ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kashe Dan Uwansa Saboda Kin Ba Da Gudunmawar Naira 1,000

by Leadership Hausa
9 months ago

Taron iyali ya rikide zuwa mummunan lamari a Jihar Delta, bayan wani mutum mai shekaru 47 ya kashe dan uwansa na farko, bisa zargin rikici mai zafi kan dowo masa da Naira 1,000.

Lamarin, wanda ya faru a ranar 12 ga Disamba, 2025, a Karamar Hukumar Ughelli South, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Delta, SP Edafe Bright, ne ya tabbatar da haka a wani bidiyo da aka wallafa a shafin D ranar Litinin.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Ta Farko Game Da Tattalin Arziki Mai Alaka Da Yanayin Duniyarmu
  • An Yi Matukar Inganta Harkokin Sadarwa A Kasar Sin Cikin Shekaru Biyar Da Suka Wuce

A cewar Edafe, iyalin sun dawo ne daga jana’izar wani daga cikin danginsu, sannan suka zauna domin yin taron iyali.

ADVERTISEMENT

Sai dai yanayin ya lalace lokacin da aka samu sabani kan dawo gudummawar Naira 1,000.

Edafe ya ce: “Wannan matashin yana ta ja da rigima, yana tayar da hayaniya yana cewa dole sai an mayar masa da 1,000 dinsa.”

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Ya ci gaba da cewa, “A yayin jan-rigimar, ya fara fada. A wani lokaci, a cewarsa, yayin da yake kokarin kubuta daga fadan, sai ya yi amfani da hannunsa ya bugi daya daga cikin ‘yan uwansa, wanda daga bisani ya rasu.

“Yanzu ga shi, gardamar Naira 1,000 ta kai ga mutuwar wani dan uwa. An rika gargadinsa har ma da wannan mutumin da daga karshe ya rasu.

“Ruhin da ya shiga jikinsa, a cewarsa, bai bar shi ya saurari ‘yan uwansa ba. Mutumin da ya mutu yana da shekaru 42, ya mutu kawai saboda Naira 1,000.”

Wanda ake zargin, mai suna Ezekiel, mai shekaru 47, ya nuna nadama yayin da yake magana, tare da ikirarin cewa mutuwar hatsari ce.

Ya amince cewa ‘yan uwa da dama, ciki har da mamacin, sun roke shi da ya kwantar da hankalinsa. “Kuskure ne. Ban ma san lokacin da na buge shi ba,” in ji shi.

Ezekiel ya bayyana cewa kudin Naira 1,000 da ake magana a kai gudummawa ce da aka bayar domin bukukuwan jana’iza, wadda bisa al’ada ake mayar wa mai ita bayan an kammala jana’izar.

“Bayan an kammala komai, sukan raba kudin. Haka ne muke mayar wa mai kudin nasa,” in ji shi.

Edafe ya yi amfani da faruwar wannan mummunan lamari wajen kira ga jama’a da su kame zuciya, ko da a lokacin kananan abubuwan da ke tayar da hankali.

“Nawa kawai shi ne in yi magana da masu sauraronmu su fahimci muhimmancin sarrafa fushi. Dole ne ku kwantar da hankali. Duk wani nau’in fada na iya kai wa ga mutuwa. Zai iya zama kisan kai ba da gangan ba. Zai iya zama kisan kai. Don Allah, magana kadan ta isa ga mai hikima. Rigakafi ya fi magani,” Edafe ya kammala.

Jaridar PUNCH ta ruwaito a shekarar 2023 cewa wani mutum mai suna Ibrahim Dauda ya kashe dan uwansa, Tunde, bisa zargin rikici kan Naira 1,000, a gidansu da ke yankin Igando na Jihar Lagos.

A baya-bayan nan, a watan Satumba, rundunar ‘yansandan Jihar Anambra ta kama wani mai suna Okwuchukwu Ezimuo bisa zargin soka wa dan uwansa wuka har ya mutu, sakamakon rikicin filin iyali a Karamar Hukumar Idemili South ta jihar.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Mutane 7 Sun Mutu, 4 Sun Jikkata A Mummunan Hatsarin Mota A Yobe

Mutane 7 Sun Mutu, 4 Sun Jikkata A Mummunan Hatsarin Mota A Yobe

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.