• English
  • Business News
Thursday, July 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gasar Firimiyar Bana Ta Shammaci Mutane

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Yadda Gasar Firimiyar Bana Ta Shammaci Mutane
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Za a iya cewa gasar firimiya ta kasar Ingila ta shammaci mutane musamman wadanda suke ganin wasu kungiyoyin kawai rakiya za su yi, yayin da ake ganin wadanda za su tabuka abin a zo a gani kuma suke tafiyar biri a yashi.

Kungiyar kwallon kafa ta Tottenham ce kungiyar da aka fara yi wa kallon wadda babu abin da za ta yi sai rakiya kawai, ganin yadda dab da za a fara gasar ta sayar da babban dan wasanta, Harry Kane, wanda ya koma kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen akan zunzurutun kudi yuro miliyan 100 tare da tsarabe-tsarabe.

  • Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa
  • Arsenal Ta Koma Ta Daya A Rukunin B, Bayan Doke Sevilla A Champions League

Harry Kane ya kasance kyaftin din kungiyar ta Birnin Landan kuma shi ne jagoran kungiyar musamman wajen zura kwallo a raga, sai dai tafiyar dan wasan ta saka shakku akan hasashen da ake yin a cewa ko Tottenham za ta yi abin a zo a gani ko kuma akasin haka.

Sai dai bayan fara kakar wasa ta bana kungiyar kwallon kafa ta Tottenham ta yi abin a zo a gani a karkashin sabon kociyan ta, Ange Postocoglo, wanda ya ja ragamar kungiyar wajen buga wasa mai kyau tare da lashe wasanni da dama.

Kawo yanzu Tottenham ta buga wasanni 12 tana mataki na hudu da maki 26 kuma wasanni biyu kacal ta yi rashin nasara a wannan kakar su ne wasan da ta yi rashin nasara a hannun Chelsea da ci 4-1 har gida sai kuma wanda Wolbes ta doke ta da ci 2-1 kafin a tafi hutu.

Labarai Masu Nasaba

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

Ita ma kungiyar kwallon kafa ta Manchester United za a iya cewa ta ba wa duniya mamaki bayan da tun kafin a fara kakar wasan ake ganin a wannan lokacin za ta tabuka abin a zo a gani musamman ma ganin ta sayi sabon mai tsaron raga Andre Onana da dan wasa Mason Mount da dan wasan gaba Rasmus Hojlund da kuma karbo aron dan wasa Sofyan Amrabat daga kungiyar Fiorantina ta kasar Italiya.

An yi tunanin Manchester United za ta kasance a ‘yan gaba-gaba wajen neman lashe gasar firimiyar Ingila a wannan kakar sai gashi kungiyar tana fama da kanta inda a yanzu take mataki na shida akan teburin gasar da maki 21 cikin wasanni 12 da ta fafata a kakar ta bana.

Kociyan kungiyar, Erik ten Hah yana fuskantar matsin lamba daga bangaren wasu daga cikin magoya bayan kungiyar da masu sharhi akan kwallon kafa a fadin duniya da kuma ‘yan jarida ganin gazawar kungiyar wajen buga wasa mai kyau mai kayatarwa.

Liverpool, ita ma da farko an yi hasashen za ta sha wahala a kakar bana ganin yadda ta sayar da ‘yan wasanta da dama irin su Sadio Mane da Jordan Henderson da Fabinho da Firminho da sauransu.

Ana ganin ‘yan wasan kwararru ne wajen taimakawa kungiyar wajen lashe wasa kuma a lokaci guda ta sayar da su ta dauki sababbin ‘yan wasa wadanda ake ganin za su dauki lokaci kafin su gano yadda ake buga wasa a kungiyar.

Amma kuma salon yadda Liverpool din take buga wasa shima ya ba wa masu kallo mamaki domin babu wanda ya yi hasashen kungiyar za ta yi irin kokarin da take yi a yanzu duk da cewa ‘yan wasa irinsu Muhammad Salah har yanzu suna kan ganiyarsu.

Yanzu Liverpool tana mataki na biyu da maki 27 cikin wasanni 12 da kungiyar ta fafata kuma a wasa na gaba kungiyar za ta kece raini da wadda take mataki na daya, wato Manchester City a filin wasa na Ettihad dake Birnin Manchester.

Manchester City daman tana daya daga cikin kungiyoyin da za su buga abin a zo a gani a wannan kakar ganin yadda a kakar da ta gabata kungiyar ta lashe kofuna uku rigis da suka hada da gasar firimiya da kofin kalubale na FA da kuma gasar cin kofin zakarun turai wanda ta doke Inter Milan a wasan karshe.

Amma kuma kungiyara ta saki wasu zakakuran ‘yan wasanta da suka hada da Riyadh Mahrez da Ilkay Gundogan, sannan kuma dan wasa Kebin De Bruyne ya tafi doguwar jiyya tun a wasan farko na fara gasar firimiya hakan ya sa aka yi hasashen kungiyar za ta sha wahala wajen kare kambunta na bana.

Sai gashi kawo yanzu tana mataki na daya bayan ta buga wasanni 12 kuma tana da maki 28 sannan kungiyar tana buga wasa mai kyau tun da ta sayi sababbin ‘yan wasa musamman Jeremy Doku da ta saya dan Belgium.

Ita daman kungiyar kwallon kafa ta Arsenal anyi hasashen za ta tabuka abin a zo a gani domin a kakar da ta gabata sai a wasannin karshe ta barar da damar lashe gasar firimiyar kuma a wannan kakar kungiyar ta yi sayayya mai kyau a kasuwa musamman ta dan wasa Declan Rice da kungiyar ta saya daga West Ham United akan kudi fam miliyan 115, wanda ake ganin ya yi tsada da yawa.

Amma irin yadda ya karawa kungiyar karfi ya sa ake ganin tabbas kociyan kungiyar Mikel Arteta yayi tunani wajen tilasta shugabannin kungiyar su sayi dan wasan a wannan kudin domin kwalliya tana biyan kudin sabulu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ChelseaFirimiyar IngilaLiverpool
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masana Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Karkashin BRI Domin Bunkasa Ayyukan Masana’antu A Nahiyar Afrika

Next Post

Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-7 Na Kasar Sin Ya Isa Tashar Harba Kumbuna Ta Kasar

Related

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

43 minutes ago
Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique
Wasanni

Wasanmu Da Real Madrid Zai Kasance Na Musamman – Luis Enrique

1 day ago
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense
Wasanni

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

2 days ago
Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars
Wasanni

Ahmed Musa Ya Ƙaryata Kyautar Motoci Ga Ƴan Wasa Da Ma’aikatan Kano Pillars

2 days ago
Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Yi Ƙoƙarin Dawo Da Martabar Kano Pillars A Idon Duniya — Ahmed Musa

2 days ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin
Wasanni

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

3 days ago
Next Post
Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-7 Na Kasar Sin Ya Isa Tashar Harba Kumbuna Ta Kasar

Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-7 Na Kasar Sin Ya Isa Tashar Harba Kumbuna Ta Kasar

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.