ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tarayya Za Ta Habaka Fannin Aikin Noma A 2026 —Kwararru

by Abubakar Abba
5 months ago
Gwamnatin

Yanayin noma a shekarar 2026, ya ta’allaka da irin mayar da hankalin da gwamnatin tarayya za ta yi, wajen kawo karshen manyan matsalolin da manoman kasar nan ke ci gaba da fuskanta, musamman duba da cewa; fannin na bayar da gagarumar gudunmawa, wajen samar da wadataccen abinci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin wannan kasa.

Hakan ne ya sanya, Jaridar BusinessDay, ta tattauna da wasu kwararru a fannin, inda suke yi karin haske a kan abubuwan da  suka kamata gwamnatin ta mayar da hankali a kansu, domin habaka fannin na noma.

  • Jakadan Sin: Cudanyar Al’adu Za Ta Taimaki Yunkurin Daidaita Hulda Tsakanin Sin Da Amurka
  • Gobara Ta Hallaka Mutum 2, Ta Lalata Dukiya Ta Biliyan 1.59 A Bauchi

Masanan sun bayyana cewa, fannin na noman kasar, zai kara bunkasa ne kadai idan gwamnatin ta mayar da hankali wajen magance kalubalen rashin tsaro da samar wa da manoman tallafi da tabbatar da ganin ana yin noman har zuwa karshen shekara da kuma gayyato musu ruwa da tsaki a cikin fannin da samar masu da kayan aikin noma da sauransu.

Sama Musu Kayan Aiki A Farashi Mai Sauki:

Tsadar farashin kayan aikin noma, na daya daga cikin kalubalen da manoman kasar ke ci gaba da fuskanta, wanda kuma hakan ke ci gaba zama barazana ga sana’ar ta manoman da kuma shafar jarinsu..

Kazalika, wadannan matsaloli a shekarar 2025, sun haifar da karancin abinci a kasar tare da kuma haifar da hauhawar farashin kayan abinci da kuma dakile ribar da ya kamata manoman su samu.

Nijeriya dai, ta dogara ne a kan shigo da kayan abinci daga waje, musamman domin cike gibin da ake da shi na abinci a cikin kasar.

Bisa wasu alkaluma da cibiyar kididdiga ta kasa, wato NBS ta fitar, sun suna cewa; jimillar kayan abinci na naira tiriliyan 3.34, aka shigo da su cikin kasar nan daga watan Janairu zuwa na Satumbar 2025, wanda ya karu da kashi 23 cikin 100.

Manoman kasar, na ci gaba da kokawa kan yadda ake shigo da kayan abinci da rage samar da ayyukan yi ga fannin,” a cewarsa.

Magance Kalubalen Tabarbarewar  Rashin Tsaro:

An shafe shekaru uku, fannin aikin noma na kasar nan na fuskantar matsalar sauyin yanayi.

Kazalika, akwai batun karancin ruwan sama da ambaliyar ruwan sama da ke shafar fannin, wanda hakan ke haifar da asarar biliyoyin nairori na jarin da manoman suka zuba a sana’ar tasu, musamman a Arewacin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, wasu alkaluma da hukumar kasa da kasa da ke sanya ido kan afkuwar annoba, sun nuna cewa; a shekarar 2022 jimillar mutane miliyan 21.9 sauyin yanayi ya shafa a kasar, wanda hakan ya haifar da mutuwar mutane 603 da kuma asarar da ta kai ta dala biliyan 4.2 daidai da naira biliyan 1.6.

Shi kuwa, shugaban kungiyar masu sarrafa takin zamani na gargajiya na kasa, Jude Obi ya sanar da cewa; tsananin zafin yanayi na shafar amfanin gona.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Karfafa Wa Manoma Gwiwa Don Yin Noma Har Zuwa Karshen Shekara:

Za a iya cimma hakan, idan har an samar wa da manoman kayan aikin noma na rani, musamman duba da yadda a duk shekara ake samun raguwar aikin noma a duk shekara, wanda hakan kuma ke shafar kudin shiga da manoman ke samu.

Hasashen da hukumar kula da ssmar da abinci ta duniya (FAO) a shekarar 2050 ta yi, ta ce yawan ruwan da duniya ke bukata, zai karu da kashi 50.

Bugu da kari, domin samun damar iya ciyar da yawan al’ummar kasar nan da abinci, akwai bukatar gwamnatin tarayya, ta samar da kyakkyawan yanayi ga manoman kasar, musamman ta hanyar samar musu da kayan aikin noma na rani, domin su kara habaka sana’ar tasu.

“Domin dawo da kima da kuma martabar aikin noma a kasar nan, ya zama wajibi gwamnatin tarayya, ta samar wa da manoman kayan aikin noma na zamani” in ji shugaban kungiyar manoma ta kasa, Ibrahim Kabir.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Har Yanzu Ba Mu Fitar da Rai Kan Samun Tikitin Kofin Duniya Ba — NFF

Har Yanzu Ba Mu Fitar da Rai Kan Samun Tikitin Kofin Duniya Ba — NFF

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.