ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Kayan Aiki Na Shafar Shirin Samar Da Gidaje A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Gidaje

Jami’ai a fannin gine-gine a kasar nan sun bayyana cewa, samun hauhawan farashin kayan yin gini, na janyo fannin tarnaki.

Shugaban karamar hukumar Agboyi-Ketu da ke a jihar Legas Dele Oshinowo ya bayyana hakan a kwanan baya a taron manema labarai a yankin.

  • Amurka Ta Zama Babban Cikas Ga Dakile Yakin Gaza Bayan Da Ta Hau Kujerar Na Ki
  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka

Dele ya danganta hauhawan farashin kayan na yin gini akan abubuwa da dama da suka hada da, samun sauyin kan farashin kayan, rashin tsaro, rashin samun kwararrun a fannin da sauransu.

ADVERTISEMENT

Don a lalubu da mafita kan wadannan matsalolin Dele ya ce, ana bukatar bangaren gwamnati da masu zama kansu, su kawo fannin daukin da ya dace.

Ya kara da cewa, bin ka’ida, zuba jari a fannin gine-gine da samar da shirye-shiryen bayar da horo, za su taimaka matuka wajen magance hauhawan farashin na kayan gini a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

Dele ya yi nuni da cewa, kirkiro da kyakyawan yanayi na yin kasuwanci, tabbatar da gaskiya, za su taimaka waien janyo hankalin masu son zuba jari a fannin na gine-gine, wanda hakan zai kuma taimka wajen tsadar farashin kayan na gine-gine.

Shi ma wani masani a fannin gine-gine Olorunyomi Alatise ya sanar da cewa, kara farashin kayan gini da masu saraffa su ke yi ne ke haifar da tsada a fannin gini.

Ya kara da cewa, tsadar kayan aikin na janyo tsaiko wajen gudanar da akin ginin tare da kuma shafar kasafin kudin da aka yi za a kashe don yin ginin.

A cewarsa, tsadar za ta kuma iya zamo wa masu gina gidaje don sayar wa cikas wajen samun kudaden da za su zuba don yin gine-ginen.

Ya ci gaba da cewa, tsadar ta kayan ginin za ta kima iya janyo wa a yi gini maras inganci.

A bisa kokarin da ake yi na samar da sauki kan hauhawan farashin Siminti da sauran kayan gini don a samar da gidaje masu saukin kudi a kasar nan,  a ranar Alhamis data gababa, Ministan gidaje da raya birane Ahmed Dangiwa, ya yi wata gana wa da masu sarrafa Simintin da sauran kayan gine-gine.

Bugu da kari, Dele ya kuma kaddamar da aiki na gaba da mulkinsa ya kikiro da shi don inganata rayuwar alummar karamar hukumar ta Agboyi-Ketu.

Ya kara da cewa, aikin zai mayar da hankali ne wajen tsarin gina gidaje, gina titina, yin zirga -zirga da gyarn gine-ginen hukumar.

Ya sanar da cewa, “ Muna daf da kaddamar da sassan gidajen kwana guda 170 da su dauki dakunan kwana bi biyu da kuma wasu sasaan gine-gine guda 102 da za su dauki dakunan kwana guda hudu da jimlarsu takai guda  271.

Kazalika ya ce, za a kuma samar wa da mazuna yankin da  wutar lantarki da za ta kai awa 18 suna morewa”.

Sai dai, Dele ya ce,  farashin gidajen ya karu daga Naira miliyan 15.5 zuwa Naira miliyan16.5, inda ya kara da cewa, akwai kuma gidajen  da kudinsu ya kai Naira miliyan 18.5 wadanda suka kai kimanin kashi 80 wadanda tuni, ma’aikata da sauran wasu mazuna yankin suka siya suka kuma shiga cikinsu.

Dele ya sanar da cewa, aikin da zai yi na gaba shi ne, gina sassa 248 da su dauki dakunan kwana hudu da sauransu.

Ya ce, karamar hukumar ta Agboyi Ketu, ta yi hadaka da kafanonin Google da na Microsoft domin a bayar da horo ga mazauna yankin kan fasahar zamani ta ICT.

Gidaje
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tattalin Arziki

Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas

May 24, 2026
Next Post
Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji

Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.