• Leadership Hausa
Monday, January 30, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Bakon Marubuci

Wa Ya Dace Al’umma Su Zaba?

by Yusuf Shuaibu
3 months ago
in Bakon Marubuci
0
Wa Ya Dace Al’umma Su Zaba?

Daga lokacin da aka kada gangar siyasa ta zaben 2023, ‘yan siyasa daga kowace jam’iyya da take da rajista a Nijeriya suka fara baza dabarunsu ta neman kuri’un jama’a domin samun damar darewa madafun iko.

A ‘yan shekarun baya, manyan dabarun da ‘yan siyasar suka fi amfani da su su ne: sayo shinkafa, gishiri, sukari, sabulu, da atamfofi domin rabawa ga jama’a don a zabensu.

  • Hanyoyin Kula Da Fatar Jiki (4)
  • Zamanintarwa Irin Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Shimfida Zaman lafiya Da Kwanciyar Hankalin Duniya

Kan wadannan ‘yan kayayyaki da ba su fi su yi wa mutum mako guda a gidansa ba (kason da aka ba shi) sai a jefa kuri’a ga wanda idan ya ci, ya cika wandonsa da iska ke nan sai kuma wani lokacin zaben bayan wa’adin shekara hudu.

Amma ga dukkan alamu a wannan kakar siyasar, dabarun ‘yan siyasar na daukar sabon salo, daga sayen kayan masarufi zuwa bayar da zunzurutun kudi da kuma amfani da yanayin da mutane suka tsinci kansu a ciki wajen kai musu tallafin gaggawa.

A kwanan nan baya ga matsalar tsaro, babu wani abu da ke ci wa jama’a tuwo a kwarya kamar ambaliyar ruwa.

Labarai Masu Nasaba

Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?

Ya Wajaba INEC Ta Hana Yakin Neman Zabe Bisa Amfani Da Addini

Yanzu haka ‘yan siyasa sun yi nisa wajen nuna tausayawa da alhini da kuma bayar da gudunmawa ga jama’ar da ibtila’in ya shafa.

Dama dai tun a farkon daminar bana, hukumar kula da harkokin albarkatun ruwa ta Nijeriya (NIHSA) tare da takwararta ta hasashen yanayi ta NIMET sun yi hasashe cewa za a samu yiwuwar ambaliyar ruwa a kananan hukumomi 23 da ke jihohi 32 har da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Hakan ya kuma faru, wanda ‘yan siyasa suke ta amfani da wadanda ibtila’in ya fada musu wajen tallafa manufofinsu ta siyasa.

‘Yan takara musamman masu neman shugabancin kasa sai kai ziyara inda wannan lamarin ya auku suke tare da bayar da tallafi ga wadanda annobar ta shafa.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023, Asiwaju Bola Tinubu ya ba da tallafin Naira miliyan 50 ga jama’ar da ambaliyar ruwa ta shafa a Jihar Jigawa, ga na baya-bayan nan da ya bayar da Naira milyan100 ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a Kano.

Shi kuwa dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar LP, Peter Obi ya ziyarci Jihar Benuwe, inda ya bayar da tallafin Naira miliyan biyar.

Haka kuma ya kai ziyara a Jihar Bayelsa inda ya jajanta masu da nuna jimaminsa kan faruwar lamarin.

Atiku Abubakar da ke neman takarar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar PDP shi maya bai wa wadanda ambaliyar ruwa na kasuwar Kantin Kwari da ke Kano tallafin Naira milyan 50.

Na baya-bayan nan kuwa shi ne wanda ya bai wa wadanda ibtila’in ya shafa a Jihar Yobe kayayyakin abinci da sauran wasu abubuwa.

Shi ma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso yayi nasa kokarin duk da babu wata shaida baro-baroa fili.

Haka abubuwan suke ga kananan ‘yan siyasa masu neman takara a matakin jihohi da tarayya wajen jajanta wa al’ummar da ibtila’in ruwa ta shafa tare da ba su tallafi, wanda ko ba a fada ba, mai hankali ya san don yakin neman zabe suke yi.

Yanzu muna so al’ummar Nijeriya ta yi wa kanta adalci tare da auna wadannan ‘yan takarar guda biyu da za mu kawo a kasa.

