ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kashe Dan Uwansa Saboda Kin Ba Da Gudunmawar Naira 1,000

by Leadership Hausa
5 months ago

Taron iyali ya rikide zuwa mummunan lamari a Jihar Delta, bayan wani mutum mai shekaru 47 ya kashe dan uwansa na farko, bisa zargin rikici mai zafi kan dowo masa da Naira 1,000.

Lamarin, wanda ya faru a ranar 12 ga Disamba, 2025, a Karamar Hukumar Ughelli South, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Delta, SP Edafe Bright, ne ya tabbatar da haka a wani bidiyo da aka wallafa a shafin D ranar Litinin.

  • Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Ta Farko Game Da Tattalin Arziki Mai Alaka Da Yanayin Duniyarmu
  • An Yi Matukar Inganta Harkokin Sadarwa A Kasar Sin Cikin Shekaru Biyar Da Suka Wuce

A cewar Edafe, iyalin sun dawo ne daga jana’izar wani daga cikin danginsu, sannan suka zauna domin yin taron iyali.

ADVERTISEMENT

Sai dai yanayin ya lalace lokacin da aka samu sabani kan dawo gudummawar Naira 1,000.

Edafe ya ce: “Wannan matashin yana ta ja da rigima, yana tayar da hayaniya yana cewa dole sai an mayar masa da 1,000 dinsa.”

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

Ya ci gaba da cewa, “A yayin jan-rigimar, ya fara fada. A wani lokaci, a cewarsa, yayin da yake kokarin kubuta daga fadan, sai ya yi amfani da hannunsa ya bugi daya daga cikin ‘yan uwansa, wanda daga bisani ya rasu.

“Yanzu ga shi, gardamar Naira 1,000 ta kai ga mutuwar wani dan uwa. An rika gargadinsa har ma da wannan mutumin da daga karshe ya rasu.

“Ruhin da ya shiga jikinsa, a cewarsa, bai bar shi ya saurari ‘yan uwansa ba. Mutumin da ya mutu yana da shekaru 42, ya mutu kawai saboda Naira 1,000.”

Wanda ake zargin, mai suna Ezekiel, mai shekaru 47, ya nuna nadama yayin da yake magana, tare da ikirarin cewa mutuwar hatsari ce.

Ya amince cewa ‘yan uwa da dama, ciki har da mamacin, sun roke shi da ya kwantar da hankalinsa. “Kuskure ne. Ban ma san lokacin da na buge shi ba,” in ji shi.

Ezekiel ya bayyana cewa kudin Naira 1,000 da ake magana a kai gudummawa ce da aka bayar domin bukukuwan jana’iza, wadda bisa al’ada ake mayar wa mai ita bayan an kammala jana’izar.

“Bayan an kammala komai, sukan raba kudin. Haka ne muke mayar wa mai kudin nasa,” in ji shi.

Edafe ya yi amfani da faruwar wannan mummunan lamari wajen kira ga jama’a da su kame zuciya, ko da a lokacin kananan abubuwan da ke tayar da hankali.

“Nawa kawai shi ne in yi magana da masu sauraronmu su fahimci muhimmancin sarrafa fushi. Dole ne ku kwantar da hankali. Duk wani nau’in fada na iya kai wa ga mutuwa. Zai iya zama kisan kai ba da gangan ba. Zai iya zama kisan kai. Don Allah, magana kadan ta isa ga mai hikima. Rigakafi ya fi magani,” Edafe ya kammala.

Jaridar PUNCH ta ruwaito a shekarar 2023 cewa wani mutum mai suna Ibrahim Dauda ya kashe dan uwansa, Tunde, bisa zargin rikici kan Naira 1,000, a gidansu da ke yankin Igando na Jihar Lagos.

A baya-bayan nan, a watan Satumba, rundunar ‘yansandan Jihar Anambra ta kama wani mai suna Okwuchukwu Ezimuo bisa zargin soka wa dan uwansa wuka har ya mutu, sakamakon rikicin filin iyali a Karamar Hukumar Idemili South ta jihar.

Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Mutane 7 Sun Mutu, 4 Sun Jikkata A Mummunan Hatsarin Mota A Yobe

Mutane 7 Sun Mutu, 4 Sun Jikkata A Mummunan Hatsarin Mota A Yobe

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.