ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsagaita Wuta: Wurare 5 Da Sharuɗan Iran Suka Ci Karo Da Na Amurka

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago

A ƙarshen makon nan ne ƙasashen Amurka da Iran ƙarƙashin jagorancin Pakistan za su yi wani zama a Islamabad domin tattauna yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin ƙasashen biyu.

Kwana biyu da suka gabata aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta mako biyu, domin bayar da damar tattauna cikakkiyar yarjejeniyar dakatar da yaƙin Amurka da Isra’ila da kuma Iran a wani ɓangaren.

Duka ɓangarorin biyu sun gabatar da sharuɗɗan kawo ƙarshen yaƙin da aka shafe kimanin kwana 40 ana gwabzawa.

ADVERTISEMENT
  • ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa
  • Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata
  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku
  • Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives
  • Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

To sai dai akwai manyan ɓangarori biyar da ƙasashen biyu suka ci karo da juna a sharuɗɗan da kowanesu ya gindaya.

A matsayinta na mai shiga tsakani, Pakistan za ta yi ƙoƙarin daidaita al’amura tare da shawo kan ɓangarorin biyu wajen sassauta sharuɗɗan nasu domin cimma yarjejeniyar ta dindindin.

LABARAI MASU NASABA

Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Kodayake ba a wallafa cikakkun sharuɗɗan ba, da suka haɗa da na Iran 10 da na Amurka 15, cibiyar nazarin alaƙa tsakanin ƙasashen duniya, ”Council on Foreign Relations”, ta zayyana wasu wurare biyar da ƙasashen biyu suka ci karo da juna a sharuɗɗan nasu, sun haɗa da:

Mashigar Hormuz

Mashigar Hormuz ta ƙasance ɗaya daga cikin abubuwan da aka fi ambata a tsawon lokacin wannan yaƙi.

Tun bayan fara kai mata hare-hare, Iran ta ɗauki matakin rufe mashigar a matsayin martani ga hare-haren.

Mashigar Hormuz ta ƙasance hanyar da kashi 20 cikin ɗari na man fetur da iskar gas na duniya ke bi ta wurin.

Galibin man da ke bi ta mashigar na ƙasashen Gabas ta Tsakiya da na yankin gulf ne, ƙasashen da Iran ta zarga da taimaka wa Amurka a hare-haren da take kai mata.

Sharaɗin Iran: Za ta riƙa lura da ilahirin mashigar da zirga-zirgar jigaren da ke bi ta ciki.

Sharaɗin Amurka: Iran ta sake buɗe mashigar ba tare da sanya idanu kan zirga-zirgar jiragen da ke bi ta wurin ba.

Shirin nukiliyar Iran

Wannan na ɗaya daga cikin batutuwan da suka haddasa rashin jituwa tsakanin Iran da Isra’ila da kuma Amurka.

Duka ƙasashen sun saka sharaɗi a kansa dangane da kawo ƙarshen yaƙin.

Sharaɗin Iran: Iran ta buƙaci damar ci gaba da inganta sinadarin yureniyom (uranium) zuwa wani mataki, tare da kawo ƙarshen sharuɗan hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya (IAEA) kan shirin nukiliyarta.

Sharaɗin Amurka: Amurka ta buƙaci Iran ta haƙura kacokan da burinta na ci gaba da inganta sinadarin da kuma shirinta na nukiliya.

Ƙungiyoyin da ke goyon bayan Iran

Tun bayan fara yaƙin, ƙungiyar Hezbollah da ke Lebanon ta fara kai hare-hare cikin Isra’ila, yayin da ita ma Isra’ila ta mayar da martani ta hanyar kai hare-hare a birnin Beirut.

Baya ga Hezbollah, wata ƙungiyar da ke samun goyon bayan Iran da ta so shiga yaƙin ita ce ƙungiyar ƴantawayen Houthi da ke Yemen.

Sharaɗin Iran: Iran ta buƙaci Amurka da Isra’ila su daina kai wa waɗannan ƙungiyoyi hare-hare.

Sharaɗin Amurka: Iran da daina ɗaukar nauyin ƙungiyoyin ta hanyar ba su kuɗaɗe da kayan aiki.

Taƙaita sojoji

Batun taƙaita yawan soji a yankin na daga cikin abubuwan da ɓangarorin biyu suka ci karo da juna dangane da kawo ƙarshen yaƙin.

Sharaɗin Iran: Iran na son Amurka ta bayar da tabbacin cewa ba za ta ƙara kai mata hari ba, sannan ta janye ilahirin dakarunta daga yankin Gulf da yankin Gabas ta Tsakiya.

Sharaɗin Amurka: Amurka na son Iran ta taƙaita ƙarfin sojinta.

Diyya da takunkumai

Wani abu da sharuɗan ɓangarorin biyu ke cin karo da juna a wannan yarjejeniyar shi ne biyan diyya da batun takunkuman da aka sanya wa Iran.

Ƙasar Iran ta jima tana fuskantar jerin takunkuman tattalin arziƙi a duniya sakamakon shirinta na nukiliya.

Sannan kuma wannan yaƙi ya haifar mata da ɓarna mai yawan gaske.

Sharaɗin Iran: A ɗage mata duka takunkuman da aka sanya mata, sannan a biya ta diyyar ɓarnar da aka yi mata a wannan yaƙi.

Sharaɗin Amurka: Amurka ba ta nuna muradin hakan ba, sai dai Shugaba Trump ya nuna cewa zai iya ɗage wa Iran ɗin takunkuman nata.

Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

MASU ALAKA

Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?
Kasashen Ketare

Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

July 25, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Next Post
James J. Heckman: Matakan Harajin Kwastam Na Kasar Amurka Sun Sabawa Ilmin Tattalin Arziki

James J. Heckman: Matakan Harajin Kwastam Na Kasar Amurka Sun Sabawa Ilmin Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.