar Mulki Da Kasuwanci

June 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.