ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa Ya Dace Al’umma Su Zaba?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Zaba

Daga lokacin da aka kada gangar siyasa ta zaben 2023, ‘yan siyasa daga kowace jam’iyya da take da rajista a Nijeriya suka fara baza dabarunsu ta neman kuri’un jama’a domin samun damar darewa madafun iko.

A ‘yan shekarun baya, manyan dabarun da ‘yan siyasar suka fi amfani da su su ne: sayo shinkafa, gishiri, sukari, sabulu, da atamfofi domin rabawa ga jama’a don a zabensu.

  • Hanyoyin Kula Da Fatar Jiki (4)
  • Zamanintarwa Irin Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Shimfida Zaman lafiya Da Kwanciyar Hankalin Duniya

Kan wadannan ‘yan kayayyaki da ba su fi su yi wa mutum mako guda a gidansa ba (kason da aka ba shi) sai a jefa kuri’a ga wanda idan ya ci, ya cika wandonsa da iska ke nan sai kuma wani lokacin zaben bayan wa’adin shekara hudu.

ADVERTISEMENT

Amma ga dukkan alamu a wannan kakar siyasar, dabarun ‘yan siyasar na daukar sabon salo, daga sayen kayan masarufi zuwa bayar da zunzurutun kudi da kuma amfani da yanayin da mutane suka tsinci kansu a ciki wajen kai musu tallafin gaggawa.

A kwanan nan baya ga matsalar tsaro, babu wani abu da ke ci wa jama’a tuwo a kwarya kamar ambaliyar ruwa.

LABARAI MASU NASABA

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

Yanzu haka ‘yan siyasa sun yi nisa wajen nuna tausayawa da alhini da kuma bayar da gudunmawa ga jama’ar da ibtila’in ya shafa.

Dama dai tun a farkon daminar bana, hukumar kula da harkokin albarkatun ruwa ta Nijeriya (NIHSA) tare da takwararta ta hasashen yanayi ta NIMET sun yi hasashe cewa za a samu yiwuwar ambaliyar ruwa a kananan hukumomi 23 da ke jihohi 32 har da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Hakan ya kuma faru, wanda ‘yan siyasa suke ta amfani da wadanda ibtila’in ya fada musu wajen tallafa manufofinsu ta siyasa.

‘Yan takara musamman masu neman shugabancin kasa sai kai ziyara inda wannan lamarin ya auku suke tare da bayar da tallafi ga wadanda annobar ta shafa.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023, Asiwaju Bola Tinubu ya ba da tallafin Naira miliyan 50 ga jama’ar da ambaliyar ruwa ta shafa a Jihar Jigawa, ga na baya-bayan nan da ya bayar da Naira milyan100 ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a Kano.

Shi kuwa dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar LP, Peter Obi ya ziyarci Jihar Benuwe, inda ya bayar da tallafin Naira miliyan biyar.

Haka kuma ya kai ziyara a Jihar Bayelsa inda ya jajanta masu da nuna jimaminsa kan faruwar lamarin.

Atiku Abubakar da ke neman takarar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar PDP shi maya bai wa wadanda ambaliyar ruwa na kasuwar Kantin Kwari da ke Kano tallafin Naira milyan 50.

Na baya-bayan nan kuwa shi ne wanda ya bai wa wadanda ibtila’in ya shafa a Jihar Yobe kayayyakin abinci da sauran wasu abubuwa.

Shi ma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso yayi nasa kokarin duk da babu wata shaida baro-baroa fili.

Haka abubuwan suke ga kananan ‘yan siyasa masu neman takara a matakin jihohi da tarayya wajen jajanta wa al’ummar da ibtila’in ruwa ta shafa tare da ba su tallafi, wanda ko ba a fada ba, mai hankali ya san don yakin neman zabe suke yi.

Yanzu muna so al’ummar Nijeriya ta yi wa kanta adalci tare da auna wadannan ‘yan takarar guda biyu da za mu kawo a kasa.

Wai da dan takarar da ya ziyarci wadanda ibtila’in ambaliyar ruwa ta shafa, ya tashi takanas-ta-kano ya tafi inda suke ya jajanta musu, har ma saboda tausayi ya zubar da hawaye amma bai ba su kobo ba.

