ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Gwamnatin Tarayya Za Ta Habaka Fannin Aikin Noma A 2026 —Kwararru

by Abubakar Abba
7 months ago
Gwamnatin

Yanayin noma a shekarar 2026, ya ta’allaka da irin mayar da hankalin da gwamnatin tarayya za ta yi, wajen kawo karshen manyan matsalolin da manoman kasar nan ke ci gaba da fuskanta, musamman duba da cewa; fannin na bayar da gagarumar gudunmawa, wajen samar da wadataccen abinci da kuma kara bunkasa fannin tattalin arzikin wannan kasa.

Hakan ne ya sanya, Jaridar BusinessDay, ta tattauna da wasu kwararru a fannin, inda suke yi karin haske a kan abubuwan da  suka kamata gwamnatin ta mayar da hankali a kansu, domin habaka fannin na noma.

  • Jakadan Sin: Cudanyar Al’adu Za Ta Taimaki Yunkurin Daidaita Hulda Tsakanin Sin Da Amurka
  • Gobara Ta Hallaka Mutum 2, Ta Lalata Dukiya Ta Biliyan 1.59 A Bauchi

Masanan sun bayyana cewa, fannin na noman kasar, zai kara bunkasa ne kadai idan gwamnatin ta mayar da hankali wajen magance kalubalen rashin tsaro da samar wa da manoman tallafi da tabbatar da ganin ana yin noman har zuwa karshen shekara da kuma gayyato musu ruwa da tsaki a cikin fannin da samar masu da kayan aikin noma da sauransu.

Sama Musu Kayan Aiki A Farashi Mai Sauki:

Tsadar farashin kayan aikin noma, na daya daga cikin kalubalen da manoman kasar ke ci gaba da fuskanta, wanda kuma hakan ke ci gaba zama barazana ga sana’ar ta manoman da kuma shafar jarinsu..

Kazalika, wadannan matsaloli a shekarar 2025, sun haifar da karancin abinci a kasar tare da kuma haifar da hauhawar farashin kayan abinci da kuma dakile ribar da ya kamata manoman su samu.

Nijeriya dai, ta dogara ne a kan shigo da kayan abinci daga waje, musamman domin cike gibin da ake da shi na abinci a cikin kasar.

Bisa wasu alkaluma da cibiyar kididdiga ta kasa, wato NBS ta fitar, sun suna cewa; jimillar kayan abinci na naira tiriliyan 3.34, aka shigo da su cikin kasar nan daga watan Janairu zuwa na Satumbar 2025, wanda ya karu da kashi 23 cikin 100.

Manoman kasar, na ci gaba da kokawa kan yadda ake shigo da kayan abinci da rage samar da ayyukan yi ga fannin,” a cewarsa.

Magance Kalubalen Tabarbarewar  Rashin Tsaro:

An shafe shekaru uku, fannin aikin noma na kasar nan na fuskantar matsalar sauyin yanayi.

Kazalika, akwai batun karancin ruwan sama da ambaliyar ruwan sama da ke shafar fannin, wanda hakan ke haifar da asarar biliyoyin nairori na jarin da manoman suka zuba a sana’ar tasu, musamman a Arewacin kasar nan.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, wasu alkaluma da hukumar kasa da kasa da ke sanya ido kan afkuwar annoba, sun nuna cewa; a shekarar 2022 jimillar mutane miliyan 21.9 sauyin yanayi ya shafa a kasar, wanda hakan ya haifar da mutuwar mutane 603 da kuma asarar da ta kai ta dala biliyan 4.2 daidai da naira biliyan 1.6.

Shi kuwa, shugaban kungiyar masu sarrafa takin zamani na gargajiya na kasa, Jude Obi ya sanar da cewa; tsananin zafin yanayi na shafar amfanin gona.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Karfafa Wa Manoma Gwiwa Don Yin Noma Har Zuwa Karshen Shekara:

Za a iya cimma hakan, idan har an samar wa da manoman kayan aikin noma na rani, musamman duba da yadda a duk shekara ake samun raguwar aikin noma a duk shekara, wanda hakan kuma ke shafar kudin shiga da manoman ke samu.

Hasashen da hukumar kula da ssmar da abinci ta duniya (FAO) a shekarar 2050 ta yi, ta ce yawan ruwan da duniya ke bukata, zai karu da kashi 50.

Bugu da kari, domin samun damar iya ciyar da yawan al’ummar kasar nan da abinci, akwai bukatar gwamnatin tarayya, ta samar da kyakkyawan yanayi ga manoman kasar, musamman ta hanyar samar musu da kayan aikin noma na rani, domin su kara habaka sana’ar tasu.

“Domin dawo da kima da kuma martabar aikin noma a kasar nan, ya zama wajibi gwamnatin tarayya, ta samar wa da manoman kayan aikin noma na zamani” in ji shugaban kungiyar manoma ta kasa, Ibrahim Kabir.

Gwamnatin
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Har Yanzu Ba Mu Fitar da Rai Kan Samun Tikitin Kofin Duniya Ba — NFF

Har Yanzu Ba Mu Fitar da Rai Kan Samun Tikitin Kofin Duniya Ba — NFF

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.