ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tarayya Za Ta Habaka Fannin Aikin Noma A 2026 —Kwararru

by Abubakar Abba
5 months ago
Gwamnatin

Yanayin noma a shekarar 2026, ya ta’allaka da irin mayar da hankalin da gwamnatin tarayya za ta yi, wajen kawo karshen manyan matsalolin da manoman kasar nan ke ci gaba da fuskanta, musamman duba da cewa; fannin na bayar da gagarumar gudunmawa, wajen samar da wadataccen abinci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin wannan kasa.

Hakan ne ya sanya, Jaridar BusinessDay, ta tattauna da wasu kwararru a fannin, inda suke yi karin haske a kan abubuwan da  suka kamata gwamnatin ta mayar da hankali a kansu, domin habaka fannin na noma.

  • Jakadan Sin: Cudanyar Al’adu Za Ta Taimaki Yunkurin Daidaita Hulda Tsakanin Sin Da Amurka
  • Gobara Ta Hallaka Mutum 2, Ta Lalata Dukiya Ta Biliyan 1.59 A Bauchi

Masanan sun bayyana cewa, fannin na noman kasar, zai kara bunkasa ne kadai idan gwamnatin ta mayar da hankali wajen magance kalubalen rashin tsaro da samar wa da manoman tallafi da tabbatar da ganin ana yin noman har zuwa karshen shekara da kuma gayyato musu ruwa da tsaki a cikin fannin da samar masu da kayan aikin noma da sauransu.

Sama Musu Kayan Aiki A Farashi Mai Sauki:

Tsadar farashin kayan aikin noma, na daya daga cikin kalubalen da manoman kasar ke ci gaba da fuskanta, wanda kuma hakan ke ci gaba zama barazana ga sana’ar ta manoman da kuma shafar jarinsu..

Kazalika, wadannan matsaloli a shekarar 2025, sun haifar da karancin abinci a kasar tare da kuma haifar da hauhawar farashin kayan abinci da kuma dakile ribar da ya kamata manoman su samu.

Nijeriya dai, ta dogara ne a kan shigo da kayan abinci daga waje, musamman domin cike gibin da ake da shi na abinci a cikin kasar.

Bisa wasu alkaluma da cibiyar kididdiga ta kasa, wato NBS ta fitar, sun suna cewa; jimillar kayan abinci na naira tiriliyan 3.34, aka shigo da su cikin kasar nan daga watan Janairu zuwa na Satumbar 2025, wanda ya karu da kashi 23 cikin 100.

Manoman kasar, na ci gaba da kokawa kan yadda ake shigo da kayan abinci da rage samar da ayyukan yi ga fannin,” a cewarsa.

Magance Kalubalen Tabarbarewar  Rashin Tsaro:

An shafe shekaru uku, fannin aikin noma na kasar nan na fuskantar matsalar sauyin yanayi.

Kazalika, akwai batun karancin ruwan sama da ambaliyar ruwan sama da ke shafar fannin, wanda hakan ke haifar da asarar biliyoyin nairori na jarin da manoman suka zuba a sana’ar tasu, musamman a Arewacin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, wasu alkaluma da hukumar kasa da kasa da ke sanya ido kan afkuwar annoba, sun nuna cewa; a shekarar 2022 jimillar mutane miliyan 21.9 sauyin yanayi ya shafa a kasar, wanda hakan ya haifar da mutuwar mutane 603 da kuma asarar da ta kai ta dala biliyan 4.2 daidai da naira biliyan 1.6.

Shi kuwa, shugaban kungiyar masu sarrafa takin zamani na gargajiya na kasa, Jude Obi ya sanar da cewa; tsananin zafin yanayi na shafar amfanin gona.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Karfafa Wa Manoma Gwiwa Don Yin Noma Har Zuwa Karshen Shekara:

Za a iya cimma hakan, idan har an samar wa da manoman kayan aikin noma na rani, musamman duba da yadda a duk shekara ake samun raguwar aikin noma a duk shekara, wanda hakan kuma ke shafar kudin shiga da manoman ke samu.

Hasashen da hukumar kula da ssmar da abinci ta duniya (FAO) a shekarar 2050 ta yi, ta ce yawan ruwan da duniya ke bukata, zai karu da kashi 50.

Bugu da kari, domin samun damar iya ciyar da yawan al’ummar kasar nan da abinci, akwai bukatar gwamnatin tarayya, ta samar da kyakkyawan yanayi ga manoman kasar, musamman ta hanyar samar musu da kayan aikin noma na rani, domin su kara habaka sana’ar tasu.

“Domin dawo da kima da kuma martabar aikin noma a kasar nan, ya zama wajibi gwamnatin tarayya, ta samar wa da manoman kayan aikin noma na zamani” in ji shugaban kungiyar manoma ta kasa, Ibrahim Kabir.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Har Yanzu Ba Mu Fitar da Rai Kan Samun Tikitin Kofin Duniya Ba — NFF

Har Yanzu Ba Mu Fitar da Rai Kan Samun Tikitin Kofin Duniya Ba — NFF

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.