ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa Ya Dace Al’umma Su Zaba?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Zaba

Daga lokacin da aka kada gangar siyasa ta zaben 2023, ‘yan siyasa daga kowace jam’iyya da take da rajista a Nijeriya suka fara baza dabarunsu ta neman kuri’un jama’a domin samun damar darewa madafun iko.

A ‘yan shekarun baya, manyan dabarun da ‘yan siyasar suka fi amfani da su su ne: sayo shinkafa, gishiri, sukari, sabulu, da atamfofi domin rabawa ga jama’a don a zabensu.

  • Hanyoyin Kula Da Fatar Jiki (4)
  • Zamanintarwa Irin Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Shimfida Zaman lafiya Da Kwanciyar Hankalin Duniya

Kan wadannan ‘yan kayayyaki da ba su fi su yi wa mutum mako guda a gidansa ba (kason da aka ba shi) sai a jefa kuri’a ga wanda idan ya ci, ya cika wandonsa da iska ke nan sai kuma wani lokacin zaben bayan wa’adin shekara hudu.

ADVERTISEMENT

Amma ga dukkan alamu a wannan kakar siyasar, dabarun ‘yan siyasar na daukar sabon salo, daga sayen kayan masarufi zuwa bayar da zunzurutun kudi da kuma amfani da yanayin da mutane suka tsinci kansu a ciki wajen kai musu tallafin gaggawa.

A kwanan nan baya ga matsalar tsaro, babu wani abu da ke ci wa jama’a tuwo a kwarya kamar ambaliyar ruwa.

LABARAI MASU NASABA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

Yanzu haka ‘yan siyasa sun yi nisa wajen nuna tausayawa da alhini da kuma bayar da gudunmawa ga jama’ar da ibtila’in ya shafa.

Dama dai tun a farkon daminar bana, hukumar kula da harkokin albarkatun ruwa ta Nijeriya (NIHSA) tare da takwararta ta hasashen yanayi ta NIMET sun yi hasashe cewa za a samu yiwuwar ambaliyar ruwa a kananan hukumomi 23 da ke jihohi 32 har da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Hakan ya kuma faru, wanda ‘yan siyasa suke ta amfani da wadanda ibtila’in ya fada musu wajen tallafa manufofinsu ta siyasa.

‘Yan takara musamman masu neman shugabancin kasa sai kai ziyara inda wannan lamarin ya auku suke tare da bayar da tallafi ga wadanda annobar ta shafa.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben 2023, Asiwaju Bola Tinubu ya ba da tallafin Naira miliyan 50 ga jama’ar da ambaliyar ruwa ta shafa a Jihar Jigawa, ga na baya-bayan nan da ya bayar da Naira milyan100 ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a Kano.

Shi kuwa dan takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar LP, Peter Obi ya ziyarci Jihar Benuwe, inda ya bayar da tallafin Naira miliyan biyar.

Haka kuma ya kai ziyara a Jihar Bayelsa inda ya jajanta masu da nuna jimaminsa kan faruwar lamarin.

Atiku Abubakar da ke neman takarar shugaban kasa a inuwar jam’iyyar PDP shi maya bai wa wadanda ambaliyar ruwa na kasuwar Kantin Kwari da ke Kano tallafin Naira milyan 50.

Na baya-bayan nan kuwa shi ne wanda ya bai wa wadanda ibtila’in ya shafa a Jihar Yobe kayayyakin abinci da sauran wasu abubuwa.

Shi ma dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso yayi nasa kokarin duk da babu wata shaida baro-baroa fili.

Haka abubuwan suke ga kananan ‘yan siyasa masu neman takara a matakin jihohi da tarayya wajen jajanta wa al’ummar da ibtila’in ruwa ta shafa tare da ba su tallafi, wanda ko ba a fada ba, mai hankali ya san don yakin neman zabe suke yi.

Yanzu muna so al’ummar Nijeriya ta yi wa kanta adalci tare da auna wadannan ‘yan takarar guda biyu da za mu kawo a kasa.

