ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Cacar Zamani Ke Tatike Matasan Arewacin Nijeriya

by Bello Hamza
4 months ago
Cacar

Caca wata matsala ce da ta dade a tsakanin al’ummar arewacin Nijeriya, a shekarun baya matasa da magindata aka fi samu a wararen caca inda ake amfani da karta wajen gudanar da ita. A lokutta da dama zaka samu an tatike mutun tun daga kudaden da yake dauke da su har zuwa kayan da ya sa a jikinsa. Duk da haramcin da addini da al’ada suka yi ga aikata caca har zuwa yanzu an kasa samo hanyoyin kawo karshen wannan mummunan lamarin, musamman saboda yadda kamfanonin gudanar da cacar a wanna lokacin suka fito da wasu hanyoyi daban-daban da suka yi daidai da wannan zamanin wajen yaudarar matasa wajen shiga harkar cacar.

A wannan lokacin harkar caca na kara bazuwa sako da lungunan arewacin Nijeriya ne saboda wasu dalilai da masana suka bayyana kamar haka- na daya shi ne matsanancin matsalar tattalin arziki da ya addabi al’umma sun kuma kasa jurewa tare da fuskantar yadda za su fitar da kansu daga matsalar. Sai kuma ci gaba da aka samu na kimiyya da fasaha musamman bayyanar wayoyin hannu da hanyoyin sarrafata, sai kuma yadda aka samu guguwar son kallon kafa musamman wadanda ake gudanarwa a kasasshen Turai. A halin yanzu lamarin caca a tsakanin matasa ya bunkasa duk kuwa da kyamarta da ake a arewacin Nijeriya saboda haramcin addini da al’ada, haka ya sa lamarin ya fi bunkasa a kudancin kasar nan amma a yanzu caca a tsakanin matasanmu na arewa ya kai kashi 40 a cikin dari yayin a kudacin kasa suke da kashi 60.

  • Cinikayyar Waje Ta Jihar Xinjiang Ta Bunkasa A Shekarar 2025
  • Akpabio: Ba A Canza Komai A Cikin Sabbin Dokokin Haraji Ba 

A bayyane lamarin yake cewa, arewacin Nijeriya na fuskantar matsanancin talauci da tsananin rashin aikin yi a tsakanin matasa abin da yake tunzura matasa yin hijira biranen kudancin Nijerira donmin neman aikin yi, daga nan ne kuma wasu da yawa a cikin su ke koyo wasu muggan dabi’u wadanda suka hada da caca An kiyasta cewa, lamarin talauci ya kai kashi 77.7 a yankin arewa maso yammacin kasa, abin da ke tunzura wasu matasan fadawa harkar caca domin su samu tsira da mutumci daga sharrin talauci da hauhawar farashin kayayyakin amfani na yau da kullum.

ADVERTISEMENT

Bazuwar wayoyin hannu da aka fi sani da ‘Smart phone’ ya taimaka wajen bazuwar caca a tsakanin matasa, a yanzu mutum zai iya ci gaba da harkar cacarsa ba tare da kowa ya sani ba musamman a wuraren babu shagunan cacar da wuraren da ake nuna kyama ga masu caca da kuma wuraren da aka haramta cacar gaba daya. Sai ya zamana kana tare da mutum na tsawon lokaci amma baka san ya yi nisa a harkar caca ba. A kan haka a halin yanzu wasu kasashe ke kafa dokar kayyade shekarun sake wa yara masu tasowa mallakar wayar hannu tare da kuma sanya ido a kan yadda suke amfani da ita.

Tasirin kallon kwallon kafa musamman wadanda ke gudana a kasashen Tura da aka fi sani da ‘English Premier League’ ya zama dandamali na tarkon kamo matasa da shigar da su harkar caca ba tare da makusantar su sun sani ba. Da yawa daga cikin su sun yi imanin cewa, sanin su na yadda ake gudanar da harkar kwallon da sanin sanin su na shahararrun ‘yan wasan yana taimaka musu wajen samun nasara a cacar da suke yi. Sai dai abin takaicin shi ne har yanzu sun kasa fahimta tare da nuna wani na kusa da su da rayuwarsa ta canza saboda ya ci wasu makudan kudade ta hanyar cacar.

LABARAI MASU NASABA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

Wani abin da ke ingiza matasanmu fadawa harkar caca a wannan lokacin shi ne yadda kamfanonin cacar ke amfanbi da wasu fitattaun mutane a cikin al’umma wajen tallar nau’o’in caca daban-daban domin yaudarar matasa. Suna kuma amfani da fitattaun ‘yan kwallon kafa da fitattun mawaka wajen wannna aiki na tallata cacar.

A jihohin arewacin Nijeriya kamar Kano inda shari’a musulunci ta haramta caca a hukumance tun a shekarar 2000, gwamnati ta kara samamen da take kai wa shagunan caca a sassan jihar amma duk da haka harkar caca na ci gaba da bunkasa a sassan kasar baki daya inda aka kiyasta ana samun abin da ya kai Dala Biliyan 3.63 (fiye da Naira tiriliyan 5.6) kamar yadda kididdigar ya nuna a karshen shekarar 2025.

Wani abin da ke daure kai a lamarin cacar nan shi ne yadda yake ninka halin talaucin da masu mu’amala da ita ke ciki maimakon ya yi musu maganin talauci, wannan na faruwa ne saboda yawancinh matasan da ke harkar cacar sukan yi amfani ne da kudaden wasu harkoki ne na rayuwarsu kamar kudin makaranta da saurancu abin da ke jefa su cikin matsanancin bashi hakan kuma zai iya kaisu ga sayar da wasu kayyakin su da wanda bama nasu ba, in abin ya yi kamari yakan kaisu ga sace-sace da shiga wasu kungiyoyin ta’addanci. Bincike ya nuna cewa, harkar caca ta bayar da gummawa wajen matsalar tsaro da ake fuskanta a sassan arewacin Nijeriya.

Haka kuma an gano cewa, wadanda suka yi nisa a harkar caca suna fuskantar matsalar kwakwalwa saboda asarar da suke tafkawa wanda a lokutta dama yake kai wa ga kashe kai (suicide) da kuma yunkurin kisan kai a lokutta da dama. Harkar caca ta lalata rayuwar matasanmu ta fannoni da dama, ‘yan makaranta kan yi watsi da karatu.

A kan haka ya kamata gwamnati, iyaye da masu fada a ji a cikin al’umma su hada hannu wajen dakile yawaitar gidajen caca a garuruwanmu. Dole iyaye su kara sanya ido a kan yadda yaransu ke amfani da wayoyin hannu da kuma irin abokan da suke mu’amala da su. Allah ya shriya mana zuri’a.

Cacar
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1
Bakon Marubuci

Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 1

May 27, 2026
obi
Bakon Marubuci

Su Wa Ke Fatattakar Obi Da Kwankwaso?

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Bakon Marubuci

Hanyoyin Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya

May 10, 2026
Next Post
Gwamnan Zamfara Ya Yaba Da Gudumawar Ɗan Majalisa Hon. Mai Palace A Bangaren Kiwon Lafiya

Gwamnan Zamfara Ya Yaba Da Gudumawar Ɗan Majalisa Hon. Mai Palace A Bangaren Kiwon Lafiya

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.