ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tarayya Za Ta Habaka Fannin Aikin Noma A 2026 —Kwararru

by Abubakar Abba
4 months ago
Gwamnatin

Yanayin noma a shekarar 2026, ya ta’allaka da irin mayar da hankalin da gwamnatin tarayya za ta yi, wajen kawo karshen manyan matsalolin da manoman kasar nan ke ci gaba da fuskanta, musamman duba da cewa; fannin na bayar da gagarumar gudunmawa, wajen samar da wadataccen abinci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin wannan kasa.

Hakan ne ya sanya, Jaridar BusinessDay, ta tattauna da wasu kwararru a fannin, inda suke yi karin haske a kan abubuwan da  suka kamata gwamnatin ta mayar da hankali a kansu, domin habaka fannin na noma.

  • Jakadan Sin: Cudanyar Al’adu Za Ta Taimaki Yunkurin Daidaita Hulda Tsakanin Sin Da Amurka
  • Gobara Ta Hallaka Mutum 2, Ta Lalata Dukiya Ta Biliyan 1.59 A Bauchi

Masanan sun bayyana cewa, fannin na noman kasar, zai kara bunkasa ne kadai idan gwamnatin ta mayar da hankali wajen magance kalubalen rashin tsaro da samar wa da manoman tallafi da tabbatar da ganin ana yin noman har zuwa karshen shekara da kuma gayyato musu ruwa da tsaki a cikin fannin da samar masu da kayan aikin noma da sauransu.

Sama Musu Kayan Aiki A Farashi Mai Sauki:

Tsadar farashin kayan aikin noma, na daya daga cikin kalubalen da manoman kasar ke ci gaba da fuskanta, wanda kuma hakan ke ci gaba zama barazana ga sana’ar ta manoman da kuma shafar jarinsu..

Kazalika, wadannan matsaloli a shekarar 2025, sun haifar da karancin abinci a kasar tare da kuma haifar da hauhawar farashin kayan abinci da kuma dakile ribar da ya kamata manoman su samu.

Nijeriya dai, ta dogara ne a kan shigo da kayan abinci daga waje, musamman domin cike gibin da ake da shi na abinci a cikin kasar.

Bisa wasu alkaluma da cibiyar kididdiga ta kasa, wato NBS ta fitar, sun suna cewa; jimillar kayan abinci na naira tiriliyan 3.34, aka shigo da su cikin kasar nan daga watan Janairu zuwa na Satumbar 2025, wanda ya karu da kashi 23 cikin 100.

Manoman kasar, na ci gaba da kokawa kan yadda ake shigo da kayan abinci da rage samar da ayyukan yi ga fannin,” a cewarsa.

Magance Kalubalen Tabarbarewar  Rashin Tsaro:

An shafe shekaru uku, fannin aikin noma na kasar nan na fuskantar matsalar sauyin yanayi.

Kazalika, akwai batun karancin ruwan sama da ambaliyar ruwan sama da ke shafar fannin, wanda hakan ke haifar da asarar biliyoyin nairori na jarin da manoman suka zuba a sana’ar tasu, musamman a Arewacin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, wasu alkaluma da hukumar kasa da kasa da ke sanya ido kan afkuwar annoba, sun nuna cewa; a shekarar 2022 jimillar mutane miliyan 21.9 sauyin yanayi ya shafa a kasar, wanda hakan ya haifar da mutuwar mutane 603 da kuma asarar da ta kai ta dala biliyan 4.2 daidai da naira biliyan 1.6.

Shi kuwa, shugaban kungiyar masu sarrafa takin zamani na gargajiya na kasa, Jude Obi ya sanar da cewa; tsananin zafin yanayi na shafar amfanin gona.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Karfafa Wa Manoma Gwiwa Don Yin Noma Har Zuwa Karshen Shekara:

Za a iya cimma hakan, idan har an samar wa da manoman kayan aikin noma na rani, musamman duba da yadda a duk shekara ake samun raguwar aikin noma a duk shekara, wanda hakan kuma ke shafar kudin shiga da manoman ke samu.

Hasashen da hukumar kula da ssmar da abinci ta duniya (FAO) a shekarar 2050 ta yi, ta ce yawan ruwan da duniya ke bukata, zai karu da kashi 50.

Bugu da kari, domin samun damar iya ciyar da yawan al’ummar kasar nan da abinci, akwai bukatar gwamnatin tarayya, ta samar da kyakkyawan yanayi ga manoman kasar, musamman ta hanyar samar musu da kayan aikin noma na rani, domin su kara habaka sana’ar tasu.

“Domin dawo da kima da kuma martabar aikin noma a kasar nan, ya zama wajibi gwamnatin tarayya, ta samar wa da manoman kayan aikin noma na zamani” in ji shugaban kungiyar manoma ta kasa, Ibrahim Kabir.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Har Yanzu Ba Mu Fitar da Rai Kan Samun Tikitin Kofin Duniya Ba — NFF

Har Yanzu Ba Mu Fitar da Rai Kan Samun Tikitin Kofin Duniya Ba — NFF

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.