Wai da dan takarar da ya ziyarci wadanda ibtila’in ambaliyar ruwa ta shafa, ya tashi takanas-ta-kano ya tafi inda suke ya jajanta musu, har ma saboda tausayi ya zubar da hawaye amma bai ba su kobo ba.

Da kuma dan takarar da shi bai samu ziyartar inda suke ba, amma sai ya aike musu da da makudan kudade da sakon jaje.

Shin wa ya kamata su zaba? Ina fatan wadanda ambaliyar ruwa ta rutsa da su wadanda suka hada da Hausawa da Yarbawa da Inyamurai za su bayar da sakamako iri daya.

Domin, cikin wadannan ‘yan takarar biyu, wanda ya nuna alhini har da sa abin a cikin ransa tare da zubar da hawaye, ana ganin kilazai fi tausaya musu idan ya samu madafun iko, watakila ma ya magance musu abin da ke haddasa ambaliyar har Abadan.

Yayin da wanda ya ba su kudi kuma bai shigar da abin cikin ransa, na iya biris da su saboda ya sallame su tun kafin ya hau mulki.

Siyasar kudi ta riga ta ratsa zukatan ‘Yan Nijeriya da dama wanda shawo kan wannan lamari na da matukar wahalar gaske.

Idan za a iya tunawa, a Shirinmu na Manhajar Podcast na Barka Da Hantsi Nijeriya da muka gabatar a farkon watan Oktoba tare da daya daga cikin dattawan kasa, Dakta Hakeem- Baba Ahmad, ya bayyana hatsarin sayen kuri’u da kuma yadda za a iya samun sahihin zabe a 2023.

Haka ma masu shirhin al’amurar siyasa suna ta kira ga ‘yan Nijeriya da su yi kokarin kauce wa sayar da kuri’unsu ga dukkan wani dan takara, su yi kokarin zaben ‘yan takarar da suka dace.

Wannan ne ya sa kungiyoyin arewa daban-daban suka taru a karkashin inuwa guda suka tattauna da ‘yan takarar domin jin manufofinsu da yadda za a kauce wa fadawa gidan jiya a yankin arewa.

Wani babban abin takaici dai shi ne, yadda ‘yan siyasa ke jan ra’ayoyin mutane da ‘yan kudi kalilan.

Inda a baya suke bayar da kudi daga Naira 10,000 zuwa 5,000, amma a halin yanzu kudin bai wuce dubu daya zuwa biyu, kai akwai ma idan ake bai wa mutum dari biyar ya sayar da ‘yancinsa na tsawon shekaru hudu masu zuwa, kamar yadda aka ga misalign haka a zabukan da aka yi a wasu jihohin kudu a kwanan bayan nan kamar Ekiti da Osun.

Wannan babban abin takaici ne ga al’ummar Nijeriya, musamman a daidai lokacin da abubuwa suka rikice. Ana tunanin babu abinda zai iya sauya matsalolin da suke addabar Nijeriya da kuma ‘yan Nijeriya face shugabanci nagari.

Idan kuwa haka ne, to ya kamata ‘yan Nijeriya su yi karatun ta-natsu wajen sanin dan takarar da za su zaba da zai kawo kyakkyawan shugabanci ba tare da la’akari da kabilanci, addini ko kuma bangarenci.

Yana da matukar muhimmanci ‘yan Nijeriya su guji kwadayin kudaden da ‘yan takara suke ba su wajen zaben shugaba ko wakili da zai jagoranci al’umma na tsawon shekaru hudu.

Sayen kuri’u wajen zaben shugaba ba zai taba haifar wa da al’ummar Nijeriya da mai ido ba,zai ci gaba da jefa kasar da mutanen kasar a cikin mawuyacin hali, baya ga wanda suke fuskanta yanzu haka!

Zaba
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
obi
Bakon Marubuci

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Bakon Marubuci

Hanyoyin Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya

May 10, 2026
Next Post
Wang Yi Ya Gana Da Jakadan Amurka Dake Kasar Sin

Wang Yi Ya Gana Da Jakadan Amurka Dake Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.