ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Kayan Aiki Na Shafar Shirin Samar Da Gidaje A Nijeriya

by Abubakar Abba
2 years ago
Gidaje

Jami’ai a fannin gine-gine a kasar nan sun bayyana cewa, samun hauhawan farashin kayan yin gini, na janyo fannin tarnaki.

Shugaban karamar hukumar Agboyi-Ketu da ke a jihar Legas Dele Oshinowo ya bayyana hakan a kwanan baya a taron manema labarai a yankin.

  • Amurka Ta Zama Babban Cikas Ga Dakile Yakin Gaza Bayan Da Ta Hau Kujerar Na Ki
  • Blinken: Idan Ba Ka Da Karfi, Za A Cinye Ka

Dele ya danganta hauhawan farashin kayan na yin gini akan abubuwa da dama da suka hada da, samun sauyin kan farashin kayan, rashin tsaro, rashin samun kwararrun a fannin da sauransu.

ADVERTISEMENT

Don a lalubu da mafita kan wadannan matsalolin Dele ya ce, ana bukatar bangaren gwamnati da masu zama kansu, su kawo fannin daukin da ya dace.

Ya kara da cewa, bin ka’ida, zuba jari a fannin gine-gine da samar da shirye-shiryen bayar da horo, za su taimaka matuka wajen magance hauhawan farashin na kayan gini a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Dele ya yi nuni da cewa, kirkiro da kyakyawan yanayi na yin kasuwanci, tabbatar da gaskiya, za su taimaka waien janyo hankalin masu son zuba jari a fannin na gine-gine, wanda hakan zai kuma taimka wajen tsadar farashin kayan na gine-gine.

Shi ma wani masani a fannin gine-gine Olorunyomi Alatise ya sanar da cewa, kara farashin kayan gini da masu saraffa su ke yi ne ke haifar da tsada a fannin gini.

Ya kara da cewa, tsadar kayan aikin na janyo tsaiko wajen gudanar da akin ginin tare da kuma shafar kasafin kudin da aka yi za a kashe don yin ginin.

A cewarsa, tsadar za ta kuma iya zamo wa masu gina gidaje don sayar wa cikas wajen samun kudaden da za su zuba don yin gine-ginen.

Ya ci gaba da cewa, tsadar ta kayan ginin za ta kima iya janyo wa a yi gini maras inganci.

A bisa kokarin da ake yi na samar da sauki kan hauhawan farashin Siminti da sauran kayan gini don a samar da gidaje masu saukin kudi a kasar nan,  a ranar Alhamis data gababa, Ministan gidaje da raya birane Ahmed Dangiwa, ya yi wata gana wa da masu sarrafa Simintin da sauran kayan gine-gine.

Bugu da kari, Dele ya kuma kaddamar da aiki na gaba da mulkinsa ya kikiro da shi don inganata rayuwar alummar karamar hukumar ta Agboyi-Ketu.

Ya kara da cewa, aikin zai mayar da hankali ne wajen tsarin gina gidaje, gina titina, yin zirga -zirga da gyarn gine-ginen hukumar.

Ya sanar da cewa, “ Muna daf da kaddamar da sassan gidajen kwana guda 170 da su dauki dakunan kwana bi biyu da kuma wasu sasaan gine-gine guda 102 da za su dauki dakunan kwana guda hudu da jimlarsu takai guda  271.

Kazalika ya ce, za a kuma samar wa da mazuna yankin da  wutar lantarki da za ta kai awa 18 suna morewa”.

Sai dai, Dele ya ce,  farashin gidajen ya karu daga Naira miliyan 15.5 zuwa Naira miliyan16.5, inda ya kara da cewa, akwai kuma gidajen  da kudinsu ya kai Naira miliyan 18.5 wadanda suka kai kimanin kashi 80 wadanda tuni, ma’aikata da sauran wasu mazuna yankin suka siya suka kuma shiga cikinsu.

Dele ya sanar da cewa, aikin da zai yi na gaba shi ne, gina sassa 248 da su dauki dakunan kwana hudu da sauransu.

Ya ce, karamar hukumar ta Agboyi Ketu, ta yi hadaka da kafanonin Google da na Microsoft domin a bayar da horo ga mazauna yankin kan fasahar zamani ta ICT.

Gidaje
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Tattalin Arziki

Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

July 11, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Next Post
Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji

Jihar Kaduna Ta Fara Ƙwaƙƙwaran Bincike Kan Yadda Lassa Ta Kashe Mutane A Asibitin Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.