ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tun Muna Kanana Aka Dora Mu A Kan Kyakkyawar Tarbiyya —Dakta Zahra’u

by Bilkisu Tijjani
4 years ago
Zahra'u

Hajiya Dakta Zahra’u Muhammad Umar, ita ce Kwamishiniyar Ma’aikatar Mata da cigaban al’umma ta Jihar Kano, kuma tsohuwar Mataimakiyar Kwamdan Hukumar Hisba ta Jihar Kano, ‘yar Gwagwarmaya mai fafutukar kula da darajar Mata da Kananan Yara.

A tattaunawarta da Wakilinmu a Kano Abdullahi Muhammad Sheka, Dakta Zahra’u Muhammad Umar ta bayyana matukar damuwarta Kan halin da yara Mata da kananan yara ke tsintar kansu a ciki. Ga dai yadda Tattaunawar ta kasance.

  • Gamayyar Matasan Arewa A Kudu Ta Yi Tir Da Karuwar Ta’addanci A Arewa

Za muso Jin dawa Muke tare a wannan Lokaci?
Alhamdulillahi Ni dai sunana Dakta Zahra’u Muhammad Umar Kwamishiniyar Ma’aikatar Mata da cigaban al’umma Ta Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Bayyanawa Jama’a takaitaccen tarihin Gwagwarmayar rayuwar ki?
Gaskiya ne ansha fama da Gwagwarmaya tun muna kanana wajen kokarin dora mu a kan kyakkyawar tarbiya, har kuma zuwa lokacin da aka samu a makarantar firamare, na yi Sakandire har kuma zuwa Jami’a tare da samun digiri har da digir-digir, na zama Mataimakiyar Kwamdan Hukumar Hisba na Jihar Kano, gashi kuma yanzu Allah cikin ikonsa ni ce Kwamishiniyar Ma’aikatar Mata ta Jihar Kano.

Kasancewar ki Mace kuma gashi kina matsayin Kwamishiniya a wannan ma’aikata, shin ko ya aka samu ma’aikatar?
Alhamdulillahi Allah ya kawo ni wannan Ma’aikata kuma Alhamdulillahi na samu wannan ma’aikata cikin tsari, tana da sassa daban-daban wadanda suka hada da sashin lura da matsalar barace-barace, kangararrun yara, sashin lura da harkokin mata da sauransu, kuma ma’aikatan hukumar kowa na aikinsa yadda ya kamata, duk abinda aka basu shi suke ba wanda yake wasa da aikinsa.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Zahra'u
Gwamnan Ganduje (a dama) tare da Dakta Zahra’u Muhammad Umar

Batun barace-barace na cikin ayyukan da suka rataya a wuyan wannan hukuma, ko ya ake kallon wannan kalubalen?
Wannan lamari shi ne babban kalubalen da wannan Ma’aikata ke fama dashi, kuma kasancewar dukkan karatuttukan da na yi a fannin addini ne, sannan duk wanda ke bibiyar hadisan Annabi Muhammad (SAW) ya sa ya hana bara, kamar yadda Allah ta’ala ya hana ta, harma Annabi yake cewa duk wanda ya mayar da barace-barace ko roke-roke zai tashi ranar alkiyama fuskarsa babu tsoka duk sai kasusuwa.
Wannan tasa a ganina ni yakamata ma nafi bayar da gudunmawa wajen hana barace-barace, saboda irin yadda addini ya nuna mana ilar bara. Amma dai saboda wannan aiki Ma’aikatar Mata kadai ba za ta iya ita kadai ba, hakan tasa na rubuta wa Gwamna shawarar samar da hukuma guda domin tunkarar wannan aiki, kuma alhamdulillahi an samar da wannan bangare kuma aiki na ci gaba yadda ake bukata.

Ina batun yara masu matsalar kangarewa, ko shaye shayen miyagun kwayoyi, shin me ake a kan Haka?
Kaji bangaren dake matukar tayar min da hankali, wanda yanzu Haka mun kammala dukkan shirye-shirye an bude cibiyar lura da masu irin waccan matsalar a garin Kiru, kuma an samar da kwararrun masana kama daga Likitoci, Malaman Jami’a da sauran masu Ilimi a wannan bangare, an bude gidan da yara 30, ana kula da abincinsu gangariya, lafiya, tsafa da duk abinda ake nema, sannan babu fita.
Muna kara yi wa Allah godiya naga faifan bidiyonsu Malam Gwanin sha’awa, harma tsoro nake kar bayan kammala samun lafiyarsu su ki yarda da komawa gidajensu, sakamakon irin rikitibar da suke sharba a wannan gidan lura da gyaran hali, kuma wani abin sha’awa ‘ya kudi kakilan ake karba wajen kula da yaran, Gwamnatin Ganduje ce ke daukar mafi yawan nauyin.