Wai da dan takarar da ya ziyarci wadanda ibtila’in ambaliyar ruwa ta shafa, ya tashi takanas-ta-kano ya tafi inda suke ya jajanta musu, har ma saboda tausayi ya zubar da hawaye amma bai ba su kobo ba.

Da kuma dan takarar da shi bai samu ziyartar inda suke ba, amma sai ya aike musu da da makudan kudade da sakon jaje.

Shin wa ya kamata su zaba? Ina fatan wadanda ambaliyar ruwa ta rutsa da su wadanda suka hada da Hausawa da Yarbawa da Inyamurai za su bayar da sakamako iri daya.

Domin, cikin wadannan ‘yan takarar biyu, wanda ya nuna alhini har da sa abin a cikin ransa tare da zubar da hawaye, ana ganin kilazai fi tausaya musu idan ya samu madafun iko, watakila ma ya magance musu abin da ke haddasa ambaliyar har Abadan.

Yayin da wanda ya ba su kudi kuma bai shigar da abin cikin ransa, na iya biris da su saboda ya sallame su tun kafin ya hau mulki.

Siyasar kudi ta riga ta ratsa zukatan ‘Yan Nijeriya da dama wanda shawo kan wannan lamari na da matukar wahalar gaske.

Idan za a iya tunawa, a Shirinmu na Manhajar Podcast na Barka Da Hantsi Nijeriya da muka gabatar a farkon watan Oktoba tare da daya daga cikin dattawan kasa, Dakta Hakeem- Baba Ahmad, ya bayyana hatsarin sayen kuri’u da kuma yadda za a iya samun sahihin zabe a 2023.

Haka ma masu shirhin al’amurar siyasa suna ta kira ga ‘yan Nijeriya da su yi kokarin kauce wa sayar da kuri’unsu ga dukkan wani dan takara, su yi kokarin zaben ‘yan takarar da suka dace.

Wannan ne ya sa kungiyoyin arewa daban-daban suka taru a karkashin inuwa guda suka tattauna da ‘yan takarar domin jin manufofinsu da yadda za a kauce wa fadawa gidan jiya a yankin arewa.

Wani babban abin takaici dai shi ne, yadda ‘yan siyasa ke jan ra’ayoyin mutane da ‘yan kudi kalilan.

Inda a baya suke bayar da kudi daga Naira 10,000 zuwa 5,000, amma a halin yanzu kudin bai wuce dubu daya zuwa biyu, kai akwai ma idan ake bai wa mutum dari biyar ya sayar da ‘yancinsa na tsawon shekaru hudu masu zuwa, kamar yadda aka ga misalign haka a zabukan da aka yi a wasu jihohin kudu a kwanan bayan nan kamar Ekiti da Osun.

Wannan babban abin takaici ne ga al’ummar Nijeriya, musamman a daidai lokacin da abubuwa suka rikice. Ana tunanin babu abinda zai iya sauya matsalolin da suke addabar Nijeriya da kuma ‘yan Nijeriya face shugabanci nagari.

Idan kuwa haka ne, to ya kamata ‘yan Nijeriya su yi karatun ta-natsu wajen sanin dan takarar da za su zaba da zai kawo kyakkyawan shugabanci ba tare da la’akari da kabilanci, addini ko kuma bangarenci.

Yana da matukar muhimmanci ‘yan Nijeriya su guji kwadayin kudaden da ‘yan takara suke ba su wajen zaben shugaba ko wakili da zai jagoranci al’umma na tsawon shekaru hudu.

Sayen kuri’u wajen zaben shugaba ba zai taba haifar wa da al’ummar Nijeriya da mai ido ba,zai ci gaba da jefa kasar da mutanen kasar a cikin mawuyacin hali, baya ga wanda suke fuskanta yanzu haka!

Tags: 'Yan TakaraHakeem Baba AhmedKuri'a Masu ZabeSiyasaZaben 2023
Previous Post

Ruhin Hanyar Ruwa Ta Red Flag Zai Ci Gaba Da Kasancewa Har Abada

Next Post

Wang Yi Ya Gana Da Jakadan Amurka Dake Kasar Sin

Related

Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?
Bakon Marubuci

Yarfe Da Kazafi Tsakanin Manyan ‘Yan Takarar Shugabancin Nijeriya: Duk Gautar Ja Ce?