Da kuma dan takarar da shi bai samu ziyartar inda suke ba, amma sai ya aike musu da da makudan kudade da sakon jaje.

Shin wa ya kamata su zaba? Ina fatan wadanda ambaliyar ruwa ta rutsa da su wadanda suka hada da Hausawa da Yarbawa da Inyamurai za su bayar da sakamako iri daya.

Domin, cikin wadannan ‘yan takarar biyu, wanda ya nuna alhini har da sa abin a cikin ransa tare da zubar da hawaye, ana ganin kilazai fi tausaya musu idan ya samu madafun iko, watakila ma ya magance musu abin da ke haddasa ambaliyar har Abadan.

Yayin da wanda ya ba su kudi kuma bai shigar da abin cikin ransa, na iya biris da su saboda ya sallame su tun kafin ya hau mulki.

Siyasar kudi ta riga ta ratsa zukatan ‘Yan Nijeriya da dama wanda shawo kan wannan lamari na da matukar wahalar gaske.

Idan za a iya tunawa, a Shirinmu na Manhajar Podcast na Barka Da Hantsi Nijeriya da muka gabatar a farkon watan Oktoba tare da daya daga cikin dattawan kasa, Dakta Hakeem- Baba Ahmad, ya bayyana hatsarin sayen kuri’u da kuma yadda za a iya samun sahihin zabe a 2023.

Haka ma masu shirhin al’amurar siyasa suna ta kira ga ‘yan Nijeriya da su yi kokarin kauce wa sayar da kuri’unsu ga dukkan wani dan takara, su yi kokarin zaben ‘yan takarar da suka dace.

Wannan ne ya sa kungiyoyin arewa daban-daban suka taru a karkashin inuwa guda suka tattauna da ‘yan takarar domin jin manufofinsu da yadda za a kauce wa fadawa gidan jiya a yankin arewa.

Wani babban abin takaici dai shi ne, yadda ‘yan siyasa ke jan ra’ayoyin mutane da ‘yan kudi kalilan.

Inda a baya suke bayar da kudi daga Naira 10,000 zuwa 5,000, amma a halin yanzu kudin bai wuce dubu daya zuwa biyu, kai akwai ma idan ake bai wa mutum dari biyar ya sayar da ‘yancinsa na tsawon shekaru hudu masu zuwa, kamar yadda aka ga misalign haka a zabukan da aka yi a wasu jihohin kudu a kwanan bayan nan kamar Ekiti da Osun.

Wannan babban abin takaici ne ga al’ummar Nijeriya, musamman a daidai lokacin da abubuwa suka rikice. Ana tunanin babu abinda zai iya sauya matsalolin da suke addabar Nijeriya da kuma ‘yan Nijeriya face shugabanci nagari.

Idan kuwa haka ne, to ya kamata ‘yan Nijeriya su yi karatun ta-natsu wajen sanin dan takarar da za su zaba da zai kawo kyakkyawan shugabanci ba tare da la’akari da kabilanci, addini ko kuma bangarenci.

Yana da matukar muhimmanci ‘yan Nijeriya su guji kwadayin kudaden da ‘yan takara suke ba su wajen zaben shugaba ko wakili da zai jagoranci al’umma na tsawon shekaru hudu.

Sayen kuri’u wajen zaben shugaba ba zai taba haifar wa da al’ummar Nijeriya da mai ido ba,zai ci gaba da jefa kasar da mutanen kasar a cikin mawuyacin hali, baya ga wanda suke fuskanta yanzu haka!

Zaba
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar
Bakon Marubuci

Buni Ya Nuna Kwarewarsa Ta Diflomasiyya

August 28, 2026
An Kusa Ceto Ɗaliban Neja Da Aka Sace – Ribadu
Bakon Marubuci

Shin Tinubu Ya Tabbatar Da Sauke Ribadu Daga Mukaminsa?

August 28, 2026
Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya
Bakon Marubuci

Kwairanga Ya Kafa Tarihi A Shugabancin Hukumar Kula Da Kasuwar Hannun Jari Ta Nijeriya

July 24, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Gana Da Jakadan Amurka Dake Kasar Sin

Wang Yi Ya Gana Da Jakadan Amurka Dake Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.