ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Kayan Aiki Na Shafar Shirin Samar Da Gidaje A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Gidaje

Jami’ai a fannin gine-gine a kasar nan sun bayyana cewa, samun hauhawan farashin kayan yin gini, na janyo fannin tarnaki.

Shugaban karamar hukumar Agboyi-Ketu da ke a jihar Legas Dele Oshinowo ya bayyana hakan a kwanan baya a taron manema labarai a yankin.

  • Amurka Ta Zama Babban Cikas Ga Dakile Yakin Gaza Bayan Da Ta Hau Kujerar Na Ki
  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka

Dele ya danganta hauhawan farashin kayan na yin gini akan abubuwa da dama da suka hada da, samun sauyin kan farashin kayan, rashin tsaro, rashin samun kwararrun a fannin da sauransu.

ADVERTISEMENT

Don a lalubu da mafita kan wadannan matsalolin Dele ya ce, ana bukatar bangaren gwamnati da masu zama kansu, su kawo fannin daukin da ya dace.

Ya kara da cewa, bin ka’ida, zuba jari a fannin gine-gine da samar da shirye-shiryen bayar da horo, za su taimaka matuka wajen magance hauhawan farashin na kayan gini a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

Dele ya yi nuni da cewa, kirkiro da kyakyawan yanayi na yin kasuwanci, tabbatar da gaskiya, za su taimaka waien janyo hankalin masu son zuba jari a fannin na gine-gine, wanda hakan zai kuma taimka wajen tsadar farashin kayan na gine-gine.

Shi ma wani masani a fannin gine-gine Olorunyomi Alatise ya sanar da cewa, kara farashin kayan gini da masu saraffa su ke yi ne ke haifar da tsada a fannin gini.

Ya kara da cewa, tsadar kayan aikin na janyo tsaiko wajen gudanar da akin ginin tare da kuma shafar kasafin kudin da aka yi za a kashe don yin ginin.

A cewarsa, tsadar za ta kuma iya zamo wa masu gina gidaje don sayar wa cikas wajen samun kudaden da za su zuba don yin gine-ginen.

Ya ci gaba da cewa, tsadar ta kayan ginin za ta kima iya janyo wa a yi gini maras inganci.

A bisa kokarin da ake yi na samar da sauki kan hauhawan farashin Siminti da sauran kayan gini don a samar da gidaje masu saukin kudi a kasar nan,  a ranar Alhamis data gababa, Ministan gidaje da raya birane Ahmed Dangiwa, ya yi wata gana wa da masu sarrafa Simintin da sauran kayan gine-gine.

Bugu da kari, Dele ya kuma kaddamar da aiki na gaba da mulkinsa ya kikiro da shi don inganata rayuwar alummar karamar hukumar ta Agboyi-Ketu.

Ya kara da cewa, aikin zai mayar da hankali ne wajen tsarin gina gidaje, gina titina, yin zirga -zirga da gyarn gine-ginen hukumar.

Ya sanar da cewa, “ Muna daf da kaddamar da sassan gidajen kwana guda 170 da su dauki dakunan kwana bi biyu da kuma wasu sasaan gine-gine guda 102 da za su dauki dakunan kwana guda hudu da jimlarsu takai guda  271.

Kazalika ya ce, za a kuma samar wa da mazuna yankin da  wutar lantarki da za ta kai awa 18 suna morewa”.

Sai dai, Dele ya ce,  farashin gidajen ya karu daga Naira miliyan 15.5 zuwa Naira miliyan16.5, inda ya kara da cewa, akwai kuma gidajen  da kudinsu ya kai Naira miliyan 18.5 wadanda suka kai kimanin kashi 80 wadanda tuni, ma’aikata da sauran wasu mazuna yankin suka siya suka kuma shiga cikinsu.

Dele ya sanar da cewa, aikin da zai yi na gaba shi ne, gina sassa 248 da su dauki dakunan kwana hudu da sauransu.

Ya ce, karamar hukumar ta Agboyi Ketu, ta yi hadaka da kafanonin Google da na Microsoft domin a bayar da horo ga mazauna yankin kan fasahar zamani ta ICT.

Gidaje
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Next Post
Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji

Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.