ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsagaita Wuta: Wurare 5 Da Sharuɗan Iran Suka Ci Karo Da Na Amurka

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago

A ƙarshen makon nan ne ƙasashen Amurka da Iran ƙarƙashin jagorancin Pakistan za su yi wani zama a Islamabad domin tattauna yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin ƙasashen biyu.

Kwana biyu da suka gabata aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta mako biyu, domin bayar da damar tattauna cikakkiyar yarjejeniyar dakatar da yaƙin Amurka da Isra’ila da kuma Iran a wani ɓangaren.

Duka ɓangarorin biyu sun gabatar da sharuɗɗan kawo ƙarshen yaƙin da aka shafe kimanin kwana 40 ana gwabzawa.

ADVERTISEMENT
  • Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

To sai dai akwai manyan ɓangarori biyar da ƙasashen biyu suka ci karo da juna a sharuɗɗan da kowanesu ya gindaya.

A matsayinta na mai shiga tsakani, Pakistan za ta yi ƙoƙarin daidaita al’amura tare da shawo kan ɓangarorin biyu wajen sassauta sharuɗɗan nasu domin cimma yarjejeniyar ta dindindin.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

Kodayake ba a wallafa cikakkun sharuɗɗan ba, da suka haɗa da na Iran 10 da na Amurka 15, cibiyar nazarin alaƙa tsakanin ƙasashen duniya, ”Council on Foreign Relations”, ta zayyana wasu wurare biyar da ƙasashen biyu suka ci karo da juna a sharuɗɗan nasu, sun haɗa da:

Mashigar Hormuz

Mashigar Hormuz ta ƙasance ɗaya daga cikin abubuwan da aka fi ambata a tsawon lokacin wannan yaƙi.

Tun bayan fara kai mata hare-hare, Iran ta ɗauki matakin rufe mashigar a matsayin martani ga hare-haren.

Mashigar Hormuz ta ƙasance hanyar da kashi 20 cikin ɗari na man fetur da iskar gas na duniya ke bi ta wurin.

Galibin man da ke bi ta mashigar na ƙasashen Gabas ta Tsakiya da na yankin gulf ne, ƙasashen da Iran ta zarga da taimaka wa Amurka a hare-haren da take kai mata.

Sharaɗin Iran: Za ta riƙa lura da ilahirin mashigar da zirga-zirgar jigaren da ke bi ta ciki.

Sharaɗin Amurka: Iran ta sake buɗe mashigar ba tare da sanya idanu kan zirga-zirgar jiragen da ke bi ta wurin ba.

Shirin nukiliyar Iran

Wannan na ɗaya daga cikin batutuwan da suka haddasa rashin jituwa tsakanin Iran da Isra’ila da kuma Amurka.

Duka ƙasashen sun saka sharaɗi a kansa dangane da kawo ƙarshen yaƙin.

Sharaɗin Iran: Iran ta buƙaci damar ci gaba da inganta sinadarin yureniyom (uranium) zuwa wani mataki, tare da kawo ƙarshen sharuɗan hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya (IAEA) kan shirin nukiliyarta.

Sharaɗin Amurka: Amurka ta buƙaci Iran ta haƙura kacokan da burinta na ci gaba da inganta sinadarin da kuma shirinta na nukiliya.

Ƙungiyoyin da ke goyon bayan Iran

Tun bayan fara yaƙin, ƙungiyar Hezbollah da ke Lebanon ta fara kai hare-hare cikin Isra’ila, yayin da ita ma Isra’ila ta mayar da martani ta hanyar kai hare-hare a birnin Beirut.

Baya ga Hezbollah, wata ƙungiyar da ke samun goyon bayan Iran da ta so shiga yaƙin ita ce ƙungiyar ƴantawayen Houthi da ke Yemen.

Sharaɗin Iran: Iran ta buƙaci Amurka da Isra’ila su daina kai wa waɗannan ƙungiyoyi hare-hare.

Sharaɗin Amurka: Iran da daina ɗaukar nauyin ƙungiyoyin ta hanyar ba su kuɗaɗe da kayan aiki.

Taƙaita sojoji

Batun taƙaita yawan soji a yankin na daga cikin abubuwan da ɓangarorin biyu suka ci karo da juna dangane da kawo ƙarshen yaƙin.

Sharaɗin Iran: Iran na son Amurka ta bayar da tabbacin cewa ba za ta ƙara kai mata hari ba, sannan ta janye ilahirin dakarunta daga yankin Gulf da yankin Gabas ta Tsakiya.

Sharaɗin Amurka: Amurka na son Iran ta taƙaita ƙarfin sojinta.

Diyya da takunkumai

Wani abu da sharuɗan ɓangarorin biyu ke cin karo da juna a wannan yarjejeniyar shi ne biyan diyya da batun takunkuman da aka sanya wa Iran.

Ƙasar Iran ta jima tana fuskantar jerin takunkuman tattalin arziƙi a duniya sakamakon shirinta na nukiliya.

Sannan kuma wannan yaƙi ya haifar mata da ɓarna mai yawan gaske.

Sharaɗin Iran: A ɗage mata duka takunkuman da aka sanya mata, sannan a biya ta diyyar ɓarnar da aka yi mata a wannan yaƙi.

Sharaɗin Amurka: Amurka ba ta nuna muradin hakan ba, sai dai Shugaba Trump ya nuna cewa zai iya ɗage wa Iran ɗin takunkuman nata.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

MASU ALAKA

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran
Kasashen Ketare

Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

June 6, 2026
Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran
Kasashen Ketare

Kasashen Da Darajar Kudadensu Suka Fadi Da Wadanda Nasu Suka Tashi Sanadiyyar Yakin Iran

June 6, 2026
Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Next Post
James J. Heckman: Matakan Harajin Kwastam Na Kasar Amurka Sun Sabawa Ilmin Tattalin Arziki

James J. Heckman: Matakan Harajin Kwastam Na Kasar Amurka Sun Sabawa Ilmin Tattalin Arziki

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.