ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kashe Dan Uwansa Saboda Kin Ba Da Gudunmawar Naira 1,000

by Leadership Hausa
6 months ago

Taron iyali ya rikide zuwa mummunan lamari a Jihar Delta, bayan wani mutum mai shekaru 47 ya kashe dan uwansa na farko, bisa zargin rikici mai zafi kan dowo masa da Naira 1,000.

Lamarin, wanda ya faru a ranar 12 ga Disamba, 2025, a Karamar Hukumar Ughelli South, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Delta, SP Edafe Bright, ne ya tabbatar da haka a wani bidiyo da aka wallafa a shafin D ranar Litinin.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Ta Farko Game Da Tattalin Arziki Mai Alaka Da Yanayin Duniyarmu
  • An Yi Matukar Inganta Harkokin Sadarwa A Kasar Sin Cikin Shekaru Biyar Da Suka Wuce

A cewar Edafe, iyalin sun dawo ne daga jana’izar wani daga cikin danginsu, sannan suka zauna domin yin taron iyali.

ADVERTISEMENT

Sai dai yanayin ya lalace lokacin da aka samu sabani kan dawo gudummawar Naira 1,000.

Edafe ya ce: “Wannan matashin yana ta ja da rigima, yana tayar da hayaniya yana cewa dole sai an mayar masa da 1,000 dinsa.”

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

Ya ci gaba da cewa, “A yayin jan-rigimar, ya fara fada. A wani lokaci, a cewarsa, yayin da yake kokarin kubuta daga fadan, sai ya yi amfani da hannunsa ya bugi daya daga cikin ‘yan uwansa, wanda daga bisani ya rasu.

“Yanzu ga shi, gardamar Naira 1,000 ta kai ga mutuwar wani dan uwa. An rika gargadinsa har ma da wannan mutumin da daga karshe ya rasu.

“Ruhin da ya shiga jikinsa, a cewarsa, bai bar shi ya saurari ‘yan uwansa ba. Mutumin da ya mutu yana da shekaru 42, ya mutu kawai saboda Naira 1,000.”

Wanda ake zargin, mai suna Ezekiel, mai shekaru 47, ya nuna nadama yayin da yake magana, tare da ikirarin cewa mutuwar hatsari ce.

Ya amince cewa ‘yan uwa da dama, ciki har da mamacin, sun roke shi da ya kwantar da hankalinsa. “Kuskure ne. Ban ma san lokacin da na buge shi ba,” in ji shi.

Ezekiel ya bayyana cewa kudin Naira 1,000 da ake magana a kai gudummawa ce da aka bayar domin bukukuwan jana’iza, wadda bisa al’ada ake mayar wa mai ita bayan an kammala jana’izar.

“Bayan an kammala komai, sukan raba kudin. Haka ne muke mayar wa mai kudin nasa,” in ji shi.

Edafe ya yi amfani da faruwar wannan mummunan lamari wajen kira ga jama’a da su kame zuciya, ko da a lokacin kananan abubuwan da ke tayar da hankali.

“Nawa kawai shi ne in yi magana da masu sauraronmu su fahimci muhimmancin sarrafa fushi. Dole ne ku kwantar da hankali. Duk wani nau’in fada na iya kai wa ga mutuwa. Zai iya zama kisan kai ba da gangan ba. Zai iya zama kisan kai. Don Allah, magana kadan ta isa ga mai hikima. Rigakafi ya fi magani,” Edafe ya kammala.

Jaridar PUNCH ta ruwaito a shekarar 2023 cewa wani mutum mai suna Ibrahim Dauda ya kashe dan uwansa, Tunde, bisa zargin rikici kan Naira 1,000, a gidansu da ke yankin Igando na Jihar Lagos.

A baya-bayan nan, a watan Satumba, rundunar ‘yansandan Jihar Anambra ta kama wani mai suna Okwuchukwu Ezimuo bisa zargin soka wa dan uwansa wuka har ya mutu, sakamakon rikicin filin iyali a Karamar Hukumar Idemili South ta jihar.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Mutane 7 Sun Mutu, 4 Sun Jikkata A Mummunan Hatsarin Mota A Yobe

Mutane 7 Sun Mutu, 4 Sun Jikkata A Mummunan Hatsarin Mota A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026
Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

Har Yanzu Ba Mu Karɓi Kuɗaɗen Da Aka Ware Mana Na Zaɓukan 2027 Ba – INEC

June 26, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

June 26, 2026
Noma

Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba

June 26, 2026
Darussan Da Suka Fi Dacewa A Fahimta Daga Alkur’ani A Wannan Zamanin (2)

Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)

June 26, 2026
Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutuwar Ɗaliba A Wata Sakandiren Kano

June 26, 2026
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.