2 days ago
Ya Wajaba INEC Ta Hana Yakin Neman Zabe Bisa Amfani Da Addini
Bakon Marubuci

Ya Wajaba INEC Ta Hana Yakin Neman Zabe Bisa Amfani Da Addini

1 week ago
Ko Ayyana Goyon Baya Ga Dan Siyasa Da Wasu Ke Yi Zai Yi Tasiri?
Bakon Marubuci

Ko Ayyana Goyon Baya Ga Dan Siyasa Da Wasu Ke Yi Zai Yi Tasiri?

2 weeks ago
Emefiele: Duk Mai Tunanin Sauro Ya Yi Kadan Bai Kwana Da Shi Ba Ne!
Bakon Marubuci

Emefiele: Duk Mai Tunanin Sauro Ya Yi Kadan Bai Kwana Da Shi Ba Ne!

3 weeks ago
Bukatar Sake Fasalin Yadda Ake Karbar Sabon Katin Zabe
Bakon Marubuci

Bukatar Sake Fasalin Yadda Ake Karbar Sabon Katin Zabe

4 weeks ago
Man Kolmani: Yaushe Za A Fara Cin Moriyarsa?
Bakon Marubuci

Man Kolmani: Yaushe Za A Fara Cin Moriyarsa?

2 months ago
Next Post
Wang Yi Ya Gana Da Jakadan Amurka Dake Kasar Sin

Wang Yi Ya Gana Da Jakadan Amurka Dake Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Samar Da Karfin Farfado Da Tattalin Arzikin Duniya A Shekarar 2023

Kasar Sin Za Ta Samar Da Karfin Farfado Da Tattalin Arzikin Duniya A Shekarar 2023

January 30, 2023
Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Bunkasa Farfadowar Tattalin Arziki Da Daidaito A Fannin Cinikayyar Waje Da Zuba Jari

Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Bunkasa Farfadowar Tattalin Arziki Da Daidaito A Fannin Cinikayyar Waje Da Zuba Jari

January 29, 2023
Buhari Ya Nada Dogara A Matsayin Sabon Darakta Janal Na Hukumar NYSC

Buhari Ya Nada Dogara A Matsayin Sabon Darakta Janal Na Hukumar NYSC

January 29, 2023
Jirgin Sama Kirar Kasar Sin Samfurin C919 Ya Tashi A Karon Farko Cikin Sabuwar Shekarar Zomo

Jirgin Sama Kirar Kasar Sin Samfurin C919 Ya Tashi A Karon Farko Cikin Sabuwar Shekarar Zomo

January 29, 2023
Sin Na Gabatar Da Kyakkyawan Misali A Fannin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa In Ji Wani Masani

Sin Na Gabatar Da Kyakkyawan Misali A Fannin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa In Ji Wani Masani

January 29, 2023
APC Ta Kasa Cika Alƙawarin Sauya Fasalin Ƙasa, In Ji Atiku

APC Ta Kasa Cika Alƙawarin Sauya Fasalin Ƙasa, In Ji Atiku

January 29, 2023
Kwantena Ta Latse Wata Motar Bas, Ta Kashe Fasinjoji 8 A Legas

Kwantena Ta Latse Wata Motar Bas, Ta Kashe Fasinjoji 8 A Legas

January 29, 2023
Abubuwan 5 Da Zaku So Ku Ji A Ganawar Gwamnan CBN Da Shugaba Buhari A Daura

Abubuwan 5 Da Zaku So Ku Ji A Ganawar Gwamnan CBN Da Shugaba Buhari A Daura

January 29, 2023
Inganta Ilimi: Gwamnatin Jihar Gombe Ta Dauki Karin Sabbin Malamai 1,000 Aiki

Inganta Ilimi: Gwamnatin Jihar Gombe Ta Dauki Karin Sabbin Malamai 1,000 Aiki

January 29, 2023
Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano Ta Cafke Jarumar TikTok Murja Ibrahim Kunya

Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano Ta Cafke Jarumar TikTok Murja Ibrahim Kunya

January 29, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.