Ya ya dangantakar aiki take tsakanin ki da Ma’aikatan wannan Ma’aikata?
Ni ba abinda zance da abokan aikinna sai godiya suna yin duk abinda ake bukata, kuma kamar yadda ma’aiki ke shawarar sahabansa, haka Nima na nauki irin wannan umarni, duk abinda zan yi sai na shawarce su, hakan tasa muke aiki tare cikin nutsuwa da Jin dadi.

Gwamnatin Gwamna Ganduje ta ciki Shekara 7 da doriya, shin ko kwalliya ta biya kudin sabulu?
Alhamdulillahi Gwamna Ganduje ya cika alkawarin da ya yi wa Kanawa harma da kari, musamman idan aka dubi yadda ya mayar da birnin Kano wani kasaitaccen birni, dubi gadojin sama da kasa sai kace a Dubai, dubi manyan Asibitoci musamman asibitin kwararru na Muhammadu Buhari dake Giginyu, dubi na yara dake titin zuwa Gidan Zoo, samar da cibiyar koya sana’u ta Aliko Dagote, Dubi Inganta Harkar
Noma, tsaro da Tallafa wa Mata da matasa a Kananan Hukumomin Jihar Kano 44 wadda Mai Dakin Gwamnan ke kai gauro ta kai mari ana saukewa Mata kabakin arzikin.

Zahra'u
Dakta Zahra’u Muhammad Umar

Wasu a batun Fidda wanda zai yi wa Jam’iyyar APC takarar kujerar Gwamna a shekara ta 2023 wasu sun yi zanton yadda masu abin hannu suka bazo zawarcin wannan kujera, kwatsam kuma sai aka ji Gwamna Ganduje ya nuna mataimakinsa, me hakan ya nuna?
“Gaskiya da rikon amana”, tsantseni da sanin ya kamata sannan uwa uba rashin kwadayin mai girma Gwamna, wannan ke tabbatar da kaunar da Ganduje kewa Kano da Kanawa, daukar mataimakinsa alama ce ta adalci, wanda kuma duk duniya an Jinjina masa bisa yakana da dattako.

Duk da kila ke ba malamar lissafi bace, amma da za’a ce ki baiwa Gwamnatin Ganduje maki, shin ko maki nawa zaki bashi?
Alhamdulillahi ba don matsalar Korona ba da maki 100% bisa 100% zan bashi, domin bayan alkawurran da ya dauka har sai da ya yi kari, domin baya cikin alkawarin da ya yi alokacin yakin neman zabe cewa zai kara yawan Masarautu a Kano, gashi ya yi, tuni wadannan garuruwan sun zama birane, kalli batun Ilimi Kyauta kuma wajibi ga kowa, ko Hasidin iza hasada ya yarda Ganduje ya ciri tuta.

Yanzu da ake tunkarar Zaben Shekara ta 2023 wadda Kuma Gawuna ne Dan Takarar Jam’iyyar APC, shin koya kike Kallon nagartar dan takarar naku?
Ai daman kyan da ya gaji ubansa, mun gamsu tare da yakinin tsayar da Gawuna wannan takara Alhairi ne ga Kano da Kanawa, ba karamin hange Gwamna Ganduje ya yi ba wajen nuna Gawuna a matsayin wanda da yardar Allah zai gaji buzunsa.

Me Kika fi sha’awar Ma’aikatan da kuka Yi aiki tare su dinga tunaki dashi?
Kyakkyawan Adalcin mu ka kwatanta tare da abokan aikinmu, sannan su kara himmatuwa Wajen dorawa inda Muka tsaya.

Mene sakon ki na karshe?
“Jama’a su kara Jajircewa wajen tarbiyar yaransu, wannan lamari shi ne yafi tsayamin a rai, ka ga Yara ana tsinto su a kwararo, wasu suce korosu akayi daga gida, Idan kuma muka gayyaci iyayen alokuta da dama sai kaga Uwar ko uban sunfi yaran bukatar taimako, Haka muke ta fama. Don Haka Ina kara kira ga iyaye a ci gaba da addu’a a tarbiyantar Yara, sai Allah ya jikanmu.

Muna godiya
Nima na gode

Zahra'u
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
2023: Masu Ruwa Da Tsaki A APC Sun Bukaci Zulum Ya Zama Abokin Takarar Tinubu

2023: Masu Ruwa Da Tsaki A APC Sun Bukaci Zulum Ya Zama Abokin Takarar Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.