ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wane Irin Tanadi Kuka Yi Wa Sallah Karama A Wannan Lokacin?

by Rabi'at Sidi Bala
3 months ago
Sallah

Shafin TASKIRA shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban daban da suka shafi al”umma, cikin sun hadar da; zamantakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya da dai sauransu.

Tsokacinmu na yau zai yi duba game da abin da ya shafi Sallah Karama. Inda shafin ya ji ta bakin wasu daga cikin ma’abota shafin game da wannan batu; “Wane irin tanadi aka yi wa Salllah Karama a wannan lokacin?, A kowacce shekara akan fitar da wasu nau’ikan kaya na sakawa wadanda ake fitar musu da sunaye daban-daban na yayi, shin ko wannan sallar an yi mata tanadin kaya na musamman?, Wacce shawara za a bawa matasa da kuma iyaye game da kayan Sallah, musamman wadanda Allah bai hore musu da kaya me yawa ba?”.

Ga dai bayanan nasu kamar haka:

ADVERTISEMENT

Sunana Badariyya Muhammad, Jihar Kano:

Gaskiya wannan sallar an yi mata tanadi da yawa, musamman kayan adon na mata aka tanada, kamar takalmin da za a yi yayinsa me suna Shafa Wali, sai kuma Hijab me sarka me suna Capacity, sai atamfa me ‘stones’. Kayan da aka tanada kenan a wannan sallah in sha Allah. Sannan ina kira ga ‘yan’uwa mata musamman matasa ‘yan’uwanmu da su rage buri, kuma su yi hakuri da iya abin da iyaye suka yi musu, kada ki ce lallai sai ke ma an yi miki Shafa Wali ko kuma Capacity, ki yi hakuri domin duk kudi gare su ba wai sauki ne da su kamar ruwan sha ba. Abin da Allah ya horewa iyayenka ka yi hakuri da shi, kar ka je kana roko wajen saurayi ko bayar da kai dan neman kudin atamfa me ‘stones’

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

Sunana Abba Abubakar Yakubu, daga Jos, Jihar Filato:

Cikin yardar Allah nan da mako mai zuwa ana shirye-shiryen kammala azumi da gudanar da bikin Sallah Karama. Tun kafin ganin watan Ramadan wasu da dama sun fara shirin tunkarar bikin sallah, musamman wadanda ke fargabar samun akasi daga wajen tela. Shi ya sa mako guda da shigar azumi har wasu teloli na cewa sun rufe karbar dinkin sallah, sai na idon kunya. Saboda yadda aka yi gaggawar kai dinkuna da wuri. Kamar yadda yake bisa al’ada kowacce shekara ba a rasa irin salon dinki ko kayan da za a ce akwai yiwuwar za a yi yayinsu a bana, musamman ga yara da mata. Manya ma suna da irin nasu kayan da ake sa ran ganin su da yawa a jikin mutane, kamar dinkin yadi da babbar riga mai aikin zare na zamani. Su kuma mata dogayen riguna na Abaya da hijabai masu salon dinki daban-daban. Nasihata ga ‘yan’uwa musulmi maza da mata shi ne, kada a tsawwala wa kai, ko a yi buri fiye da abin da Allah ya hore mana. A yi dinki na mutunci, tarbiyya da tsare al’ada. Kuma a guji matsawa har a ciwo bashi don a yi irin dinkin wance ko gyaran jiki irin na wance ba. A yi shirin sallah daidai misali. Kadaran Kadahan!

Sunana Hassana Iyayi Yahaya (Maman Noor), daga Jihar Kano:

Allah ya kai mu lafiya shi ne babban tanadin, Hmmm Aikuwa wannan shekarar an fitar kala-kala ma kuwa sai fatan Allah hore abin siya. Wanda Allah bai hore ba a wanke na Bara a saka shi ne lafiya lau.

Sunana Aminu Adamu, Malam Madori, A Jihar Jigawa:

To magana ta gaskiya al’amarin sallah a wannan shekara sai mu ce Alhamdullilah, domin hidimar sallah daidai gwargwado mun yi muna kuma kan yi har zuwa lokacin sallah. To, magana sutura ta yayi ko akwai ta ma domin ni shadda nafi amfani da ita musamman lokacin bukukuwan sallah dama bukukuwan aure ko suna, don mu shadda ce adon mu na sallah insha’Allah. To, shawarata a nan ita ce ya kamata mutum yayi amfani da irin damar da yake da ita kada yayi gasa ko koyi da wani wanda yafi karfin sa wajen gudanar da hidimar sallah, kuma mu dage da yi wa kasar mu Najeriya addu’ar samun zaman lafiya a wannan kwanaki masu albarka.

Sunana Sadiya Abubakar Maru, daga Gombe:

Ba a rasa nono a riga, wannan abu ne da kowa ya sani tun fil azal. Al’umma sun fara tanadin sallar bana tun da wuri ta hanyar sayen kayan sawa da kuma bada dinki da wuri domin gudun samun matsala daga wajen tela. Shekarar bana ma ta zo da sabon salo kamar yadda aka saba a kowace sallah. Kamar yadda yake yawo a kafafen sada zumunda, akwai hijaabi mai capacity, takalmin shafa wali, da zani mai ‘stone’ wanda mutane da dama ke nema ido rufe. Shawarata ita ce kowa ya daga hannu ya kalli yatsun hannunsa, zai ga ba daidai suke ba. Wannan yana nuni da cewa daidai ruwa daidai gari. Kada a takura kai wajen yin abin da karfin mutum bai kai ba, ayi mika daidai da abun rufa. Idan Allah ya hore miki ki yi, idan bai hore miki ba kada a duma kai.

Sunana Muhammad Isah, Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Sallar Bana Alhamdulillahi domin ta zo cikin saukin tsadar rayuwa. Saboda kayan abinci ya zo da dan sauki. Eh a Bana mata a garin mu sun fi yin Ankon LESHI DA SHADDA SHAMPOO. Shawara da zan bawa matasa  da ma iyaye shi ne su tuna idan bana Allah bai hore miki ba to, a baya ai an yi sabbin kaya kala-kala a saka hakuri idan Allah ya so nan gaba sai a dinka sabbin kaya. A samu mai kyau a saka a tafi masallacin Idi.

Sallah
Rabi'at Sidi Bala
+ postsBio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Maniyyatan Nijeriya
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
'Yan Bindiga
Manyan Labarai

Yan Bindiga Sun Kashe Manoma Shida A Birnin Gwari Ta Jihar Kaduna

June 23, 2026
Next Post
Tun Ina Karama Nake Sha’awar Harkar Wasan Kwaikwayo —Fartima Hamza

Tun Ina Karama Nake Sha'awar Harkar Wasan Kwaikwayo —Fartima Hamza

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

An Kashe Mutum 2, Takwas Sun Jikkata Yayin Rikicin A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.